< Joshua 2 >

1 Then Ioshua the sonne of Nun sent out of Shittim two men to spie secretly, saying, Go, view the land, and also Iericho: and they went, and came into an harlots house, named Rahab, and lodged there.
Sai Yoshuwa ɗan Nun ya aika’yan leƙen asiri guda biyu a ɓoye daga Shittim ya ce, “Ku je ku duba, ku ga yadda wurin yake, musamman Yeriko.” Sai suka je suka shiga gidan wata karuwa mai suna Rahab, suka sauka a can.
2 Then report was made to the King of Iericho, saying, Beholde, there came men hither to night, of the children of Israel, to spie out the countrey.
Aka gaya wa sarkin Yeriko cewa, “Ji fa, waɗansu Isra’ilawa sun shigo nan da dare don su leƙi asirin ƙasar.”
3 And the King of Iericho sent vnto Rahab, saying, Bring foorth the men that are come to thee, and which are entred into thine house: for they be come to search out all the land.
Saboda haka sai sarki ya aika wannan saƙo zuwa ga Rahab, “Ki fito da mutanen da suka zo suka sauka a gidanki, gama sun zo su leƙi asirin ƙasar ne gaba ɗaya.”
4 (But ye woman had taken the two men, and hid them) Therefore saide she thus, There came men vnto me, but I wist not whence they were.
Amma matar ta ɓoye mutanen nan biyu. Ta ce, “I, mutanen sun zo wurina, amma ban san daga ina suka zo ba,
5 And when they shut the gate in the darke, the men went out, whither the men went I wote not: follow ye after them quickly, for ye shall ouertake them.
da yamma kuwa, kafin a rufe ƙofar gari sai mutanen suka tafi. Ban san hanyar da suka bi ba, ku yi sauri ku bi su. Mai yiwuwa ku same su.”
6 (But she had brought them vp to the roofe of the house, and hidde them with the stalkes of flaxe, which she had spread abroad vpon the roofe)
(Amma ta kai su saman rufin ɗaki ta ɓoye su a ƙarƙashin karan rama da ta baza a rufin ɗaki.)
7 And certaine men pursued after them, the way to Iorden, vnto the foordes, and as soone as they which pursued after them, were gone out, they shut the gate.
Sai mutanen garin suka kama hanyar Urdun don su nemi’yan leƙen asirin, daga fitar su sai aka rufe ƙofar garin.
8 And before they were a sleepe, she came vp vnto them vpon the roofe,
Kafin’yan leƙen asirin su kwanta, sai ta tafi wurinsu a bisa rufin ɗakin
9 And saide vnto the men, I knowe that the Lord hath giuen you the land, and that the feare of you is fallen vpon vs, and that all the inhabitants of the land faint because of you.
ta ce musu, “Na sani Ubangiji ya riga ya ba ku ƙasan nan, tsoronku kuma ya kama mu har zukatan mazaunan ƙasar duka sun narke saboda ku.
10 For we haue heard, howe the Lord dried vp the water of the redde Sea before you, when you came out of Egypt, and what you did vnto the two Kings of the Amorites, that were on the other side Iorden, vnto Sihon and to Og, whom ye vtterly destroyed:
Mun ji yadda Ubangiji ya busar da ruwan Jan Teku domin ku lokacin da kuka fito daga ƙasar Masar, da kuma abin da kuka yi wa Sihon da Og, sarakunan nan biyu na Amoriyawa gabas da Urdun, waɗanda kuka hallaka su sarai.
11 And when wee heard it, our heartes did faint, and there remained no more courage in any because of you: for the Lord your God, he is the God in heauen aboue, and in earth beneath.
Da muka ji labarin, duk sai zuciyar kowa ta narke, kowa ya karaya saboda ku, gama Ubangiji Allahnku shi ne Allah na sama da ƙasa.
