< Habakkuk 1 >

1 The burden that Habakkuk the prophet saw.
Saƙon da annabi Habakkuk ya karɓa.
2 How long, O Lord, shall I cry out, and you will not heed? Shall I shout to you while suffering violence, and you will not save?
Har yaushe, ya Ubangiji, zan yi kukan neman taimako, amma ka ƙi ji? Ina kuka a gare ka saboda zalunci amma ba ka ce ufam ba.
3 Why have you revealed to me iniquity and hardship, to see plunder and injustice opposite me? And there has been judgment, but the opposition is more powerful.
Me ya sa ka bari ina ta kallon rashin gaskiya? Me ya sa kake barin abin da ba daidai ba? Hallaka da tashin hankali suna a gabana; ga rashin jituwa da faɗa ko’ina.
4 Because of this, the law has been torn apart, and judgment does not persevere to its conclusion. For the impious prevail against the just. Because of this, a perverse judgment is issued.
Saboda haka ba a bin doka, shari’a kuma ba ta aiki. Mugaye sun kewaye masu adalci don a hana gaskiya tă yi aiki.
5 Gaze among the nations, and see. Admire, and be astounded. For a work has been done in your days, which no one will believe when it is told.
“Ka dubi al’ummai, ka gani, ka sha mamaki. Ga shi zan yi wani abu a kwanakinka, wanda ko ma an faɗa maka ba za ka gaskata ba.
6 For behold, I will raise up the Chaldeans, a bitter and swift people, marching across the width of the earth, to possess tabernacles not their own.
Zan tā da Babiloniyawa, waɗannan marasa hankali da kuma marasa tausayi; masu gajeren haƙuri, waɗanda suke ratsa ko’ina a duniya don su ƙwace wuraren zaman da ba nasu ba.
7 It is dreadful and terrible. From themselves, judgment and their burden will issue.
Suna da bantsoro da firgitarwa; dokoki da ƙa’idodinsu ne kawai suka sani.
8 Their horses are more nimble than leopards and swifter than wolves in the evening; their horsemen will spread out. And then their horsemen will approach from far away; they will fly like the eagle, hurrying to devour.
Dawakansu sun fi damisoshi sauri, sun fi kyarketan yamma zafin rai. Mahayansu suna zuwa a guje; mahayansu daga nesa suka fito. Suna firiya kamar ungulu mai sauka da gaggawa don yă ci mushe;
9 They will all approach towards the prey; their face is like a burning wind. And they will gather captives together like sand.
duk sukan zo da nufin tā-da-na-zaune-tsaye. Ana jin tsoronsu tun ma kafin su iso suna tattara bayi kamar yashi.
10 And concerning kings, he will triumph, and sovereign rulers will be his laughingstock, and he will laugh over every fortress, and he will transport a rampart and seize it.
Sukan yi wa sarakuna ba’a su kuma rena masu mulki. Sukan yi wa dukan birane masu mafaka dariya; sukan tara ƙasa su hau, su cinye abokan gābansu da yaƙi.
11 Then his spirit will be altered, and he will cross over and fall. Such is his strength from his god.
Sa’an nan su wuce da sauri kamar iska, mutane ne masu laifi, waɗanda ƙarfinsu shi ne allahnsu.”
12 Have you not existed from the beginning, Lord my God, my holy one, and so we shall not die? Lord, you have stationed him for judgment, and you have established that his strength will be swept away.
Ya Ubangiji, ba tun fil azal kake ba? Ya Allahna, Mai Tsarkina, ba za mu mutu ba. Ya Ubangiji ka sanya su su tabbatar da hukunci; Ya Dutse, ka naɗa su don su yi hukunci.
13 Your eyes are pure, you do not behold evil, and you cannot look towards iniquity. Why do you look upon the agents of iniquity, and remain silent, while the impious is devouring one who is more just than himself?
Idanunka masu tsarki ne da suka fi gaban duban mugunta; ba ka amince da abin da ke ba daidai ba. To, don me ka ƙyale munafukai suna cin karensu ba babbaka? Me ya sa kake shiru sa’ad da mugaye suke haɗiye adalai da suka fi su adalci?
14 And you will make men like the fish of the sea and like the creeping things that have no ruler.
Ka mai da maza kamar kifin teku, kamar halittun tekun da ba su da shugaba.
15 He lifted up everything with his hook. He drew them in with his dragnet, and gathered them into his netting. Over this, he will rejoice and exult.
Mugu abokin gāba yakan kama su duka da ƙugiya, yă jawo su waje da abin kamun kifinsa, yă tattara su cikin ragarsa, ta haka yakan yi murna da farin ciki.
16 For this reason, he will offer victims to his dragnet, and he will sacrifice to his netting. For through them, his portion has been made fat, and his meals elite.
Saboda haka yakan yi hadaya wa abin kamun kifinsa yă kuma ƙona turare wa ragarsa, domin ta wurin abin kamun kifinsa ne yake yin rayuwar jin daɗi yă kuma zaɓi irin abincin da yake so.
17 Because of this, therefore, he expands his dragnet and will not be lenient in continually putting to death the peoples.
Zai ci gaba da juye abin kamun kifinsu ke nan, suna hallaka al’ummai ba tausayi?

< Habakkuk 1 >