< Numbers 16 >

1 Then, behold, Korah the son of Izhar, the son of Kohath, the son of Levi, with Dathan and Abiram, the sons of Eliab, and also On the son of Peleth, of the sons of Ruben,
Kora ɗan Izhar, wanda yake Balawe ne daga dangin Kohatawa, wata rana ya nemi Datan da Abiram’ya’yan Eliyab, da On ɗan Felet dukansu daga kabilar Ruben, suka haɗa kai
2 rose up against Moses, with two hundred fifty others of the sons of Israel, leading men of the assembly, and who, at the time of a council, would be called by name.
suka tayar wa Musa. Sai suka nemi goyon bayan sanannun shugabannin Isra’ilawa da aka naɗa a majalisa su guda 250,
3 And when they had stood against Moses and Aaron, they said: “Let it be sufficient for you that the entire multitude is of holy ones, and that the Lord is among them. Why do you elevate yourselves above the people of the Lord?”
tare kuwa suka zo wurin Musa da Haruna, suka ce musu, “Kun wuce gona da iri! Dukan jama’an nan masu tsarki ne, kowannensu, Ubangiji kuma yana tare da su. Me ya sa kuke ɗaukan kanku fiye da taron jama’ar Ubangiji?”
4 When Moses had heard this, he fell prone on his face.
Da Musa ya ji haka, sai ya fāɗi rubda ciki ya yi addu’a
5 And speaking to Korah, and to the entire multitude, he said: “In the morning, the Lord will cause it to be known who belongs to him, and which holy ones he will join to himself. And whomever he will choose, they shall be close to him.
Sai ya ce wa Kora da dukan waɗannan da suke tare shi, “Da safe, Ubangiji zai nuna wane ne yake nasa, da kuma wane ne yake da tsarki. Zai kuma sa mutumin yă zo kusa da shi. Mutumin da ya zaɓa kuwa zai sa yă zo kusa da shi.
6 Therefore, do this: Each one of you, Korah and all your associates, take your censer,
Kai Kora da ƙungiyarka, gobe, za ku ɗauki farantai,
7 and drawing fire into it tomorrow, place incense upon it before the Lord. And whomever he will choose, the same shall be holy. You sons of Levi have been raised up greatly.”
ku zuba wuta a ciki, ku kuma zuba musu turaren wuta a gaban Ubangiji. Sa’an nan wanda Ubangiji ya zaɓa a tsakaninmu sh ne mai tsarki. Ku Lawiyawa ku ne kuka wuce gona da iri!”
8 And he said again to Korah: “Listen, sons of Levi.
Musa ya kuma ce wa Kora, “Yanzu ku saurara, ku Lawiyawa!
9 Is it a small thing to you, that the God of Israel has separated you from all the people, and has joined you to himself, so that you would serve him in the rituals of the tabernacle, and stand before gatherings of the people, and minister to him?
Ashe, bai ishe ku ba, cewa Allah na Isra’ila, ya keɓe ku daga sauran jama’ar Isra’ilawa, ya kuma kawo ku kusa da shi don ku yi aiki a tabanakul na Ubangiji, ku kuma tsaya a gaba jama’a don ku yi musu aiki?
10 Was the reason that he caused you and all your brothers, the sons of Levi, to approach him, so that you would even claim for yourselves the priesthood too,
Ya kawo ku da kuma dukan’yan’uwanku Lawiyawa kusa da shi, amma yanzu kuna ƙoƙari ku karɓi aikin firist.
11 and so that your entire group would stand against the Lord? For what is Aaron that you should murmur against him?”
Kai da ƙungiyarka kun haɗa kai kuna yi wa Haruna gunaguni, amma wane ne Haruna? A zahiri tawaye ne kuke wa Ubangiji.”
12 Therefore, Moses sent to call for Dathan and Abiram, the sons of Eliab, who responded: “We will not come.
Sai Musa ya aika a kira Datan da Abiram,’ya’yan Eliyab maza, amma suka ce, “Ba za mu zo ba!
13 Is it a small matter to you, that you have led us away from a land that was flowing with milk and honey, so as to kill us in the desert, unless you could also be a ruler over us?
Bai isa ba ne da ka fitar da mu daga ƙasar mai zub da madara da zuma, ka kawo mu nan hamada don ka kashe mu? Yanzu kuma so kake ka mai da kanka sarki a bisanmu?
14 You have led us, it is true, to a land that flows with streams of milk and honey, and you have given us possession of fields and vineyards. But will you also tear out our eyes? We will not come.”
Ban da haka ma, ai, ba ka riga ka kai mu ƙasar mai zub da madara da zuma ba, ba ka ba mu gādon filaye da gonakin annabi ba, yanzu kuma kana so ka ruɗe mu. Mun ƙi, ba za mun zo ba!”
15 And Moses, being very angry, said to the Lord: “Do not look with favor on their sacrifices. You know that I have not accepted from them, at any time, so much as a young donkey, nor have I afflicted any of them.”
