< Zephaniah 2 >

1 Assemble, be gathered together, O people not worthy to be loved.
Ku tattaru, ku tattaru, Ya ku al’umma marar kunya,
2 Until the decree settles accounts, the day like dust is passing away, before which the wrath of the fury of the Lord may overcome you, before which the day of the anger of the Lord may overcome you.
kafin ƙayyadadden lokacin nan yă zo ranan nan kuma ta share ku kamar ƙaiƙayi kuma kafin fushi mai tsanani na Ubangiji yă auko muku, kafin ranar fushin Ubangiji ta auko muku.
3 Seek the Lord, all you meek of the earth; you who have been working are his judgment. Seek the just, seek the meek. So then, in some way, you might be hidden in the day of the fury of the Lord.
Ku nemi Ubangiji, dukanku ƙasashe masu tawali’u, ku da kuke yin abin da ya umarta. Ku nemi adalci da tawali’u; mai yiwuwa ku sami mafaka a ranar fushin Ubangiji.
4 For Gaza will be destroyed, and Ashkelon will be in the desert; they will expel Ashdod at midday, and Ekron will be eradicated.
Za a yashe Gaza a kuma bar Ashkelon kango. Da tsakar rana Ashdod za tă zama babu kowa a kuma tumɓuke Ekron.
5 Woe to you who inhabit the coast of the sea, you people of perdition. The word of the Lord is over you, Canaan, the land of the Philistines, and I will disperse you, so that not one inhabitant will be left.
Taku ta ƙare ku da kuke zama a bakin teku, Ya ku mutanen Keretawa; maganar Ubangiji tana gāba da ke, Ya ke Kan’ana, ƙasar Filistiyawa. “Zan hallaka ki kuma babu abin da zai rage.”
6 And the coastline of the sea will be a resting place for shepherds and a fence line for cattle.
Ƙasar da take a bakin teku, inda Keretawa suke zaune, za tă zama wurin da makiyaya da ta garken tumaki.
7 And it will be the line of him who will remain from the house of Judah. There they will pasture. In the houses of Ashkelon, they will rest towards evening. For the Lord their God will visit them, and he will turn away their captivity.
Za tă zama mallakar raguwar gidan Yahuda; a can za su sami wurin kiwo. Da yamma za su kwanta a gidajen Ashkelon. Ubangiji Allahnsu zai lura da su; zai maido musu da martabarsu.
8 I have heard about the disgrace of Moab and the blasphemies of the sons of Ammon, by which they have defamed my people and have been magnified beyond their borders.
“Na ji irin zagin da Mowab take yi, da kuma ba’ar Ammonawa, waɗanda suka zagi mutanena suna kuma yi barazana a kan ƙasarsu.
9 Because of this, as I live, says the Lord of hosts, the God of Israel, Moab will be like Sodom, and the sons of Ammon like Gomorrah, like the dryness of thorns, and piles of salt, and a desert, all the way to eternity. The remnant of my people will despoil them, and the residue of my nation will possess them.
Saboda haka, muddin ina raye,” in ji Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, “tabbatacce Mowab za tă zama kamar Sodom, Ammonawa kuma kamar Gomorra, ƙasa mai ciyayi da rammukan gishiri, ƙasa marar amfani har abada. Raguwar mutanena za su washe su; waɗanda suka rage na al’ummata za su gāda ƙasarsu.”
10 This will come upon them for their arrogance, because they have blasphemed and have been magnified over the people of the Lord of hosts.
Wannan ne zai zama sakamakon girmankansu, saboda zagi da kuma ba’ar da suka yi wa mutanen Ubangiji Maɗaukaki.
11 The Lord will be a horror over them, and he will reduce all the gods of the earth. And they will adore him, each man from his own place, all the islands of the Gentiles.
Ubangiji zai zama abin tsoro a gare su sa’ad da ya hallaka allolin ƙasar. Al’ummai a kowane bakin teku za su yi masa sujada, kowa a ƙasarsa.
12 Even so, you Ethiopians, you will be executed by my sword.
“Ku ma, ya Kushawa, za a kashe ku da takobina.”
13 And he will extend his hand over the North, and he will destroy Assur. And he will set the Beautiful in the wilderness, and in an impassable place, and like a desert.
Zai kuma miƙa hannunsa gāba da arewa yă kuma hallaka Assuriya, zai mai da Ninebe kango gaba ɗaya ta kuma zama busasshiya kamar hamada.
14 And flocks will lie down in its midst, all the beasts of the Gentiles. And the pelican and the hedgehog will stay at its threshold; the voice of the singing bird will be at the window, with the crow above its threshold, for I will diminish her strength.
Garkuna za su kwanta a can, da kowace irin halitta, Mujiyar hamada da bushiya za su zauna a kan ginshiƙanta. Kukansu za tă ratsa tagogi, ɓuraguzai za su tare ƙofofin shiga, za a kware ginshiƙan al’ul.
15 This is the glorious city, dwelling in trust, which said in her heart, “I am and there is no one other than me.” How has she become a lair for beasts in the desert? All who pass through her will hiss and wag their hand.
Birnin da yake harka ke nan da take zaune lafiya. Ta ce wa kanta, “Ni ce, kuma babu kamata.” Dubi irin kangon da ta zama mana, mazaunin namun jeji! Duk wanda ya wuce ta sai ya yi mata tsaki yana kaɗa kai.

< Zephaniah 2 >