< Job 21 >

1 Bvt Iob answered, and sayd,
Sai Ayuba ya amsa,
2 Heare diligently my wordes, and this shalbe in stead of your consolations.
“Ku saurare ni da kyau; bari wannan yă zama ta’aziyyar da za ku ba ni.
3 Suffer mee, that I may speake, and when I haue spoken, mocke on.
Ku ba ni zarafi in yi magana, bayan na gama sai ku yi ba’arku.
4 Doe I direct my talke to man? If it were so, how should not my spirit be troubled?
“A wurin mutum ne na kawo kukana? Don me ba zan kāsa haƙuri ba?
5 Marke mee, and be abashed, and lay your hand vpon your mouth.
Ku dube ni, ku kuma yi mamaki; ku rufe bakina da hannunku.
6 Euen when I remember, I am afrayde, and feare taketh hold on my flesh.
Lokacin da na yi tunanin wannan, sai in ji tsoro; jikina yă fara rawa.
7 Wherefore do the wicked liue, and waxe olde, and grow in wealth?
Don me mugaye suke rayuwa har su tsufa, suna kuma ƙaruwa da iko?
8 Their seede is established in their sight with them, and their generation before their eyes.
Suna ganin’ya’yansu suna girma, suna ganin jikokinsu suna tasowa a kan idanunsu.
9 Their houses are peaceable without feare, and the rod of God is not vpon them.
Gidajensu suna zama cikin lafiya ba ruwansu da fargaba. Kuma Allah ba ya ba su horo.
10 Their bullocke gendreth, and fayleth not: their cow calueth, and casteth not her calfe.
Shanunsu ba sa fasa haihuwa; suna haihuwa ba sa yin ɓari.
11 They send forth their children like sheepe, and their sonnes dance.
Suna aika’ya’yansu kamar garke;’ya’yansu suna guje-guje da tsalle-tsalle.
12 They take the tabret and harpe, and reioyce in the sound of the organs.
Suna rera da kayan kiɗa na ganga da garaya; suna jin daɗin busar sarewa.
13 They spend their dayes in wealth, and suddenly they go downe to the graue. (Sheol h7585)
Suna yin rayuwarsu cikin arziki kuma su mutu cikin salama. (Sheol h7585)
14 They say also vnto God, Depart from vs: for we desire not the knowledge of thy wayes.
Duk da haka suna ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu.’ Ba ma so mu san hanyoyinka.
15 Who is the Almightie, that we should serue him? and what profit should we haue, if we should pray vnto him?
Wane ne Maɗaukaki har da za mu bauta masa? Wace riba za mu samu ta wurin yin addu’a gare shi?
16 Lo, their wealth is not in their hand: therfore let the counsell of the wicked bee farre from me.
Amma arzikinsu ba a hannunsu yake ba saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
17 How oft shall the candle of the wicked be put out? and their destruction come vpon them? he wil deuide their liues in his wrath.
“Duk da haka, sau nawa fitilar mugu take mutuwa? Sau nawa bala’i yake auka masa, ko Allah ya taɓa hukunta mugu cikin fushi?
18 They shall be as stubble before the winde, and as chaffe that the storme carieth away.
Sau nawa suke zama kamar tattaka a iska, ko kuma kamar ƙura da iskar hadari take kwashewa?
19 God wil lay vp the sorowe of the father for his children: when he rewardeth him, hee shall knowe it.
An ce ‘Allah yana tara wa’ya’yan mutum horon da zai ba mutumin.’ Bari yă ba mutumin horo don yă san ya yi haka!
20 His eyes shall see his destruction, and he shall drinke of the wrath of the Almightie.
Bari idanunsa su ga yadda zai hallaka; bari yă sha daga fushin Maɗaukaki.
21 For what pleasure hath he in his house after him, when the nomber of his moneths is cut off?
Ko zai damu da iyalin da ya bari a baya sa’ad da kwanakinsa suka ƙare?
22 Shall any teache God knowledge, who iudgeth the highest things?
“Wani zai iya koya wa Allah ilimi tun da yana shari’anta har da waɗanda suke manya masu iko?
23 One dyeth in his full strength, being in all ease and prosperitie.
Wani mutum zai mutu cikin jin daɗi da kwanciyar hankali,
24 His breasts are full of milke, and his bones runne full of marowe.
jikinsa ɓulɓul, ƙasusuwansa da alamar ƙarfi.
25 And another dieth in the bitternes of his soule, and neuer eateth with pleasure.
Wani kuma zai mutu cikin ɗacin rai, bai taɓa jin daɗin wani abu mai kyau ba.
26 They shall sleepe both in the dust, and the wormes shall couer them.
Dukansu kuwa za a bizne su a ƙasa, kuma tsutsotsi za su cinye su.
27 Behold, I know your thoughts, and the enterprises, wherewith ye do me wrong.
“Na san duk abin da kuke tunani, yadda za ku saɓa mini.
28 For ye say, Where is the princes house? and where is the tabernacle of the wickeds dwelling?
Kuna cewa, ‘Yanzu ina gidan babban mutumin nan, tenti wurin da mugaye suke zama?’
29 May ye not aske the that go by the way? and ye can not deny their signes.
Ba ku taɓa tambayar waɗanda suke tafiya ba? Ba ku kula da labaransu,
30 But the wicked is kept vnto the day of destruction, and they shall be brought forth to the day of wrath.
cewa an kāre mugu daga ranar bala’i, an kāre shi daga ranar fushi?
31 Who shall declare his way to his face? and who shall reward him for that he hath done?
Wane ne yake gaya masa abin da ya yi? Wane ne yake rama abin da ya yi?
32 Yet shall he be brought to the graue, and remaine in the heape.
Za a bizne shi a kabari, a kuma yi tsaron kabarinsa.
33 The slimie valley shalbe sweete vnto him, and euery man shall draw after him, as before him there were innumerable.
Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali; dukan jama’a suna binsa, da yawa kuma suna gabansa.
34 How then comfort ye me in vaine, seeing in your answeres there remaine but lyes?
“Saboda haka ta yaya za ku iya yi mini ta’aziyya da surutan banzan nan naku? Babu wani abu cikin amsarku sai ƙarya!”

< Job 21 >