< Numbers 1 >

1 The Lord spake againe vnto Moses in the wildernesse of Sinai, in the Tabernacle of the Congregation, in the first day of the second moneth, in the second yere after they were come out of the land of Egypt, saying,
Ubangiji ya yi magana da Musa a Tentin Sujada a cikin Hamadar Sinai, a rana ta fari na watan biyu a shekara ta biyu, bayan Isra’ilawa suka fito Masar ya ce,
2 Take ye the summe of all the Congregation of the children of Israel, after their families, and housholdes of their fathers with the nomber of their names: to wit, all the males, man by man:
“Ka yi ƙidayan dukan al’umman Isra’ilawa bisa ga iyalansu da kabilarsu, ka rubuta kowa da sunansa bi da bi.
3 From twentie yere olde and aboue, all that go forth to the warre in Israel, thou and Aaron shall number them, throughout their armies.
Da kai da Haruna za ku lissafta dukan mazan Isra’ila bisa ga sashensu, waɗanda suka kai shekaru ashirin ko fiye, da za su iya shiga soja.
4 And with you shalbe men of euery tribe, such as are the heads of the house of their fathers.
Mutum ɗaya daga kowace kabila wanda yake shugaban danginsa, zai taimake ku.
5 And these are the names of the men that shall stand with you, of the tribe of Reuben, Elizur, the sonne of Shedeur:
“Ga sunayen da za su taimake ku. “Daga kabilar Ruben, Elizur ɗan Shedeyur;
6 Of Simeon, Shelumiel the sonne of Zurishaddai:
daga kabilar Simeyon, Shelumiyel ɗan Zurishaddai;
7 Of Iudah, Nahshon the sonne of Amminadab:
daga kabilar Yahuda, Nashon ɗan Amminadab;
8 Of Issachar, Nethaneel, the sonne of Zuar:
daga kabilar Issakar, Netanel ɗan Zuwar;
9 Of Zebulun, Eliab, the sonne of Helon:
daga kabilar Zebulun, Eliyab ɗan Helon;
10 Of the children of Ioseph: of Ephraim, Elishama the sonne of Ammihud: of Manasseh, Gamliel, the sonne of Pedahzur:
daga kabilar’ya’yan Yusuf, daga Efraim, Elishama ɗan Ammihud; daga Manasse, Gamaliyel ɗan Fedazur;
11 Of Beiamin, Abida the sonne of Gideoni:
daga kabilar Benyamin, Abidan ɗan Gideyoni;
12 Of Dan, Ahiezer, the sonne of Ammishaddai:
daga kabilar Dan, Ahiyezer ɗan Ammishaddai;
13 Of Asher, Pagiel, the sonne of Ocran:
daga kabilar Asher, Fagiyel ɗan Okran;
14 Of Gad, Eliasaph, the sonne of Deuel:
daga kabilar Gad, Eliyasaf ɗan Deyuwel;
15 Of Naphtali, Ahira the sonne of Enan.
daga kabilar Naftali, Ahira ɗan Enan.”
16 These were famous in the Congregation, princes of the tribes of their fathers, and heads ouer thousands in Israel.
Waɗannan su ne mutanen da aka naɗa daga cikin jama’a, shugabannin asalin kabilu. Su ne kuma shugabannin dangogin Isra’ila.
17 The Moses and Aaron tooke these men which are expressed by their names.
Sai Musa da Haruna suka ɗauki sunayen mutanen nan da aka ba su,
18 And they called all the Congregation together, in the first day of the second moneth, who declared their kindreds by their families, and by the houses of their fathers, according to the nomber of their names, from twentie yere olde and aboue, man by man.
suka kira dukan al’umma wuri ɗaya a rana ta fari ga wata na biyu. Aka kuwa rubuta mutanen bisa ga asalin kabilansu da iyalansu. Aka kuma rubuta sunayen maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekaru ashirin ko fiye,
19 As the Lord had commanded Moses, so he nombred them in the wildernesse of Sinai.
yadda Ubangiji ya umarci Musa. Da haka ya ƙidaya su a Hamadar Sinai.
