< Zephaniah 1 >

1 The word of the Lord that came to Zephaniah the son of Cushi, the son of Gedaliah, the son of Amariah, the son of Hezekiah, in the days of Josiah the son of Amon, king of Judah.
Domin mai bi da kaɗe-kaɗe. A kan kayan kiɗi masu tsirkiyata. Maganar Ubangiji da ta zo wa Zefaniya ɗan Kushi, ɗan Gedaliya, ɗan Amariya, ɗan Hezekiya, a zamanin Yosiya ɗan Amon sarkin Yahuda.
2 While gathering, I will gather together all things from the face of the earth, says the Lord.
“Zan hallaka kome a fuskar duniya,” in ji Ubangiji.
3 I will gather man and cattle; I will gather the flying things of the air and the fish of the sea. And the impious will be a catastrophe. And I will disperse men before the face of the earth, says the Lord.
“Zan hallaka mutane da dabbobi; zan kuma hallaka tsuntsayen sama da kifayen teku, da gumakan da suke sa mugaye su yi tuntuɓe.” “Sa’ad da zan kawar da mutum daga fuskar duniya,” in ji Ubangiji.
4 And I will extend my hand over Judah and over all the inhabitants of Jerusalem. And I will disperse from this place the remnant of Baal, and the names of the administrators along with the priests,
“Zan miƙa hannuna gāba da Yahuda da kuma dukan mazaunan Urushalima. Zan datse raguwar Ba’al daga wannan wuri, da sunayen firistocin gumaka da na marasa sanin Allah,
5 and those who adore the military campaign over the ceiling of the sky, both those who adore and swear by the Lord, and those who swear by Melchom,
waɗanda suka rusuna a kan rufin ɗaki don su yi sujada ga rundunar taurari. Waɗanda suka rusuna suka kuma yi rantsuwa da sunan Ubangiji suke kuma rantsuwa da sunan Molek.
6 both those who turn aside from following after the Lord, and those who have not sought the Lord, nor inquired about him.
Waɗanda suka juya daga bin Ubangiji, ba sa kuma neman Ubangiji ko su nemi nufinsa.”
7 Be silent before the face of the Lord God. For the day of the Lord is near; for the Lord has prepared a victim, he has sanctified those he has called.
Ku yi shiru a gaban Ubangiji Mai Iko Duka, gama ranar Ubangiji ta yi kusa. Ubangiji ya shirya hadaya; ya kuma tsarkake waɗanda ya gayyato.
8 And this shall be: in the day of the victim of the Lord, I will visit upon the leaders, and upon the sons of the king, and upon all who have been clothed with strange garments.
“A ranar hadayar Ubangiji zan hukunta sarakuna da kuma’ya’yan sarakuna da duk waɗanda suke sanye da rigunan ƙasashen waje.
9 And I will visit upon all who enter arrogantly over the threshold in that day, those who fill the house of the Lord their God with iniquity and deceit.
A wannan rana zan hukunta dukan waɗanda suke kauce taka madogarar ƙofa, waɗanda suke cika haikalin allolinsu da rikici da ruɗu.
10 And this shall be in that day, says the Lord: the voice of an outcry from the fish gate, and a howling from the Second, and a great contrition from the hills.
“A wannan rana,” in ji Ubangiji, “Za a ji kuka daga Ƙofar Kifi, kururuwa daga Sabon Mazauni, da kuma amo mai ƙarfi daga tuddai.
11 Howl, inhabitants of the Pillar. All the people of Canaan have fallen silent. All were ruined who had been wrapped in silver.
Ku yi kururuwa, ku da kuke zaune a yankin kasuwa; za a hallaka dukan’yan kasuwanku, dukan waɗanda suke kasuwanci da azurfa za su lalace.
12 And this shall be in that time: I will scrutinize Jerusalem with lamps, and I will visit upon the men who have become stuck in the dregs, who say in their hearts, “The Lord will not do good, and he will not do evil.”
A wannan lokaci zan bincike Urushalima da fitilu in kuma hukunta waɗanda ba su kula ba, waɗanda suke kamar ruwan inabin da aka bar a ƙasan tukunya, waɗanda suke tsammani, ‘Ubangiji ba zai yi kome ba nagari ko mummuna.’
13 And their strength will be in plundering, and their houses in the desert. And they will build houses and not dwell in them, and they will plant vineyards and not drink their wine.
Za a washe dukiyarsu, a rurrushe gidajensu. Za su gina gidaje amma ba za su zauna a ciki ba; za su shuka inabi amma ba za su sha ruwansa ba.”
14 The great day of the Lord is near; it is near and exceedingly swift. The voice of the day of the Lord is bitter; the strong will be tested there.
Babbar ranar Ubangiji ta yi kusa, ta yi kusa kuma tana zuwa da sauri. Ku saurara! Kukan ranar Ubangiji za tă yi zafi, za a ji kururuwan jarumi a can.
15 That day is a day of wrath, a day of tribulation and anguish, a day of calamity and misery, a day of darkness and gloom, a day of clouds and whirlwinds,
Ranan nan za tă zama ranar fushi, rana ce ta baƙin ciki da azaba, rana ce ta tashin hankali da lalacewa, ranar duhu baƙi ƙirin, ranar gizagizai da baƙin duhu,
16 a day of the trumpet and the trumpet blast over fortified cities and over exalted ramparts.
rana ce ta busa ƙaho da kururuwar yaƙi gāba da birane masu mafaka, da kuma kusurwar hasumiyoyi.
17 And I will trouble men, and they will walk like the blind, because they have sinned against the Lord. And their blood will be poured out like soil, and their bodies like manure.
“Zan kawo baƙin ciki a kan mutane za su kuma yi tafiya kamar makafi, domin sun yi wa Ubangiji zunubi. Za a zubar da jininsu kamar ƙura kayan cikinsu kuma kamar najasa.
18 Neither their silver, nor their gold, will be able to free them in the day of the wrath of the Lord. All the land will be devoured in the fire of his zeal, for with all speed, he will bring to consummation every inhabitant of the land.
Azurfarsu ko zinariyarsu ba za su iya cetonsu ba a ranar fushin Ubangiji.” A cikin zafin kishinsa za a hallaka dukan duniya gama zai kawo ƙarshen dukan mazaunan duniya nan da nan.

< Zephaniah 1 >