Sai Musa ya husata ƙwarai, ya ce wa Ubangiji, “Kada ka karɓi hadayarsu. Ban ƙwace wani jakinsu ba, ban kuwa cuce waninsu ba.”
16 And he said to Korah: “You and your congregation, stand alone before the Lord, and apart from Aaron, tomorrow.
Musa ya ce wa Kora, “Da kai da kuma dukan ƙungiyarka za ku bayyana a gaban Ubangiji gobe, kai da su. Haruna ma zai kasance a can.
17 Let each one of you take censers, and place incense in them, offering to the Lord two hundred fifty censers. Let Aaron also hold his censer.”
Kowannenku zai ɗauki faranti yă zuba turare a ciki. Wato, farantai 250 ke nan, a kuma miƙa su a gaban Ubangiji. Kai da Haruna za ku miƙa farantanku, ku ma.”
18 When they had done this, Moses and Aaron stood up,
Sai kowane mutum ya ɗauki farantinsa, ya sa wuta da kuma turare a ciki, suka tsaya da Musa da Haruna a ƙofar Tentin Sujada.
19 and, having crowded the entire multitude close to them at the door of the tabernacle, the glory of the Lord appeared to them all.
Sa’ad da Kora ya tara mabiyansa don su yi hamayya da Musa da Haruna a ƙofar Tentin Sujada, sai ɗaukakar Ubangiji ta bayyana ga dukan taron.
20 And the Lord, speaking to Moses and Aaron, said:
Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
21 “Separate yourselves from the midst of this congregation, so that I may suddenly destroy them.”
“Ku ware kanku daga taron nan don in gama da su nan take.”
22 But they fell prone on their faces, and they said, “O most strong One, the God of the spirits of all flesh, should your anger rage against all, for the sin of one?”
Amma Musa da Haruna suka fāɗi rubda ciki suka tā da murya suka ce, “Ya Allah, Allahn ruhohin dukan’yan adam, za ka husata da dukan taron ne, bayan mutum ɗaya ne ya yi zunubi?”
23 And the Lord said to Moses:
Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
24 “Instruct the entire people to separate from the tents of Korah, and Dathan, and Abiram.”
“Faɗa wa taron cewa, ‘Ku nisanci tentin Kora, da na Datan, da na Abiram.’”
25 And Moses rose up and went to Dathan and Abiram. And the elders of Israel followed him,
Musa ya tashi ya tafi wurin Datan da Abiram, dattawan Isra’ilawa kuwa suka bi shi.
26 and he said to the crowd, “Withdraw from the tabernacles of these impious men, and touch nothing which pertains to them, lest you become involved in their sins.”
Ya gargaɗe taron ya ce, “Ku ƙaurace wa tentin waɗannan mugayen mutane! Kada ku taɓa kome da yake nasu, domin kada a shafe ku saboda zunubansu.”
27 And when they had withdrawn from their tents all around, Dathan and Abiram came out and stood at the entrance of their pavilions, with their wives and children, and with all their associates.
Sai suka tashi daga inda tentin Kora, da Datan, da Abiram suke. Datan da Abiram kuwa suka fita suna tsaye tare da matansu da’ya’yansu da’yan ƙananansu a ƙofar tentinsu.
28 And Moses said: “By this shall you know that the Lord has sent me to do all that you discern, and that I have not brought these things out of my own heart:
Sai Musa ya ce musu, “Da haka za ku san cewa Ubangiji ne ya aiko ni, in yi dukan waɗannan abubuwa, ba da nufin kaina na yi su ba.
29 If these men pass away by the common death of men, or if they will be visited by a scourge, of a kind by which others are often visited, then the Lord did not send me.
In waɗannan mutane sun mutu kamar yadda mutane suke mutuwa, in abin da yakan sami kowa shi ne ya same su, to, ba Ubangiji ne ya aiko ni ba.
30 But if the Lord accomplishes something new, so that the earth opens its mouth and swallows them whole, along with everything that belongs to them, and they descend alive into the underworld, then you shall know that they have blasphemed the Lord.” (Sheol h7585)
Amma in Ubangiji ya kawo wani abu sabo, ya sa ƙasa ta buɗe bakinta, ta haɗiye su da dukan abin da suke da shi, suka gangara cikin kabari a raye, ta haka za ku sani mutanen nan sun rena Ubangiji.” (Sheol h7585)
31 Therefore, as soon as he had ceased to speak, the earth broke open under their feet.
Nan da nan da ya gama faɗi wannan, sai ƙasa ta tsage inda Datan da Abiram suke tsaye,
32 And opening its mouth, it devoured them with their tabernacles and their entire substance.
ta kuma buɗe bakinta, ta haɗiye su tare da mutanen gidansu da dukan mutanen Kora da dukan abin da yake mallakarsu.
33 And they descended alive, the ground closing around them, into the underworld, and they perished from the midst of the multitude. (Sheol h7585)
Suka gangara cikin kabari da rai, tare dukan mallakarsu; ƙasa ta rufe su, suka hallaka, suka rabu da jama’ar. (Sheol h7585)
34 Yet truly, all of Israel, which was standing all around, took flight at the clamor of those who were perishing, saying, “Lest perhaps the earth may swallow us whole also.”
