< Deuteronomy 19 >

1 When the Lord thy God shall roote out the nations, whose lande the Lord thy God giueth thee, and thou shalt possesse them, and dwell in their cities, and in their houses,
Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya hallakar da al’ummai waɗanda yake ba ku ƙasarsu, sa’ad da kuka kore su, kuka kuma zauna a birane da gidajensu,
2 Thou shalt separate three cities for thee in the middes of thy lande which the Lord thy God giueth thee to possesse it.
sai ku keɓe wa kanku birane uku waɗanda suke a tsakiyar ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku ku mallaka.
3 Thou shalt prepare thee the way, and deuide the coastes of the land, which the Lord thy God giueth thee to inherite, into three parts, that euery manslayer may flee thither.
Ku gina hanyoyi zuwa cikinsu, ku kuma raba ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo kashi uku, saboda duk wani da ya yi kisankai yă iya gudu zuwa can.
4 This also is ye cause wherfore the manslayer shall flee thither, and liue: who so killeth his neighbor ignorantly, and hated him not in time passed:
Ga doka game da mutumin da ya kashe wani, ya kuma gudu don yă cece ransa, wani wanda ya kashe maƙwabcinsa ba da gangan ba, ba kuwa da wata ƙiyayya a tsakaninsu a dā ba.
5 As hee that goeth vnto the wood with his neighbor to hew wood, and his hand striketh with the axe to cut downe the tree, if the head slip from the helue, and hit his neighbour that he dieth, the same shall flee vnto one of the cities, and liue,
Misali, in mutum ya je jeji da maƙwabcinsa domin yankan itace, sai ruwan gatarinsa ya kwaɓe daga ƙotar yayinda yake saran itacen, ya sari maƙwabcin har ya mutu. Mutumin nan zai iya gudu zuwa ɗaya daga cikin waɗannan birane don yă ceci ransa.
6 Least the auenger of the blood follow after the manslayer, while his heart is chafed, and ouertake him, because the way is long, and slaie him, although he be not worthy of death, because he hated him not in time passed.
In ba haka ba mai neman ɗaukan fansa jini, zai iya binsa cikin fushi, yă cim masa, saboda nisan hanyar, har ya kashe shi, ko da yake bai cancanci mutuwa ba, tun da yake ba ƙiyayya tsakaninsa da abokinsa a dā.
7 Wherefore I command thee, saying, Thou shalt appoint out three cities for thee.
Wannan ne ya sa na umarce ku ku keɓe wa kanku birane uku.
8 And when the Lord thy God enlargeth thy coastes (as he hath sworne vnto thy fathers) and giueth thee all the lande which he promised to giue vnto thy fathers,
In Ubangiji Allahnku ya fadada yankinku, kamar yadda ya alkawarta da rantsuwa wa kakanninku, ya kuma ba ku ƙasar gaba ɗaya kamar yadda ya yi musu alkawari,
9 (If thou keepe all these commandements to doe them, which I commaund thee this day: to wit, that thou loue the Lord thy God, and walke in his waies for euer) then shalt thou adde three cities moe for thee besides those three,
idan dai kun lura, kuka kiyaye umarnin da nake ba ku a yau, wato, ta wurin ƙaunar Ubangiji Allahnku, kuka kuma yi tafiya kullum cikin hanyoyinsa, to, sai ku keɓe ƙarin birane uku.
10 That innocent bloude be not shed within thy land, which the Lord thy God giueth thee to inherite, lest bloud be vpon thee.
Ku yi haka don kada a zub da jinin marar laifi a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo, don kada ku kuma zama masu laifin zub da jini.
11 But if a man hate his neighbour, and lay waite for him, and rise against him, and smite any man that he die, and flee vnto any of these cities,
Amma idan wani mutum yana ƙin maƙwabcinsa, ya kuma yi kwanto yana fakonsa, ya yi masa rauni, har ya kashe shi, sa’an nan ya gudu zuwa ɗaya daga cikin waɗannan birane,
12 Then the Elders of his citie shall send and set him thence, and deliuer him into the hands of the auenger of the blood, that he may die.
dattawan garinsa za su aika a kawo shi, a dawo da shi daga birnin, a miƙa shi ga mai neman fansar jini don yă kashe shi.
13 Thine eye shall not spare him, but thou shalt put away the crie of innocent blood from Israel, that it may goe well with thee.
Kada ku ji tausayinsa. Dole ku fid da laifin zub da jinin marar laifi daga Isra’ila, don ku sami zaman lafiya.
14 Thou shalt not remooue thy neighbours marke, which they of olde time haue set in thine inheritance, that thou shalt inherite in the lande, which ye Lord thy God giueth thee to possesse it.
Kada ka gusar da dutsen nuna shaidar iyakar maƙwabcinka wanda kakanni suka sa, a gādon da ka samu a ƙasar da Ubangiji Allahnka yake ba ka mallaka.
15 One witnes shall not rise against a man for any trespasse, or for any sinne, or for any fault that hee offendeth in, but at the mouth of two witnesses or at the mouth of three witnesses shall the matter be stablished.
Shaidar mutum guda ba tă isa a tabbatar cewa mutum yana da laifi game da laifin da ake tuhumarsa ba, ko kuwa a kan wani laifin da ake zaginsa da aikata ba. Dole a tabbata da batun ta bakin shaidu biyu, ko uku.
16 If a false witnesse rise vp against a man to accuse him of trespasse,
In wani ɗan sharri ya tashi ya yi wa wani sharri, don a sami wani da laifi,
17 Then both the men which striue together, shall stand before ye Lord, euen before the Priests and the Iudges, which shall be in those daies,
dole mutanen nan biyu da suke rikici su tsaya a gaban Ubangiji, a gaban firistoci da alƙalai waɗanda suke aiki a lokacin.
18 And the Iudges shall make diligent inquisition: and if the witnesse be found false, and hath giuen false witnes against his brother,
Dole alƙalan su yi bincike sosai, in kuma aka tabbatar mai ba da shaida maƙaryaci ne, yana ba da shaidar zur a kan ɗan’uwansa ne,
19 Then shall yee doe vnto him as hee had thought to doe vnto his brother: so thou shalt take euil away forth of the middes of thee.
to, sai a yi da shi yadda ya yi niyya yă yi da ɗan’uwansa. Dole ku fid da mugu daga cikinku.
20 And the rest shall heare this, and feare, and shall henceforth commit no more any such wickednes among you.
Sauran mutane za su ji wannan su kuma ji tsoro, ba kuwa za a ƙara yin irin wannan mugun abu a cikinku ba.
21 Therefore thine eye shall have no compassion, but life for life, eye for eye, tooth for tooth, hand for hand, foote for foote.
Kada ku ji tausayi, rai yă zama a maimakon rai, ido a maimakon ido, haƙori a maimakon haƙori, hannu a maimakon hannu, ƙafa a maimakon ƙafa.

< Deuteronomy 19 >