20 So were the sonnes of Reuben Israels eldest sonne by their generations, by their families, and by the houses of their fathers, according to the nomber of their names, man by man euery male from twentie yere olde and aboue, as many as went forth to warre:
Daga zuriyar Ruben ɗan fari na Isra’ila. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
21 The nomber of them, I say, of the tribe of Reuben, was sixe and fourtie thousande, and fiue hundreth.
Jimillar maza daga mutanen Ruben 46,500 ne.
22 Of the sonnes of Simeon by their generatios, by their families, and by the houses of their fathers, the summe therof by the nomber of their names, man by man, euery male from twentie yeere olde and aboue, all that went forth to warre:
Daga zuriyar Simeyon. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
23 The summe of them, I say, of the tribe of Simeon was nine and fiftie thousande, and three hundreth.
Jimillar maza daga mutanen Simeyon 59,300 ne.
24 Of the sonnes of Gad by their generations, by their families, and by the houses of their fathers, according to the nomber of their names, from twentie yere olde and aboue, all that went forth to warre:
Daga zuriyar Gad. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
25 The number of them, I say, of the tribe of Gad was fiue and fourtie thousand, and six hundreth and fiftie.
Jimillar maza daga mutanen Gad 45,650 ne.
26 Of the sonnes of Iudah by their generations, by their families, and by the houses of their fathers, according to the nomber of their names, from twentie yere olde and aboue, all that went forth to warre:
Daga zuriyar Yahuda. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
27 The nomber of them, I say, of the tribe of Iudah was three score and fourteene thousande, and sixe hundreth.
Jimillar maza daga mutanen Yahuda 74,600 ne.
28 Of the sonnes of Issachar by their generations, by their families, and by the houses of their fathers, according to the nomber of their names, from twentie yeere olde and aboue, all that went forth to warre:
Daga zuriyar Issakar. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
29 The nomber of them also of the tribe of Issachar was foure and fiftie thousande and foure hundreth.
Jimillar maza daga mutanen Issakar 54,400 ne.
30 Of the sonnes of Zebulun by their generations, by their families, and by the houses of their fathers, according to the number of their names, from twentie yeere olde and aboue, all that went foorth to warre:
Daga zuriyar Zebulun. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
31 The nomber of them also of the tribe of Zebulun was seuen and fiftie thousand and foure hundreth.
Jimillar maza daga mutanen Zebulun 57,400 ne.
32 Of the sonnes of Ioseph, namely of the sonnes of Ephraim by their generations, by their families, and by the houses of their fathers, according to the nomber of their names, from twentie yeere olde and aboue, all that went foorth to warre:
Daga’ya’yan Yusuf. Daga zuriyar Efraim. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
33 The nomber of them also of the tribe of Ephraim was fourtie thousande and fiue hundreth.
Jimillar maza daga mutanen Efraim 40,500 ne.
34 Of the sonnes of Manasseh by their generations, by their families, and by the houses of their fathers, according to the nomber of their names, from twentie yeere olde and aboue, all that went foorth to warre:
Daga zuriyar Manasse. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
35 The nober of the also of ye tribe of Manasseh was two and thirtie thousand and two hundreth.
Jimillar maza daga mutanen Manasse 32,200 ne.
36 Of the sonnes of Beniamin by their generations, by their families, and by the houses of their fathers, according to the nomber of their names, from twentie yeere olde and aboue, all that went foorth to warre:
Daga zuriyar Benyamin. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
37 The nomber of them also of the tribe of Beniamin was fiue and thirtie thousande and foure hundreth.
Jimillar maza daga mutanen Benyamin 35,400 ne.
38 Of the sonnes of Dan by their generations, by their families, and by the houses of their fathers, according to the nomber of their names, from twentie yeere olde and aboue, all that went foorth to warre:
Daga zuriyar Dan. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
39 The nomber of the also of ye tribe of Dan was three score and two thousand and seue hudreth.
Jimillar maza daga mutanen Dan 62,700 ne.
