< Job 19 >

1 Bvt Iob answered, and said,
Sai Ayuba ya amsa,
2 Howe long will yee vexe my soule, and torment me with wordes?
“Har yaushe za ku yi ta ba ni azaba ku kuma murƙushe ni da maganganunku?
3 Ye haue now ten times reproched me, and are not ashamed: ye are impudent toward mee.
Yanzu sau goma ke nan kuna wulaƙanta ni, kuna kai mini hari na rashin kunya.
4 And though I had in deede erred, mine errour remaineth with me.
In gaskiya ne na yi laifi, kuskurena ya rage nawa.
5 But in deede if ye will aduance your selues against me, and rebuke me for my reproche,
In kuwa za ku ɗaukaka kanku a kaina kuna ɗauka wahalar da nake sha domin na yi laifi ne,
6 Know nowe, that God hath ouerthrowen me, and hath compassed me with his net.
sai ku san cewa Allah ya yi mini ba daidai ba ya kewaye ni da ragarsa.
7 Beholde, I crie out of violence, but I haue none answere: I crie, but there is no iudgement.
“Ko da yake na yi kuka cewa, ‘An yi mini ba daidai ba!’ Ba a amsa mini ba; ko da yake na nemi taimako, ba a yi adalci ba.
8 Hee hath hedged vp my way that I cannot passe, and he hath set darkenesse in my paths.
Ya tare mini hanya yadda ba zan iya wucewa ba; ya rufe hanyata da duhu.
9 Hee hath spoyled mee of mine honour, and taken the crowne away from mine head.
Ya cire darajar da nake da ita, ya kuma cire rawani daga kaina.
10 He hath destroyed mee on euery side and I am gone: and he hath remoued mine hope like a tree.
Ya yi kaca-kaca da ni har sai da na ƙare; ya tuge begen da nake da shi kamar itace.
11 And he hath kindled his wrath against me, and counteth mee as one of his enemies.
Yana jin haushina ya lissafta ni cikin maƙiyansa.
12 His armies came together, and made their way vpon me, and camped about my tabernacle.
Rundunarsa ta zo da ƙarfi; suka kafa sansani kewaye da ni, suka zagaye tentina.
13 He hath remooued my brethre farre from me, and also mine acquaintance were strangers vnto me.
“Ya raba ni da’yan’uwana maza; abokaina sun zama baƙi gare ni.
14 My neighbours haue forsaken me, and my familiars haue forgotten me.
Dangina sun tafi; abokaina na kurkusa sun manta da ni.
15 They that dwel in mine house, and my maydes tooke me for a stranger: for I was a stranger in their sight.
Waɗanda sukan ziyarce ni, da masu yi mini aiki mata sun ɗauke ni baƙo.
16 I called my seruant, but he would not answere, though I prayed him with my mouth.
Na kira bawana, amma bai amsa ba, ko da yake na roƙe shi da bakina.
17 My breath was strange vnto my wife, though I prayed her for the childrens sake of mine owne body.
Numfashina yana ɓata wa matata rai;’yan’uwana sun ƙi ni.
18 The wicked also despised mee, and when I rose, they spake against me.
Har’yan yara suna rena ni; in sun gan ni sai su fara yi mini riyar reni.
19 All my secret friends abhorred me, and they whome I loued, are turned against me.
Duk abokaina sun yashe ni; waɗanda nake ƙauna sun zama ba sa ƙaunata.
20 My bone cleaueth to my skinne and to my flesh, and I haue escaped with the skinne of my teeth.
Ni ba kome ba ne sai dai fata da ƙashi, da ƙyar na tsira.
21 Haue pitie vpon me: haue pitie vpon me, (O yee my friendes) for the hande of God hath touched me.
“Ku tausaya mini, abokaina, ku ji tausayina, gama hannun Allah ya sauko a kaina.
22 Why do ye persecute me, as God? and are not satisfied with my flesh?
Don me kuke fafarata kamar yadda Allah yake yi? Ba ku gaji da yagar fatata ba?
23 Oh that my wordes were nowe written! oh that they were written euen in a booke,
“Kash, da ma a ce ana rubuta maganganuna, da an rubuta su a littafi,
24 And grauen with an yron pen in lead, or in stone for euer!
a rubuta su da ƙarfe a kan dutse don su dawwama har abada!
25 For I am sure, that my Redeemer liueth, and he shall stand the last on the earth.
Na san wanda zai fanshe ni yana nan da rai, kuma a ƙarshe zai tsaya a kan duniya.
26 And though after my skin wormes destroy this bodie, yet shall I see God in my flesh.
Kuma bayan an hallaka fatata, duk da haka a cikin jiki zan ga Allah.
27 Whome I my selfe shall see, and mine eyes shall beholde, and none other for me, though my reynes are consumed within me.
Zan gan shi da kaina da idanuna, Ni, ba wani ba ne. Zuciyata ta cika da wannan tunani!
28 But yee sayde, Why is hee persecuted? And there was a deepe matter in me.
“In kuka ce, ‘Za ku ci gaba da matsa mini, tun da shi ne tushen damuwa,’
29 Be ye afraide of the sworde: for the sworde will be auenged of wickednesse, that yee may knowe that there is a iudgement.
sai ku ma ku ji tsoron takobin; gama fushi yakan kawo hukunci ta wurin takobi, sa’an nan za ku san cewa akwai shari’a.”

< Job 19 >