< Haggai 1 >

1 In the second year of king Darius, in the sixth month, on the first day of the month, the word of the Lord came, by the hand of Haggai the prophet, to Zerubbabel the son of Shealtiel, governor of Judah, and to Jesus the son of Jehozadak, the high priest, saying:
A shekara ta biyu ta mulkin Sarki Dariyus, a rana ta fari ga watan shida, maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai zuwa ga Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, gwamnan Yahuda, da kuma Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist.
2 Thus says the Lord of hosts, saying: This people claims that the time has not yet arrived for building the house of the Lord.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Waɗannan mutane sun ce, ‘Lokaci bai yi ba tukuna da za a gina gidan Ubangiji.’”
3 But the word of the Lord came by the hand of Haggai the prophet, saying:
Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai cewa,
4 Is it time for you to dwell in paneled houses, while this house is deserted?
“Ashe, lokaci ya yi da za ku zauna a ɗakunan da kuka yi da rufin katako, amma haikalin nan yana zaman kufai?”
5 And now, thus says the Lord of hosts: Set your hearts upon your ways.
To, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku lura da al’amuranku.
6 You sowed much and have brought in little. You consumed and have not been satisfied. You drank and have not been inebriated. You covered yourselves and have not been warmed. And whoever gathered wages, has put them in a bag with holes.
Kun shuka da yawa, amma kun girbe kaɗan. Kun ci, amma ba ku ƙoshi ba. Kun sha, amma ba ku kashe ƙishirwa ba. Kun sa tufafi, amma ba ku ji ɗumi ba. Kuna karɓar albashi, ya zama sai ka ce kuna zuba a hudajjen aljihu.”
7 Thus says the Lord of hosts: Set your hearts upon your ways.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku lura da al’amuranku.
8 Ascend to the mountain, bring wood and build the house, and it shall be acceptable to me, and I shall be glorified, says the Lord.
Ku haura zuwa kan duwatsu ku sauko da katakai don ku gina gidan, don ni ma in ji daɗinsa, in kuma sami ɗaukaka,” in ji Ubangiji.
9 You have looked for more, and behold, it became less, and you brought it home, and I blew it away. What is the cause of this, says the Lord of hosts? It is because my house is desolate, yet you have hurried, each one to his own house.
“Ga shi, kukan sa rai za ku sami da yawa, amma sai ku ga kun sami kaɗan. Ɗan kaɗan ɗin ma da kukan kawo gida, nakan hura shi yă tafi. Me ya sa yake faruwa haka?” In ji Ubangiji Maɗaukaki. “Saboda gidana da yake zaman kango, yayinda kowannenku yana faman gina gidansa.
10 Because of this, the heavens over you have been prohibited from giving dew, and the earth has been prohibited from giving her sprouts.
Shi ya sa, saboda ku sammai sun ƙi saukar da raɓa, ƙasa kuma ta ƙi ba da amfani.
11 And I called a drought over the land, and over the mountains, and over the wheat, and over the wine, and over the oil, and whatever the soil would bring forth, and over men, and over beasts of burden, and over all the labor of hands.
Na kawo fări a ƙasar, da a kan duwatsu, da a kan hatsi, da a kan dukan abin da yake tsirowa daga ƙasa, da a kan mutane, da a kan dabbobi da kuma a kan wahalar hannuwanku.”
12 And Zerubbabel the son of Shealtiel, and Jesus the son of Jehozadak, the high priest, and all the remnant of the people heeded the voice of the Lord their God, and the words of Haggai the prophet, just as the Lord their God sent him to them. And the people were fearful before the face of the Lord.
Sa’an nan sai Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, da Yoshuwa ɗan Yehozadak, wanda yake babban firist, da kuma dukan raguwar jama’ar suka yi biyayya da muryar Ubangiji Allahnsu da kuma saƙon annabi Haggai, domin Ubangiji Allahnsu ne ya aiko shi. Mutane kuwa suka ji tsoron Ubangiji.
13 And Haggai, a messenger of the Lord among messengers of the Lord, spoke to the people, saying: the Lord says, “I am with you.”
Sai Haggai, ɗan saƙon Ubangiji, ya ba da wannan saƙo na Ubangiji ga mutane cewa, “Ina tare da ku” in ji Ubangiji.
14 And the Lord stirred the spirit of Zerubbabel the son of Shealtiel, governor of Judah, and the spirit of Jesus the son of Jehozadak, the high priest, and the spirit of the remainder of all the people. And they entered and performed work in the house of the Lord of hosts their God.
Saboda haka Ubangiji ya motsa zuciyar Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, wanda yake gwamna a Yahuda, da kuma zuciyar Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist, da kuma zukatan dukan raguwar jama’ar. Suka zo suka fara aiki a gidan Ubangiji Maɗaukaki, Allahnsu,
15 On the twenty-fourth day of the month, in the sixth month, in the second year of king Darius, they began.
a ranar ashirin da huɗu ga watan shida. A shekara ta biyu ta mulkin Sarki Dariyus,

< Haggai 1 >