40 Of the sonnes of Asher by their generations, by their families, and by the houses of their fathers, according to the number of their names, from twentie yeere olde and aboue, all that went foorth to warre:
Daga zuriyar Asher. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
41 The nomber of them also of ye tribe of Asher was one and fourtie thousand and fiue hudreth.
Jimillar maza daga mutanen Asher 41,500 ne.
42 Of the children of Naphtali, by their generations, by their families, and by the houses of their fathers, according to the nomber of their names, from twentie yeere olde and aboue, all that went to the warre:
Daga zuriyar Naftali. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
43 The nomber of them also of the tribe of Naphtali, was three and fiftie thousand, and foure hundreth.
Jimillar maza daga mutanen Naftali kuwa 53,400 ne.
44 These are the summes which Moses, and Aaron nombred, and the Princes of Israel, the twelue men, which were euery one for the house of their fathers.
Waɗannan su ne mazan da Musa da Haruna, tare da shugabanni goma sha biyun nan na Isra’ila suka ƙidaya, kowa a madadin iyalinsa.
45 So this was all the summe of the sonnes of Israel, by the houses of their fathers, from twenty yeere olde and aboue, all that went to the warre in Israel,
Dukan Isra’ilawan da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, an ƙidaya su bisa ga iyalansu.
46 And all they were in nomber sixe hudreth and three thousande, fiue hundreth and fiftie.
Jimillar kuwa ita ce mutum 603,550.
47 But the Leuites, after the tribes of their fathers were not nombred among them.
Ba a dai ƙidaya zuriyar Lawi tare da saura kabilan ba.
48 For the Lord had spoken vnto Moses, and said,
Ubangiji ya riga ya gaya wa Musa cewa,
49 Onely thou shalt not number the tribe of Leui, neither take the summe of them among the children of Israel:
“Ka tabbatar ba ka ƙidaya mutanen Lawi ko kuma ka haɗe su tare a ƙidayan sauran Isra’ilawa ba.
50 But thou shalt appoynt the Leuites ouer the Tabernacle of the Testimonie, and ouer all the instruments thereof, and ouer all things that belong to it: they shall beare the Tabernacle, and all the instruments thereof, and shall minister in it, and shall dwell round about the Tabernacle.
A maimakon haka sai ka naɗa Lawiyawa su lura da tabanakul Shaida, wato, kan dukan kayayyaki da kuma kome da yake na wuri mai tsarki. Za su ɗauko tabanakul da dukan kayayyakinsa; za su lura da shi, su kasance kewaye da shi.
51 And when the Tabernacle goeth forth, the Leuites shall take it downe: and when the Tabernacle is to be pitched, ye Leuites shall set it vp: for the stranger that commeth neere, shalbe slaine.
Duk sa’ad da za a gusar da tabanakul, Lawiyawa ne za su saukar da shi; kuma duk sa’ad da za a kafa shi, Lawiyawa ne za su yi haka. Duk wani dabam da ya je kusa da shi za a kashe shi.
52 Also the children of Israel shall pitch their tentes, euery man in his campe, and euery man vnder his standerd throughout their armies.
Sauran Isra’ilawa za su zauna ƙungiya-ƙungiya, kowane mutum a ƙungiyarsa daidai bisa ga ƙa’idarsa.
53 But the Leuites shall pitch rounde about the Tabernacle of the Testimonie, least vengeance come vpon the Congregation of the children of Israel, and the Leuites shall take the charge of the Tabernacle of the Testimonie.
Amma Lawiyawa za su kafa sansaninsu kewaye da tabanakul na Shaida. Don kada fushi yă fāɗo a kan al’ummar Isra’ilawa. Hakkin Lawiyawa ne su kula da tabanakul na Shaida.”
54 So the children of Israel did according to all that ye Lord had comanded Moses: so did they.
Isra’ilawa suka yi duk waɗannan kamar dai yadda Ubangiji ya umarci Musa.

< Numbers 1 >