< Numbers 17 >

1 And the Lord spoke to Moses, saying:
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 “Speak to the sons of Israel, and receive from each of them a rod by their kinships, from all the leaders of the tribes, twelve rods, and write the name of each one on his rod.
“Ka yi magana da Isra’ilawa, ka kuma karɓi sanduna goma sha biyu daga wurinsu, sanda guda daga kowane shugaban gidan kakanninsu. Ka rubuta sunan kowa a sandansa.
3 But the name of Aaron shall be for the tribe of Levi, and one rod separately shall contain all their families.
A kan sandan Lawi kuwa ka rubuta sunan Haruna, gama dole a sami sanda ɗaya saboda shugaban gidan kakanninsu.
4 And you shall place these in the tabernacle of the covenant before the testimony, where I will speak to you.
Ka ajiye su a Tentin Sujada, a gaba akwatin Alkawari, inda zan sadu da kai.
5 Whomever of these I will choose, his rod will germinate, and so shall I restrain the complaints of the sons of Israel before me, by which they murmur against you.”
Sandan mutumin da na zaɓa zai yi toho, da haka zan raba kaina da gunagunin da Isra’ilawa suke yi.”
6 And Moses spoke to the sons of Israel. And all the leaders gave him rods, one for each tribe. And there were twelve rods, aside from the rod of Aaron.
Saboda haka Musa ya yi magana da Isra’ilawa, sai shugabanninsu suka ba shi sanduna goma sha biyu, sanda ɗaya don shugaba, bisa ga gidajen kakanninsu, sandan Haruna kuma yana a cikinsu.
7 And when Moses had placed these before the Lord, in the tabernacle of the testimony,
Sai Musa ya ajiye sandunan a gaban Ubangiji a cikin Tentin Sujada.
8 returning on the following day, he found that the rod of Aaron for the house of Levi, had germinated, and that the swelling buds had opened into flowers, which, spreading their petals, were formed into those of an almond tree.
Kashegari da Musa ya shiga cikin Tentin Sujada sai ga sandan Haruna na gidan Lawiyawa ya yi toho, ya yi furanni, ya kuma yi’ya’yan almon.
9 Therefore, Moses brought out all the rods, from the sight of the Lord, to all the sons of Israel. And they saw, and each one received their rods.
Sai Musa ya fitar wa dukan Isra’ilawa dukan sandunan da suke daga gaban Ubangiji. Suka duba, kowa kuma ya ɗauki sandansa.
10 And the Lord said to Moses: “Carry back the rod of Aaron into the tabernacle of the testimony, so that it may be kept there as a sign of the rebellion of the sons of Israel, and so that their complaints may be quieted before me, lest they die.”
Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka mayar da sandan Haruna a akwatin Alkawari, don a ajiye shi alama ga masu tawaye. Wannan zai kawo ƙarshen gunaguninsu a kaina, domin kada su mutu.”
11 And Moses did just as the Lord had instructed.
Musa kuwa ya aikata kamar dai yadda Ubangiji ya umarce shi.
12 Then the sons of Israel said to Moses: “Behold, we have been consumed; we have been ruined.
Sai Isra’ilawa suka ce wa Musa, “To, ai in haka ne, mun ƙare ke nan!
13 Whoever approaches to the tabernacle of the Lord dies. Will we all be wiped away, even to total annihilation?”
Idan an ce duk wanda ya zo kusa da tabanakul na Ubangiji zai mutu, ai rayuwarmu kamar mun mutu ke nan.”

< Numbers 17 >