12 Now therefore, I pray you, sweare vnto me by the Lord; that as I haue shewed you mercie, ye will also shewe mercie vnto my fathers house, and giue me a true token,
Yanzu ina roƙonku ku rantse mini da Ubangiji cewa za ku yi wa iyalina alheri kamar yadda na yi muku alheri. Ku ba ni ƙwaƙƙwarar shaida cewa
13 And that yee will saue aliue my father and my mother, and my brethren, and my sisters, and all that they haue: and that yee will deliuer our soules from death.
za ku ceci rayukan mahaifina da mahaifiyata, da’yan’uwana maza da mata, da duk waɗanda suke nasu, za ku cece mu daga mutuwa.”
14 And the men answered her, Our life for you to die, if ye vtter not this our businesse: and when the Lord hath giuen vs the lande, we will deale mercifully and truely with thee.
Mutanen suka tabbatar mata suka ce, “Ranmu a bakin ranki! In ba ki faɗa wa kowa abin da ya kawo mu ba, za mu yi miki alheri da aminci lokacin da Ubangiji ya ba mu ƙasar.”
15 Then she let them downe by a corde thorowe the windowe: for her house was vpon the towne wall, and she dwelt vpon the wall.
Sai ta zura igiya ta taga suka bi, domin gidan da take yana haɗe da katangar birnin.
16 And she said vnto them, Goe you into the mountaine, least the pursuers meete with you, and hide your selues there three dayes, vntill the pursuers be returned: then afterwarde may yee goe your way.
Ta ce musu, “Ku tafi cikin tuddan ƙasar don kada mutanen sarki su same ku. Ku ɓuya a can na kwana uku, har sai masu nemanku su komo, sa’an nan ku kama hanyarku.”
17 And the men said vnto her, We will be blamelesse of this thine othe, which thou hast made vs sweare.
Mutanen suka ce mata, “Rantsuwar da kika sa muka yi, ba za tă yi amfani ba
18 Behold, when we come into the land, thou shalt bind this cord of red threde in the window, whereby thou lettest vs downe, and thou shalt bring thy father and thy mother, and thy brethren, and all thy fathers houshold home to thee.
sai in kin ɗaura jan ƙyalle a tagar da kika zura mu, kuma sai in kin kawo mahaifinki da mahaifiyarki, da’yan’uwanki, da dukan iyalinki cikin gidanki.
19 And whosoeuer then doeth goe out at the doores of thine house into the streete, his blood shalbe vpon his head, and we will be giltlesse: but whosoeuer shall be with thee in the house, his blood shalbe on our head, if any hande touch him:
In wani ya fita kan hanya, alhakin jininsa yă kasance a kansa; ba ruwanmu. Amma in aka taɓa wani da yake cikin gidanki tare da ke, alhakin jininsa yana kanmu.
20 And if thou vtter this our matter, we will be quite of thine othe, which thou hast made vs sweare.
In kika tone mana asiri, za mu karya alkawarin da kika sa muka yi.”
21 And she answered, According vnto your wordes, so be it: then she sent them away, and they departed, and she bound the red cord in ye window.
Ta ce, “Na yarda! Bari yă zama yadda kuka ce.” Sai ta sallame su suka tafi. Ta kuwa ɗaura jan ƙyalle a tagar.
22 And they departed, and came into the mountaine, and there abode three dayes, vntil the pursuers were returned: and the pursuers sought them throughout all the way, but founde them not.
Sai suka tafi, suka shiga cikin tuddai, suka yi zamansu a can kwana uku har masu nemansu suka koma, gama masu nemansu suka yi ta nema ko’ina a hanyar, amma ba su sami kowa ba.
23 So the two men returned, and descended from the mountaine, and passed ouer, and came to Ioshua the sonne of Nun, and tolde him all things that came vnto them.
Sa’an nan mutanen nan biyu,’yan leƙen asiri suka sauka daga tuddai suka haye kogi zuwa wurin Yoshuwa ɗan Nun, suka gaya masa duk abin da ya faru da su.
24 Also they saide vnto Ioshua, Surely the Lord hath deliuered into our handes all the lande: for euen all the inhabitants of the countrey faint because of vs.
Suka ce wa Yoshuwa, “Ba shakka Ubangiji ya ba mu ƙasan nan duka, tana hannunmu, mutane can duk sun narke da tsoro saboda mu.”

< Joshua 2 >