< Joel 2 >

1 Blow the trumpet in Zion, wail on my holy mountain, let all the inhabitants of the land be stirred up. For the day of the Lord is on its way; for it is near:
Ku busa ƙaho a cikin Sihiyona; ku yi karar amo a tsaunina mai tsarki. Bari dukan mazaunan ƙasar su yi rawan jiki, gama ranar Ubangiji tana zuwa. Tana gab da faruwa
2 a day of darkness and gloom, a day of clouds and whirlwinds. Like the morning reaching over the mountains, they are a numerous and strong people. Nothing like them has existed since the beginning, nor will exist after them, even in the years of generation upon generation.
rana ce ta baƙin duhu ƙirin, ranar gizagizai ce baƙi ƙirin. Babbar rundunar mayaƙa mai ƙarfi tana zuwa kamar ketowar alfijir a kan duwatsu yadda ba a taɓa ganin irinta ba, ba kuwa za a ƙara ganin irinta ba har tsararraki masu zuwa.
3 Before their face is a devouring fire, and behind them is a burning flame. The land before them is like a lush garden, and behind them is a desolate desert, and there is no one who can escape them.
A gabansu wuta tana ci, a bayansu ga harshen wuta yana ci, A gabansu ƙasa ta yi kamar gonar Eden, a bayansu kuma jeji ne wofi, babu abin da ya kuɓuce musu.
4 Their appearance is like the appearance of horses, and they will rush forward like horsemen.
Suna da kamannin dawakai; suna gudu kamar dokin yaƙi.
5 Like the sound of a four-horse chariot, they will leap over the tops of the mountains. Like the sound of a burning flame devouring stubble, they are as a strong people prepared for battle.
Da motsi kamar na kekunan yaƙi sun tsallake ƙwanƙolin duwatsu, kamar ƙarar harshen wuta mai cin tattaka, kamar runduna mai ƙarfi wadda ta ja dāgār yaƙi.
6 Before their face, the people will be tortured; each one’s appearance will retreat, as if into a jar.
Da ganinsu, al’ummai sun kamu da azaba; kowace fuska ta yanƙwane.
7 They will rush forward, as if they were strong. Like valiant warriors, they will ascend the wall. The men will advance, each one on his own way, and they will not turn aside from their path.
Sukan auka kamar jarumawa; sukan hau katanga kamar sojoji. Kowa yana takawa bisa ga tsari, ba mai kaucewa.
8 And each one will not hem in his brother; every one will walk in his own rough path. Moreover, they will drop through the breach and not be harmed.
Ba sa turin juna, kowane yakan miƙe gaba. Sukan kutsa cikin abokan gāba ba mai tsai da su.
9 They will advance into the city; they will rush through the wall. They will scale the houses; they will go in through the windows, like a thief.
Sukan ruga cikin birni, suna gudu a kan katanga. Sukan hau gidaje, sukan shiga ta tagogi kamar ɓarayi.
10 Before their face, the earth has trembled, the heavens have been moved. The sun and moon have been obscured, and the stars have retracted their splendor.
A gabansu duniya takan girgiza, sararin sama kuma yakan jijjigu, rana da wata su yi duhu, taurari kuma ba sa ba da haske.
11 And the Lord has bestowed his voice before the face of his army. For its military camps are very numerous; for they are strong and they carry out his word. For the day of the Lord is great and so very terrible, and who can withstand it?
Ubangiji ya yi tsawa wa shugaban mayaƙansa; sojojinsa sun fi a ƙirge masu ƙarfi ne kuma su waɗanda suke biyayya da umarninsa. Ranar Ubangiji da girma take; mai banrazana. Wa zai iya jure mata?
12 Now, therefore, the Lord says: “Be converted to me with your whole heart, in fasting and weeping and mourning.”
“Ko yanzu”, in ji Ubangiji, “Ku juyo gare ni da dukan zuciyarku, da azumi da kuka da makoki.”
13 And rend your hearts, and not your garments, and convert to the Lord your God. For he is gracious and merciful, patient and full of compassion, and steadfast despite ill will.
Ku kyakkece zuciyarku ba rigunanku ba. Ku juyo ga Ubangiji Allahnku, gama shi mai alheri ne mai tausayi kuma mai jinkirin fushi da yawan ƙauna, yakan kuma janye daga aika da bala’i.
14 Who knows if he might convert and forgive, and bequeath a blessing after him, a sacrifice and a libation to the Lord your God?
Wa ya sani? Ko zai juya yă kuma ji tausayi yă sa mana albarka ta wurin hadaya ta gari da hadaya ta sha wa Ubangiji Allahnku.
15 Blow the trumpet in Zion, sanctify a fast, call an assembly.
A busa ƙaho a Sihiyona, a yi shelar azumi mai tsarki, a kira tsarkakan taro.
16 Gather the people, sanctify the church, unite the elders, gather together the little ones and infants at the breast. Let the bridegroom depart from his bed, and the bride from her bridal chamber.
