< Joshua 1 >

1 Nowe after the death of Moses the seruant of the Lord, the Lord spake vnto Ioshua the sonne of Nun, Moses minister, saying,
Bayan mutuwar Musa bawan Ubangiji, sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa ɗan Nun, mataimakin Musa,
2 Moses my seruant is dead: nowe therefore arise, go ouer this Iorden, thou, and all this people, vnto the lande which I giue them, that is, to ye children of Israel.
“Bawana Musa ya mutu. Yanzu sai ka tashi tare da mutanen nan duka, ku yi shirin ƙetare kogin Urdun zuwa cikin ƙasar da zan ba su Isra’ilawa.
3 Euery place that the sole of your foote shall treade vpon, haue I giuen you, as I said vnto Moses.
Zan ba ku duk ƙasar da za ku taka, kamar yadda na yi wa Musa alkawari.
4 From the wildernesse and this Lebanon euen vnto the great riuer, the riuer Perath: all the land of the Hittites, euen vnto the great Sea towarde the going downe of the sunne, shalbe your coast.
Ƙasar da ta kama daga hamada zuwa Lebanon, zuwa babban Kogin, wato, Kogin Yuferites, da dukan ƙasar Hittiyawa zuwa Bahar Rum, wajen yamma.
5 There shall not a man be able to withstande thee all the dayes of thy life: as I was with Moses, so will I be with thee: I will not leaue thee, nor forsake thee.
Ba wanda zai yi tsayayya da kai dukan kwanakin ranka. Yadda na kasance tare da Musa, haka zan kasance tare da kai; ba zan taɓa rabuwa da kai ba; ba zan yashe ka ba.
6 Be strong and of a good courage: for vnto this people shalt thou deuide the lande for an inheritance, which I sware vnto their fathers to giue them.
“Ka yi ƙarfin hali ka kuma kasance da rashin tsoro, gama kai za ka bi da mutanen nan har su karɓi ƙasar da na yi wa kakanninsu alkawari zan ba su.
7 Onely be thou strong, and of a most valiant courage, that thou mayest obserue and doe according to all the Lawe which Moses my seruant hath commanded thee: thou shalt not turne away from it to the right hande, nor to the left, that thou mayest prosper whithersoeuer thou goest.
Ka yi ƙarfin hali ka kuma kasance da rashin tsoro, ka yi lura fa, ka yi biyayya da dokokin da bawana Musa ya ba ka; kada ka kauce ga bin dokokin ko hagu ko dama, domin ka yi nasara a duk, inda za ka je.
8 Let not this booke of the Law depart out of thy mouth, but meditate therin day and night, that thou mayest obserue and doe according to all that is written therein: for then shalt thou make thy way prosperous, and then shalt thou haue good successe.
Kada ka bar Littafin Dokokin nan yă rabu da bakinka, sai dai ka yi ta tunani game da shi dare da rana, don ka lura, ka yi duk abin da aka rubuta a ciki, ta haka ne za ka yi nasara cikin duk abin da za ka yi.
9 Haue not I commanded thee, saying, Be strong and of a good courage, feare not, nor be discouraged? for I the Lord thy God will be with thee, whithersoeuer thou goest.
Ba ni na umarce ka ba? Ka yi ƙarfin hali ka kuma kasance da rashin tsoro. Kada ka ji tsoro; kada ka karaya, gama Ubangiji Allahnka zai kasance tare da kai duk inda za ka je.”
10 Then Ioshua commanded the officers of the people, saying,
Saboda haka sai Yoshuwa ya umarci shugabannin mutane,
11 Passe through the hoste, and commande the people, saying, Prepare you vitailes: for after three dayes ye shall passe ouer this Iorden, to goe in to possesse the lande, which the Lord your God giueth you to possesse it.
“Ku ratsa cikin sansani, ku gaya wa mutane, ‘Ku shirya guzurinku. Nan da kwana uku za ku ƙetare Urdun a nan, don ku je ka mallaki ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku ta zama taku.’”
12 And vnto the Reubenites, and to the Gadites, and to halfe the tribe of Manasseh spake Ioshua, saying,
Amma Yoshuwa ya ce wa mutanen Ruben, mutanen Gad da kuma rabin mutanen kabilar Manasse,
13 Remember the worde, which Moses the seruant of the Lord commanded you, saying, The Lord your God hath giuen you rest, and hath giuen you this land.
“Ku tuna da umarnin da Musa bawan Ubangiji ya yi muku. ‘Ubangiji Allahnku ya ba ku hutawa, ya kuma ba ku wannan ƙasa.’
14 Your wiues, your children, and your cattell shall remaine in the land which Moses gaue you on this side Iorden: but ye shall goe ouer before your brethren armed, all that be men of warre, and shall helpe them,
Matanku, da yaranku, da kuma dabbobinku za su kasance a ƙasar da Musa ya ba ku a gabashin Urdun, amma dole mayaƙanku, su yi shirin yaƙi su haye, su yi gaba tare da’yan’uwanku, za ku taimaki’yan’uwanku
15 Vntill the Lord haue giuen your brethren rest, as well as to you, and vntill they also shall possesse the land, which the Lord your God giueth them: then shall ye returne vnto the lande of your possession and shall possesse it, which land Moses the Lordes seruant gaue you on this side Iorden toward the sunne rising.
har sai lokacin da Ubangiji ya ba su hutawa, kamar yadda ya yi muku, kuma har sai su ma sun ƙwace ƙasar da Ubangiji Allahnku ya yi alkawari zai ba su. Bayan haka ne za ku koma ku mallaki ƙasarku, wadda Musa bawan Ubangiji ya ba ku a gabashin Urdun.”
16 Then they answered Ioshua, saying, Al that thou hast commanded vs, we will doe, and whithersoeuer thou sendest vs, we will goe.
Sai suka amsa wa Yoshuwa suka ce, “Duk abin da ka ce mu yi, za mu yi. Duk inda kuma ka aike mu, za mu je.
17 As we obeyed Moses in all things, so will we obey thee: onely the Lord thy God be with thee, as he was with Moses.
Kamar yadda muka yi wa Musa biyayya, haka za mu yi maka biyayya. Ubangiji Allahnka ya kasance tare da Musa.
18 Whosoeuer shall rebell against thy commandement, and will not obey thy wordes in all that thou commaundest him, let him bee put to death: onely be strong and of good courage.
Duk wanda ya yi wa maganarka tawaye, ya ƙi yă yi biyayya da maganarka, ko da umarnin da ka ba shi, za a kashe shi. Ka dai ƙarfafa ka kuma yi ƙarfi hali!”

< Joshua 1 >