< Job 20 >

1 Then answered Zophar the Naamathite and saide,
Sai Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
2 Doubtlesse my thoughts cause me to answere, and therefore I make haste.
“Tunanin da ya dame ni ya sa dole in amsa domin abin ya dame ni sosai.
3 I haue heard the correction of my reproch: therefore the spirite of mine vnderstanding causeth me to answere.
Na ji wani zargin da ka yi mini na reni, kuma yadda na gane, shi ya sa zan ba da amsa.
4 Knowest thou not this of olde? and since God placed man vpon the earth,
“Ba shakka ka san yadda abin yake tuntuni, tun da aka sa mutum cikin duniya,
5 That the reioycing of the wicked is short, and that the ioy of hypocrites is but a moment?
mugun mutum bai taɓa daɗewa ba, farin cikin mutum na ɗan gajeren lokaci ne.
6 Though his excellencie mount vp to the heauen, and his head reache vnto the cloudes,
Ko da ya ƙasaita ya kai sararin sama, kansa kuma yana taɓa gizagizai.
7 Yet shall hee perish for euer, like his dung, and they which haue seene him, shall say, Where is hee?
Zai hallaka har abada, kamar bayan gidansa; waɗanda suka gan shi za su ce, ‘Ina yake?’
8 He shall flee away as a dreame, and they shall not finde him, and shall passe away as a vision of the night,
Kamar mafarki haka zai ɓace, ba za a ƙara ganinsa ba zai ɓace kamar wahayi da dare.
9 So that the eye which had seene him, shall do so no more, and his place shall see him no more.
Idon da ya gan shi ba zai ƙara ganinsa ba; wurin zamansa ba zai sāke ganinsa ba.
10 His children shall flatter the poore, and his hands shall restore his substance.
Dole’ya’yansa su mayar wa matalauta abin da ya kamata; dole hannuwansa su mayar da dukiyarsa.
11 His bones are full of the sinne of his youth, and it shall lie downe with him in the dust.
Jin ƙarfi da ya cika ƙasusuwansa zai kwantar da shi a cikin ƙura.
12 When wickednesse was sweete in his mouth, and he hid it vnder his tongue,
“Ko da yake mugunta tana da daɗi a bakinsa kuma yana ɓoye ta a harshensa,
13 And fauoured it, and would not forsake it, but kept it close in his mouth,
ko da yake ba zai iya rabuwa da ita ba, yana kuma ajiye ta a bakinsa,
14 Then his meat in his bowels was turned: the gall of Aspes was in the middes of him.
duk da haka abincin da ya ci zai zama da tsami a cikin cikinsa; zai zama kamar dafin maciji a cikinsa.
15 He hath deuoured substance, and hee shall vomit it: for God shall drawe it out of his bellie.
Zai haras da dukiyar da ya haɗiye; Allah zai sa cikinsa yă haras da su.
16 He shall sucke the gall of Aspes, and the vipers tongue shall slay him.
Zai sha dafin maciji; sarar maciji mai dafi za tă tashe shi.
17 He shall not see the riuers, nor the floods and streames of honie and butter.
Ba zai ji daɗin koguna da rafuffuka masu kwarara da zuma da madara ba.
18 He shall restore the labour, and shall deuoure no more: euen according to the substance shalbe his exchange, and he shall enioy it no more.
Dole yă ba da abin da ya yi gumi kafin yă samu, ba zai ci ba; ba zai ji daɗin ribar da ya samu daga kasuwancinsa ba.
19 For he hath vndone many: he hath forsaken the poore, and hath spoyled houses which he builded not.
Gama ya ci zalin talakawa ya bar su cikin wahala; ya ƙwace gidajen da ba shi ya gina ba.
20 Surely he shall feele no quietnes in his bodie, neither shall he reserue of that which he desired.
“Ba shakka ba zai samu abin da yake ƙoƙarin samu ba, dukiyarsa ba za tă cece shi ba.
21 There shall none of his meate bee left: therefore none shall hope for his goods.
Ba abin da ya ragu da zai ɗauka; arzikinsa ba zai dawwama ba.
22 When he shalbe filled with his abundance, he shalbe in paine, and the hand of all the wicked shall assaile him.
Yana cikin samun arziki, ɓacin rai zai auka masa; ƙunci mai ƙarfi zai zo masa.
23 He shall be about to fill his belly, but God shall sende vpon him his fierce wrath, and shall cause to rayne vpon him, euen vpon his meate.
Lokacin da ya cika cikinsa, Allah zai zuba fushinsa a kansa, zai daddaka shi.
24 He shall flee from the yron weapons, and the bow of steele shall strike him through.
Ko da yake yana guje wa makamin ƙarfe, kibiya mai bakin tagulla za tă huda shi.
25 The arrowe is drawen out, and commeth forth of the body, and shineth of his gall, so feare commeth vpon him.
Zai zāre ta daga bayansa, tsinin zai fita daga hantarsa; tsoro zai cika shi;
26 All darkenes shalbe hid in his secret places: the fire that is not blowen, shall deuoure him, and that which remaineth in his tabernacle, shalbe destroyed.
duhu kawai yake jiran dukiyarsa. Wutar da ba a fifita ba za tă cinye shi ta kuma ƙona duk abin da ya rage a tentinsa.
27 The heauen shall declare his wickednes, and the earth shall rise vp against him.
Sammai za su fallasa laifinsa; duniya za tă yi gāba da shi.
28 The increase of his house shall go away: it shall flow away in the day of his wrath.
Ambaliyar ruwa za tă tafi da gidansa, ruwaye masu gudu a ranar fushin Allah.
29 This is the portion of the wicked man from God, and the heritage that he shall haue of God for his wordes.
Abin da Allah zai sa yă faru da mugu ke nan, gādon da Allah ya ba shi ke nan.”

< Job 20 >