< Leviticus 1 >

1 Then the Lord called Moses and spoke to him from the tabernacle of the testimony, saying:
Ubangiji ya kira Musa ya yi masa magana daga cikin Tentin Sujada ya ce,
2 Speak to the sons of Israel, and you shall say to them: The man among you who will offer to the Lord a sacrifice from the cattle, that is, an offering of victims of oxen or sheep:
“Yi magana da Isra’ilawa ka ce musu, ‘Duk sa’ad da waninku ya kawo hadaya ga Ubangiji, ku kawo hadayarku ta dabba daga garkenku ta shanu ko kuwa daga tumakinku.
3 if his offering will be a holocaust, as well as from the herd, he shall offer an immaculate male at the door of the tabernacle of the testimony, to make himself pleasing to the Lord.
“‘In hadaya ta ƙonawar daga shanu ne, sai yă miƙa namiji marar lahani. Dole yă kawo shi a ƙofar Tentin Sujada don yă zama yardajje ga Ubangiji.
4 And he shall place his hand on the head of the sacrifice, and so it shall be acceptable and effective, in its expiation.
Zai ɗibiya hannunsa a kan hadaya ta ƙonawar, za a kuwa karɓa a madadinsa don a yi kafara dominsa.
5 And he shall immolate the calf in the sight of the Lord. And the priests, the sons of Aaron, shall offer its blood, pouring it all around the altar, which is before the door of the tabernacle.
Zai yanka ɗan bijimin a gaban Ubangiji, Haruna kuwa da’ya’yansa maza firist, za su kawo jinin su kuma yafa shi a kan bagaden a kowane gefe a mashigin Tentin Sujada.
6 And having pulled away the skin of the victim, they shall cut up the joints into pieces,
Zai feɗe hadaya ta ƙonawar, yă yayyanka shi gunduwa-gunduwa.
7 and they shall toss fire under the altar, having arranged beforehand a stack of wood.
’Ya’yan Haruna maza waɗanda suke firistoci za su hura wuta a bagade, su kuma shirya itace a kan wutar.
8 And they shall lay the parts which are cut up in order upon it: namely, the head, and all the things that adjoin to the liver,
Sa’an nan’ya’yan Haruna maza waɗanda suke firistoci za su shirya gunduwa-gunduwar haɗe da kan da kuma kitsen a kan itace mai cin wuta wanda yake a kan bagaden.
9 the intestines and feet having been washed with water. And the priest shall burn them on the altar as a holocaust and as a sweet odor to the Lord.
Zai wanke kayan cikin da kuma ƙafafun da ruwa, firist ɗin kuwa zai ƙone dukan waɗannan a kan bagade. Hadaya ce ta ƙonawa, hadaya ce kuma wadda aka yi da wuta, mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
10 But if the offering is from the flocks, a holocaust either of sheep or goats, he shall offer a male without blemish.
“‘In hadaya ta ƙonawar daga garke ne, ko na tumaki, ko na awaki, zai miƙa namiji ne marar lahani.
11 And he shall immolate it at the side of the altar which looks out toward the north, in the sight of the Lord. Yet truly, the sons of Aaron shall pour its blood upon the altar all around.
Zai yanka shi a gefen arewa na bagaden a gaban Ubangiji,’ya’yan Haruna firistoci kuwa za su yayyafa jinin dabbar a bagaden a kowane gefe.
12 And they shall divide the limbs, the head, and everything that adjoins to the liver. And they shall place them on the wood, under which the fire is to be thrown.
Zai yanka shi gunduwa-gunduwa, firist kuwa zai shirya su haɗe da kan, da kuma kitsen a kan itace mai cin wutar da yake a kan bagade.
13 Yet truly, the intestines and the feet they shall wash with water. And the priest, having offered everything, shall burn it upon the altar as a holocaust and as a most sweet odor to the Lord.
Zai wanke kayan cikin da kuma ƙafafun da ruwa, firist ɗin kuwa zai ƙone dukan waɗannan a kan bagade. Hadaya ce ta ƙonawa, hadaya ce kuma wadda aka yi da wuta, mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
14 But if the oblation of a holocaust to the Lord is of birds, either of turtledoves, or young pigeons,
“‘In hadaya ga Ubangiji ɗin, hadaya ta ƙonawa ta tsuntsaye ce, zai miƙa kurciya ko’yar tattabara.
15 the priest shall offer it at the altar: and twisting back the neck with the head, and also rupturing the place of the wound, he shall make the blood run down over the edge of the altar.
Firist zai kawo ta bagade, yă murɗe wuyan tsuntsun yă ƙone shi a kan bagade; zai tsiyaye jininsa tsuntsun a gefen bagaden.
16 Yet truly, the craw of the throat and the feathers he shall cast near the altar at the eastern section, in the place where the ashes are usually poured out.
Amma zai ɗauki kayan cikin tsuntsun da gashin yă zubar da su a gefen bagaden a wajen gabas a wurin zuba toka.
17 And he shall break its wing joints, but he shall neither cut, nor divide it with metal, and he shall burn it upon the altar, placing fire under the wood. It is a holocaust and an oblation of a most sweet odor to the Lord.
Zai tsaga shi biyu a tsaka, amma ba zai raba shi ba. Firist ɗin zai ɗibiya shi a bisa itacen da yake bisa bagaden, yă ƙone shi. Hadaya ce ta ƙonawa, hadaya ce kuma wadda aka yi da wuta, mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.

< Leviticus 1 >