< Numbers 18 >

1 And the Lord said to Aaron: “You, and your sons, and the house of your father with you, shall carry the iniquity of the Sanctuary. And you and your sons together shall bear the sins of your priesthood.
Ubangiji ya ce wa Haruna, “Kai da’ya’yanka, da kuma iyalin mahaifinka za ku ɗauki hakkin abin da ya shafi Tentin Sujada, kai da’ya’yanka kaɗai za ku ɗauki hakkin aikinku wanda ya shafi firistoci.
2 But take to yourselves also your brothers from the tribe of Levi, and the scepter of your father, and may they be prepared, and may they minister to you. Then you and your sons shall minister in the tabernacle of the testimony.
Ka kawo’yan’uwanka Lawiyawa daga kabilar kakanka tare da kai, don su taimake ka sa’ad da kai da’ya’yanka kuke hidima a gaban Tentin Sujada.
3 And the Levites shall stand watch by your precepts, and for all the works of the tabernacle; yet in such a manner that they shall not approach the vessels of the Sanctuary and of the altar, lest both they die, and you perish, at the same time.
Za su kasance a ƙarƙashinka, su ne kuma za su yi dukan hidima ta Tenti, amma kada su je kusa da kayayyakin wuri mai tsarki, ko bagade, in ba haka ba, da kai da su, za ku mutu.
4 But they may be with you, and they may watch over the care of the tabernacle and all its ceremonies. A foreigner shall not be mixed with you.
Za su haɗa hannu tare da kai su ɗauki nauyin lura da Tentin Sujada, dukan ayyuka a Tenti, ba kuma wanda zai zo kusa da inda kake.
5 Watch over the care of the Sanctuary, and over the ministry of the altar, lest an indignation may rise over the sons of Israel.
“Kai ne za ka ɗauki nauyin lura da wuri mai tsarki da bagade, domin kada fushi yă sāke fāɗa a kan Isra’ilawa.
6 I have given your brothers, the Levites, to you from the midst of the sons of Israel, and I have delivered them as a gift to the Lord, in order to serve in the ministries of his tabernacle.
Ni da kaina na zaɓo’yan’uwanka Lawiyawa daga cikin Isra’ilawa a matsayin kyauta a gare ku, keɓaɓɓu don Ubangiji, domin su yi hidima a Tentin Sujada.
7 But as for you and your sons: guard the priesthood. For all that pertains to the service of the altar and of what is beyond the veil shall be exercised by the priests. If any outsider will approach, he shall be killed.”
Amma kai ne kaɗai da’ya’yanka za ku yi aiki a matsayin firistoci game da kowane abu a Tentin Sujada da kuma bayan labule. Ina ba ka aikin firist, yă zama naka. Duk wani kuma da ya zo kusa da wuri mai tsarki, dole a kashe shi.”
8 And the Lord said to Aaron: “Behold, I have given you custody of my first-fruits. Everything that is sanctified by the sons of Israel I have delivered to you and your sons, for the office of the priesthood, by everlasting ordinances.
Sai Ubangiji ya ce wa Haruna, “Na ba ka aikin lura da hadayun da za a miƙa mini, dukan tsarkakan hadayun da Isra’ilawa suka ba ni, na ba ka su su zama rabonka da na’ya’yanka har abada.
9 Therefore, you shall receive these, from the things that are sanctified and offered to the Lord. Every offering, and sacrifice, and whatever is repaid to me, on behalf of sin and also for offenses, and which becomes the Holy of holies, shall be for you and for your sons.
Kai za ka riƙe sashe mafi tsarki na hadayun da suka ragu daga wuta. Daga dukan kyautai mafi tsarki na hadayun da suka miƙa mini, ko ta gari, ko don zunubi, ko kuma don laifi, wannan kashi naka ne da’ya’yanka.
10 You shall eat it in the Sanctuary. Only the males shall eat from it, because it has been consecrated for you.
Ku ci shi a matsayin abu mafi tsarki; kowane namiji zai ci. Dole ku ɗauke shi da tsarki.
11 But the first-fruits, which the sons of Israel shall vow and offer, I have given to you, and to your sons, as well as to your daughters, by a perpetual right. Whoever is clean in your house shall eat them.
“Har yanzu kuma duk abin da aka keɓe daga kyautai na dukan hadayun kaɗawa na Isra’ilawa naka ne. Na ba da wannan gare ka da’ya’yanka maza da mata, a kowane lokaci. Kowa da yake da tsarki a gidanka zai iya ci.
12 All the innermost of the oil, and of the wine, and of the grain, whatever first-fruits they offer to the Lord, I have given to you.
“Na ba ka duk man zaitun mafi kyau, da ruwan inabi mafi kyau duka, da hatsi mafi kyau duka na nunan farinsu da suke bayarwa ga Ubangiji.
13 All the first of the crops, which the soil produces and which are carried to the Lord, shall fall to your use. Whoever is clean in your house shall eat them.
Dukan nunan fari na ƙasar da suke kawo wa Ubangiji, zai zama naka. Kowa da yake da tsarki a gidanka zai iya ci.
14 All that the sons of Israel shall repay by vow shall be yours.
“Kome a Isra’ila da aka keɓe wa Ubangiji, zai zama naka.
15 Whatever goes out first from the womb, of all flesh, which they offer to the Lord, whether from men or from cattle, shall be your right; yet only in so far as, for the firstborn of man, you shall accept a price. And every animal that is unclean you shall cause to be redeemed.
Kowane haihuwar fari, ta mutum, ko ta dabba da suka miƙa wa Ubangiji, naka ne. Amma ka fanshi kowace haihuwar fari ta mutum, ko ta dabbar da take haram.
16 And its redemption shall be, after one month, five shekels of silver, by the weight of the Sanctuary. A shekel has twenty obols.
