< Jeremiah 12 >

1 O Lord, if I dispute with thee, thou art righteous: yet let mee talke with thee of thy iudgements: wherefore doeth the way of the wicked prosper? why are all they in wealth that rebelliously transgresse?
Kullum kai mai adalci ne, ya Ubangiji, sa’ad da na kawo ƙara a gabanka. Duk da haka zan yi magana da kai game da shari’arka. Me ya sa mugaye suke nasara? Me ya sa dukan maciya amana suke zama ba damuwa?
2 Thou hast planted them, and they haue taken roote: they grow, and bring forth fruite: thou art neere in their mouth, and farre from their reines.
Ka dasa su, sun kuwa yi saiwa; sun yi girma suna ba da’ya’ya. Kullum sunanka yana a bakinsu amma kana nesa da zuciyarsu.
3 But thou, Lord, knowest me: thou hast seene me, and tried mine heart towarde thee: pull them out like sheepe for the slaughter, and prepare them for the day of slaughter.
Duk da haka ka san ni, ya Ubangiji; kana ganina ka kuma gwada tunanina game da kai. Ka ja su kamar tumakin da za a yanka! Ka ware su don ranar yanka!
4 Howe long shall the lande mourne, and the herbes of euery fielde wither, for the wickednesse of them that dwell therein? the beastes are consumed and the birdes, because they sayd, He wil not see our last ende.
Har yaushe ƙasar za tă kasance busasshiya ciyawar kowane fili ta bushe? Domin waɗanda suke zaune cikinta mugaye ne, dabbobi da tsuntsaye sun hallaka. Ban da haka ma, mutane suna cewa, “Ba zai ga abin da yake faruwa da mu ba.”
5 If thou hast runne with the footemen and they haue wearied thee, then howe canst thou match thy selfe with horses? and if thou thoughtest thy selfe safe in a peaceable lande, what wilt thou do in the swelling of Iorden?
“In ka yi tsere da mutane a ƙafa suka kuma gajiyar da kai, yaya za ka yi gasa da dawakai? In ka yi tuntuɓe a lafiyayyiyar ƙasa, ƙaƙa za ka yi a kurmin Urdun?
6 For euen thy brethren, and the house of thy father, euen they haue delt vnfaithfully with thee, and they haue cryed out altogether vpon thee: but beleeue them not, though they speake faire to thee.
’Yan’uwanka, iyalinka har su ma sun bashe ka; sun tā da kuka mai ƙarfi a kanka. Kada ka amince da su, ko da yake suna faɗa maganganu masu kyau game da kai.
7 I haue forsaken mine house: I haue left mine heritage: I haue giuen the dearely beloued of my soule into the hands of her enemies.
“Zan yashe gidana, in rabu da gādona; Zan ba da wadda nake ƙauna a hannuwan abokan gābanta.
8 Mine heritage is vnto mee, as a lion in the forest: it crieth out against mee, therefore haue I hated it.
Gādona ya zama mini kamar zaki a kurmi. Yana mini ruri; saboda haka na ƙi shi.
9 Shall mine heritage bee vnto mee, as a bird of diuers colours? are not the birdes about her, saying, Come, assemble all ye beastes of the fielde, come to eate her?
Ashe, gādona bai zama mini kamar dabbare dabbaren tsuntsu mai cin nama da sauran tsuntsaye masu cin nama suka kewaye shi da faɗa ba? Tafi ka tattaro dukan namun jeji; ka kawo su su ci.
10 Many pastors haue destroyed my vineyarde, and troden my portion vnder foote: of my pleasant portion they haue made a desolate wildernesse.
Makiyaya masu yawa za su lalace gonar inabina su tattake gonata; za su mai da gonata mai kyau kango marar amfani.
11 They haue layde it waste, and it, being waste, mourneth vnto me: and the whole lande lyeth waste, because no man setteth his minde on it.
Za tă zama kango, busasshiya da kuma kango a gabana; ƙasar duka za tă zama kango domin ba wanda ya kula.
12 The destroyers are come vpon all the high places in the wildernesse: for the sworde of the Lord shall deuoure from the one end of the land, euen to the other ende of the lande: no flesh shall haue peace.
A kan dukan tsaunukan nan na hamada masu hallakarwa za su zo, gama takobin Ubangiji zai ci daga wannan iyaka ƙasa zuwa wancan; ba wanda zai zauna lafiya.
13 They haue sowen wheate, and reaped thornes: they were sicke, and had no profite: and they were ashamed of your fruites, because of the fierce wrath of the Lord.
Za su shuka alkama, su girbe ƙayayyuwa; za su gajiyar da kansu, ba za su kuwa sami kome ba. Saboda haka ku sha kunyar abin da kuka girbe saboda zafin fushin Ubangiji.”
14 Thus sayeth the Lord against all mine euill neighbours, that touch the inheritance, which I haue caused my people Israel to inherite, Beholde, I will plucke them out of their lande, and plucke out the house of Iudah from among them.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Game da dukan mugayen maƙwabtana waɗanda suka ƙwace gādon da na ba wa mutanena Isra’ila kuwa, zan tumɓuke su daga ƙasashensu zan kuma tumɓuke gidan Yahuda daga cikinsu.
15 And after that I haue plucked them out, I will returne, and haue compassion on them, and will bring againe euery man to his heritage, and euery man to his land.
Amma bayan na tumɓuke su, zan sāke jin tausayi in komo da kowannensu zuwa gādonsa da kuma ƙasarsa.
16 And if they will learne the wayes of my people, to sweare by my Name, (The Lord liueth, as they taught my people to sweare by Baal) then shall they be built in the middes of my people.
In kuma suka koyi al’amuran mutanena sosai suka kuma yi rantsuwa da sunana, suna cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye’ kamar yadda sun taɓa koya wa jama’ata yin rantsuwa da Ba’al, sa’an nan za su kahu a cikin jama’ata.
17 But if they will not obey, then will I vtterly plucke vp, and destroy that nation, sayeth the Lord.
Amma duk al’ummar da ba tă saurara ba, zan tumɓuke ta ɗungum in kuma hallaka ta,” in ji Ubangiji.

< Jeremiah 12 >