< Deuteronomy 26 >

1 Also when thou shalt come into the lande which the Lord thy God giueth thee for inheritance, and shalt possesse it, and dwell therein,
Sa’ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo, kuka mallake ta, kuka kuma zauna a cikinta,
2 Then shalt thou take of the first of all the fruite of the earth, and bring it out of the lande that the Lord thy God giueth thee, and put it in a basket, and goe vnto the place, which the Lord thy God shall chose to place his Name there.
sai ku ɗauki’ya’yan fari na dukan amfanin gonar ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, ku zuba a kwando. Sa’an nan ku je wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa yă zama mazauni don Sunansa,
3 And thou shalt come vnto the Priest, that shall be in those dayes, and say vnto him, I acknowledge this day vnto the Lord thy God, that I am come vnto the countrey which the Lord sware vnto our fathers for to giue vs.
ku faɗa wa firist da yake aiki a lokacin, “Na sakankance yau ga Ubangiji Allahnka, cewa na zo ƙasar da Ubangiji ya rantse zai ba wa kakanninmu.”
4 Then the Priest shall take the basket out of thine hand, and set it downe before the altar of the Lord thy God.
Firist ɗin zai karɓi kwandon daga hannuwanku yă sa shi a ƙasa a gaban bagaden Ubangiji Allahnku.
5 And thou shalt answere and say before the Lord thy God, A Syrian was my father, who being ready to perish for hunger, went downe into Egypt, and soiourned there with a small company, and grew there vnto a nation great, mightie and full of people.
Sa’an nan za ku furta a gaban Ubangiji Allahnku cewa, “Mahaifina mutumin Aram ne mai yawo, ya gangara zuwa Masar da mutane kaɗan, ya zauna a can, ya kuma zama babban al’umma, mai iko da kuma mai yawa.
6 And the Egyptians vexed vs, and troubled vs, and laded vs with cruell bondage.
Amma Masarawa suka wulaƙanta mu suka sa muka sha wahala, suna sa mu aikin dole.
7 But when we cried vnto the Lord God of our fathers, the Lord heard our voyce, and looked on our aduersitie, and on our labour, and on our oppression.
Sai muka yi kuka ga Ubangiji Allahn kakanninmu, Ubangiji kuwa ya ji kukanmu, ya kuma azabar da muke sha, da wahalar da muke sha, da danniyar da suke yin mana.
8 And the Lord brought vs out of Egypt in a mightie hande, and a stretched out arme, with great terriblenesse, both in signes and wonders.
Sai Ubangiji ya fitar da mu daga Masar da hannu mai ƙarfi da kuma iko, da razana mai girma da kuma alamu banmamaki da al’ajabai.
9 And he hath brought vs into this place, and hath giuen vs this land, euen a lande that floweth with milke and hony.
Ya kawo mu wannan wuri, ya kuma ba mu wannan ƙasa, ƙasa mai zub da madara da kuma zuma;
10 And now, lo, I haue brought ye first fruites of the land which thou, O Lord, hast giuen me, and thou shalt set it before the Lord thy God, and worship before the Lord thy God:
yanzu kuwa na kawo’ya’yan fari na gonar da kai, ya Ubangiji ka ba ni.” Sai ku sa kwandon a gaban Ubangiji Allahnku, sa’an nan ku rusuna a gabansa.
11 And thou shalt reioyce in all the good things which the Lord thy God hath giuen vnto thee and to thine houshold, thou and the Leuite, and the stranger that is among you.
Ku da Lawiyawa da baƙin da suke a cikinku, za ku yi murna cikin dukan abubuwa masu kyau da Ubangiji Allahnku ya ba ku tare da gidanku.
12 When thou hast made an end of tithing all the tythes of thine increase, the thirde yeere, which is the yeere of tithing, and hast giuen it vnto the Leuite, to the stranger, to the fatherlesse, and to the widowe, that they may eate within thy gates, and be satisfied,
Sa’ad da kuka gama fitar da kashi ɗaya bisa goma na dukan amfanin gona a shekara ta uku, shekarar zakka, za ku ba da su ga Balawe, baƙo, maraya da kuma gwauruwa, don su ci a cikin garuruwanku su ƙoshi.
13 Then thou shalt say before the Lord thy God, I haue brought the halowed thing out of mine house, and also haue giuen it vnto the Leuites and to the strangers, to the fatherlesse, and to the widow, according to all thy comandements which thou hast commanded me: I haue transgressed none of thy comandements, nor forgotten them.
Sa’an nan ku faɗa wa Ubangiji Allahnku, “Na cire tsattsarkan rabo daga gidana na kuma ba wa Balawe, baƙo, maraya da gwauruwa, bisa ga dukan abin da ka umarta. Ban ja gefe daga umarnanka ko in manta da wani a cikinsu ba.
14 I haue not eaten therof in my mourning, nor suffred ought to perish through vncleannes, nor giuen ought thereof for the dead, but haue hearkened vnto the voyce of the Lord my God: I haue done after al that thou hast comaded me.
Ban ci wani daga cikin tsattsarkan rabo yayinda nake makoki, ko in cire wani rabo mai tsarki yayinda nake marar tsarki, ko in miƙa wani sashensa ga matattu ba. Na yi biyayya ga Ubangiji Allahna, na aikata kome da ka umarce ni.
15 Looke downe from thine holy habitation, euen from heauen, and blesse thy people Israel, and the lande which thou hast giuen vs (as thou swarest vnto our fathers) the land that floweth with milke and hony.
Ka duba ƙasa daga sama, mazauninka mai tsarki, ka albarkace mutanenka Isra’ila da kuma ƙasar da ka ba mu kamar yadda ka yi wa kakanninmu alkawari da rantsuwa, ƙasa mai zub da madara da zuma.”
16 This day the Lord thy God doeth command thee to do these ordinances, and lawes: keepe them therefore, and do them with al thine heart, and with all thy soule.
Yau Ubangiji Allahnku ya umarce ku ku bi waɗannan ƙa’idodi da kuma dokoki, cikin natsuwa ku kiyaye su da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku.
17 Thou hast set vp the Lord this day to be thy God, and to walke in his wayes, and to keepe his ordinances, and his commandements, and his lawes, and to hearken vnto his voyce.
Kun furta a wannan rana cewa Ubangiji shi ne Allahnku, cewa za ku kuma yi tafiya a hanyoyinsa, cewa za ku kiyaye ƙa’idodinsa, umarnansa da kuma dokokinsa, kuka kuma ce za ku yi masa biyayya.
18 And the Lord hath set thee vp this day, to be a precious people vnto him (as hee hath promised thee) and that thou shouldest keepe all his commandements,
Ubangiji kuwa ya furta a wannan rana cewa ku mutanensa ne, mallakarsa kamar yadda ya yi alkawari, da kuma cewa za ku kiyaye dukan umarnansa.
19 And to make thee high aboue al nations (which he hath made) in praise, and in name, and in glory, and that thou shouldest be an holy people vnto the Lord thy God, as he hath said.
Ya furta cewa zai sa ku zama masu yabo, masu suna, masu daraja, fiye da dukan al’umman da ya yi. Za ku zama jama’a tsattsarka ta Ubangiji Allahnku, kamar yadda ya yi alkawari.

< Deuteronomy 26 >