Sa’ad da suke wata ɗaya da haihuwa, dole a fanshe su a bakin shekel biyar-biyar, bisa ga ma’aunin shekel na tsattsarkan wuri da ake amfani da shi, wanda nauyinsa ya kai gera ashirin.
17 But the firstborn of a cow, or of a sheep, or of a goat, you shall not cause to be redeemed, because they have been sanctified to the Lord. Thus, their blood you shall pour out upon the altar, and their fat you shall burn as a most sweet odor to the Lord.
“Amma kada ka fanshe ɗan fari na saniya, tunkiya, ko akuya; gama suna da tsarki. Ka yayyafa jininsu a bisan bagade, ka kuma ƙone kitsensu kamar hadayar da ka yi da wuta, mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
18 Yet truly, the flesh shall fall to your use, just as the consecrated breast and the right shoulder shall be yours.
Namansu zai zama naka, haka ma ƙirji na kaɗawa da cinyar dama za su zama naka.
19 All the first-fruits of the Sanctuary, which the sons of Israel offer to the Lord, I have given to you and to your sons as well as to your daughters, as a perpetual right. It is an everlasting covenant of salt before the Lord, for you and for your sons.”
Kome da aka keɓe daga tsarkakakku hadayun da Isra’ilawa suka miƙa wa Ubangiji, na ba ka, da kai da’ya’yanka maza da mata a matsayin zaunannen rabo. Wannan madawwamin alkawarin gishiri ne a gaban Ubangiji dominka da zuriyarka.”
20 And the Lord said to Aaron: “In their land, you shall possess nothing; neither shall you have a portion among them. I am your portion and your inheritance in the midst of the sons of Israel.
Ubangiji ya ce wa Haruna, “Ba ka da gādo a ƙasarsu, ba kuwa za ka sami rabo daga cikinsu ba; ni ne rabonka da gādonka a cikin Isra’ilawa.
21 But I have given, to the sons of Levi, all the tithes of Israel as a possession, for the ministry by which they serve me in the tabernacle of the covenant,
“Na ba wa Lawiyawa dukan zakka na Isra’ilawa a matsayin gādonsu, saboda aikin da suke yi yayinda suke hidima a Tentin Sujada.
22 so that the sons of Israel may no longer approach to the tabernacle, nor commit deadly sin.
Daga yanzu zuwa gaba, kada Isra’ilawa su yi kusa da Tentin Sujada, in ba haka ba kuwa su sha hukuncin zunubinsu, su kuma mutu.
23 Only the sons of Levi may serve me in the tabernacle and may carry the sins of the people. It shall be an everlasting ordinance in your generations. They shall possess nothing else;
Lawiyawa ne za su yi aikin Tentin Sujada, su kuma ɗauki nauyin kowane laifin da aka aikata a wurin. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla ce daga yanzu har tsararraki masu zuwa. Ba za su sami gādo a cikin Isra’ilawa ba.
24 being content with the oblation of tithes, which I have separated for their uses and necessities.”
A maimako haka, na ba wa Lawiyawa zakka da Isra’ilawa suka kawo domin hadaya ga Ubangiji, a matsayin gādonsu. Shi ya sa na ce game da su, ‘Ba su da gādo a cikin Isra’ilawa.’”
25 And the Lord spoke to Moses, saying:
Ubangiji ya ce wa Musa,
26 “Instruct the Levites, and also declare to them: When you will receive, from the sons of Israel, the tithes, which I have given to you, offer their first-fruits to the Lord, that is, the tenth part of a tenth,
“Ka yi wa Lawiyawa magana, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka karɓi zakka daga Isra’ila da na ba ku gādo, dole ku miƙa kashi ɗaya bisa goma na wannan zakka a matsayin hadaya ga Ubangiji.
27 so that it may be accounted to you as an oblation of the first-fruits, as much from the threshing floors as from the oil and wine presses.
Za a lissafta hadayarku kamar hatsin da aka sussuka daga masussuka, ko ruwan inabi daga wurin matsewar inabi.
28 And offer the first-fruits of everything, from which you receive tithes, to the Lord, and give them to Aaron the priest.
Ta haka za ku miƙa hadaya ga Ubangiji daga cikin dukan zakkar da kuka karɓa daga wurin Isra’ilawa. Daga waɗannan zakka kuwa dole ku ba Haruna firist rabon Ubangiji.
29 Everything which you shall offer from the tithes, and which you shall separate as gifts to the Lord, shall be the finest and most select.
Dole ku miƙa wa Ubangiji rabo mafi kyau da kuma sashi mafi tsarki na kowane abin da aka ba ku.’
30 And you shall say to them: ‘If you offer the noble and the better of the tithes, it shall be accounted to you as if you had given from the first-fruits of the threshing floor and of the oil and wine presses.’
“Ka faɗa wa Lawiyawa cewa, ‘Sa’ad da kuka miƙa sashi mafi kyau, za a lissafta shi a matsayin abin da ya fito daga masussuka, ko wurin matsewar ruwan inabi ne.
31 And you shall eat these in all your places, both you and your families, because it is your price for the ministry, by which you serve in the tabernacle of the testimony.
Da kai da gidanka, za ku iya cin abin da ya rage a ko’ina, gama ladan aikinku ne a Tentin Sujada.
32 And you shall not sin in this way: by reserving the excellent and fat things for yourselves, lest you pollute the oblations of the sons of Israel, and lest you die.”
Ta wurin miƙa masa sashi mafi kyau, ba za ku zama masu laifi a wannan batu ba; ta haka ba za ku ƙazantar da tsarkakakkun hadayu na Isra’ilawa ba, ba kuwa za ku mutu ba.’”

< Numbers 18 >