Da jin kukansu, dukan Isra’ilawa da suke kewaye da su suka gudu, suna ihu, “Ƙasa za tă haɗiye mu, mu ma!”
35 Then, too, a fire, going forth from the Lord, put to death the two hundred fifty men who were offering the incense.
Sai wuta ta fito daga wurin Ubangiji ta cinye mutane 250 da suke miƙa hadaya da turare.
36 And the Lord spoke to Moses, saying:
Ubangiji ya ce wa Musa,
37 “Instruct Eleazar, the son of Aaron the priest, to take up the censers which lie in the burning, and to scatter the fire to one side and another, because they were sanctified
“Ka gaya wa Eleyazar ɗan Haruna, firist, yă kawar da farantan ƙona turare daga wurin da wutar ta cinye, yă watsar da gawayin a wani wuri, gama farantan tsarkakakku ne,
38 in the deaths of these sinners. And let him form them into plates, and affix them to the altar, because incense had been offered in them to the Lord, and they were sanctified, and so that the sons of Israel may discern in them a sign and a memorial.”
gama an yi amfani da farantan don miƙa mini turare. Sai ka ɗauki farantan mutanen da suka yi zunubin da ya jawo musu mutuwa ka ƙera farantan, ka yi murfin bagade da su, gama an miƙa su a gaban Ubangiji, suka zama tsarkakakku. Bari su zama alama ga Isra’ilawa.”
39 Therefore, Eleazar the priest took the bronze censers, by which those whom the burning devoured had made an offering, and he formed them into plates, affixing them to the altar,
Haka Eleyazar, firist, ya tattara farantan tagulla waɗanda mutanen da aka hallaka suka kawo, ya ƙera murfin bagade da su,
40 so that the sons of Israel would have, thereafter, something to admonish them, lest any stranger, or anyone who is not of the offspring of Aaron, might approach to offer incense to the Lord, and lest he endure what happened to Korah, and to all his congregation, when the Lord spoke to Moses.
yadda Ubangiji ya umarce shi, ta wurin Musa. Wannan ya zama abin tuni ga Isra’ilawa domin kada wani da ba firist ba, bai kuwa fito a cikin zuriyar Haruna ba, yă zo don yă ƙona turare a gaban Ubangiji, domin kada yă zama kamar Kora da mabiyansa.
41 Then, the following day, the entire multitude of the sons of Israel murmured against Moses and Aaron, saying: “You have put to death the people of the Lord.”
Kashegari dukan taron Isra’ilawa suka yi gunaguni a kan Musa da Haruna suka ce, “Kun kashe mutanen Ubangiji.”
42 And when there arose a sedition, and the tumult increased,
Bayan haka, sai dukan jama’a suka taru domin su nuna rashin yardansu da abin da suke zato Musa da Haruna ne suka aikata. Da suka fuskanci Tentin Sujada, nan take sai girgije ya rufe shi, ɗaukaka Ubangiji kuwa ta bayyana.
43 Moses and Aaron fled to the tabernacle of the covenant. But after they had entered it, the cloud covered it, and the glory of the Lord appeared.
Sai Musa da Haruna suka je gaban Tentin Sujada,
44 And the Lord said to Moses:
Ubangiji kuma ya ce wa Musa,
45 “Withdraw from the midst of this multitude, and I will destroy them immediately.” And while they were lying on the ground,
“Ku nisanci wannan taro, gama yanzu nan zan hallaka su.” Sai Musa da Haruna suka fāɗi rubda ciki.
46 Moses said to Aaron: “Take the censer, and draw fire into it from the altar; place incense upon it, and continue on, quickly, to the people, to pray for them. For already wrath has gone forth from the Lord, and the scourge rages.”
Sai Musa ya ce wa Haruna, “Ka ɗauki farantinka ka sa turare a ciki, da wuta daga bagade, ka yi maza ka tafi wajen taron, ka yi kafara dominsu. Gama fushin Ubangiji ya riga ya sauko; an kuma fara annoba.”
47 When Aaron had done this, and he had run into the midst of the multitude, which the burning fire was now destroying, he offered the incense.
Saboda haka Haruna ya yi kamar yadda Musa ya faɗa, ya ruga a guje zuwa tsakiyar taron. An riga an fara annobar a cikin mutane, amma Haruna ya miƙa turaren ya kuma yi kafara dominsu.
48 And standing between the dead and the living, he prayed for the people, and the scourge ceased.
Ya tsaya tsakanin matattu da masu rai, annobar kuwa ta tsaya.
49 But the number of those who were struck down was fourteen thousand men, and seven hundred, aside from those who had perished in the sedition of Korah.
Amma mutane 14,700 ne suka mutu a annobar, ban da waɗanda suka mutu a sanadin Kora.
50 And Aaron returned to Moses at the door of the tabernacle of the covenant, after the destruction quieted.
Sai Haruna ya komo wurin Musa a ƙofar Tentin Sujada, gama annobar ta ƙare.

< Numbers 16 >