A tattara mutane; ku tsarkake taron; ku kawo dattawa wuri ɗaya; ku kuma tara yara, da waɗanda suke shan mama. Bari ango yă bar ɗakinsa amarya kuma lolokinta.
17 Between the vestibule and the altar, the priests, the ministers of the Lord, will weep, and they will say: “Spare, O Lord, spare your people. And do not bequeath your inheritance into disgrace, so that the nations would rule over them. Why should they say among the peoples, ‘Where is their God?’”
Bari firistocin da suke yin hidima a gaban Ubangiji, su yi kuka tsakanin filin haikali da bagade. Bari su ce, “Ka cece mutanenka, ya Ubangiji. Kada ka bar gādonka yă zama abin dariya, da abin ba’a a cikin al’ummai. Me zai sa a ce a cikin mutane, ‘Ina Allahnsu yake?’”
18 The Lord has been zealous for his land, and he has spared his people.
Ta haka Ubangiji zai yi kishin ƙasarsa yă kuma ji tausayin mutanensa.
19 And the Lord responded, and he said to his people: “Behold, I will send you grain and wine and oil, and you will again be filled with them. And I will no longer give you disgrace among the Gentiles.
Ubangiji zai amsa musu ya ce, “Ina aika da hatsi, sabon ruwan inabi, da mai, isashe da zai ƙosar da ku sosai; ba kuma zan ƙara maishe ku abin dariya ga al’ummai ba.
20 And he who is from the North, I will drive far from you. And I will expel him into an impassable land, and into the desert, with his face opposite the Eastern sea, and his furthest part towards the furthest sea. And his stench will ascend, and his rottenness will ascend, because he has acted arrogantly.
“Zan kori sojojin arewa nesa da ku, in tura su cikin busasshiyar ƙasa marar amfani kuma, kuma da sawunsu na gaba zan tura su zuwa gabashin teku da kuma sawunsu na baya tura su zuwa yammanci a Bahar Rum. Warinsu kuma zai bazu; ɗoyinsu zai tashi.” Tabbatacce ya yi al’amura masu girma.
21 Earth, do not be afraid. Exult and rejoice. For the Lord has great esteem for what he has done.
Kada ki ji tsoro, ya ƙasa; ki yi murna ki kuma yi farin ciki. Tabbatacce Ubangiji ya yi abubuwa masu girma.
22 Animals of the countryside, do not be afraid. For the beauty of the wilderness has sprung forth. For the tree has borne its fruit. The fig tree and the vine have bestowed their virtue.
Kada ku ji tsoro, ya ku namun jeji, gama wuraren kiwo sun yi kore shar. Itatuwa suna ba da’ya’yansu; itacen ɓaure da na inabi suna ba da amfaninsu.
23 And you, sons of Zion, exult and rejoice in the Lord your God. For he has given you a teacher of justice, and he will make the early and the late rains descend to you, just as it was in the beginning.
Ku yi murna, ya ku mutanen Sihiyona, ku yi farin ciki cikin Ubangiji Allahnku, gama ya ba ku ruwan bazara cikin adalci. Yakan aika muku yayyafi a yalwace, na bazara da na kaka, kamar dā.
24 And the threshing floors will be filled with grain, and the presses will overflow with wine and oil.
Masussukai za su cika da hatsi; randuna za su cika da sabon ruwan inabi da mai suna zuba.
25 And I will repay you for the years which the locust, and the beetle, and the mildew, and the caterpillar consumed: my great strength which I sent upon you.
“Zan mayar muku da abin da fāra suka ci a waɗannan shekaru waɗanda ɗango da fāra masu gaigayewa, da kuma sauran fāra da tarin fāra babban mayaƙan da na aika don su fāɗa muku.
26 And you will eat with enjoyment, and you will be satisfied, and you will praise the name of the Lord your God, who has worked miracles with you, and my people will not be confounded forever.
Za ku sami a wadace ku ci, har sai kun ƙoshi, za ku kuma yabi sunan Ubangiji Allahnku, wanda ya yi muku ayyukan banmamaki; mutanena ba za su ƙara shan kunya ba.
27 And you will know that I am in the midst of Israel, and I am the Lord your God, and there is no other, and my people will not be confounded forever.
Sa’an nan za ku sani ina cikin Isra’ila, cewa ni ne Ubangiji Allahnku, babu wani kuma; mutanena ba za su ƙara shan kunya ba.
28 And after this, it will happen that I will pour out my spirit upon all flesh, and your sons and your daughters will prophesy; your elders will dream dreams, and your youths will see visions.
“Daga baya kuma, zan zuba Ruhuna a bisan dukan mutane.’Ya’yanku maza da mata za su yi annabci, tsofaffinku za su yi mafarkai, matasanku za su ga wahayoyi.
29 Moreover, in those days I will pour out my spirit upon my servants and handmaids.
Har ma a bisan bayina, maza da mata, zan zuba Ruhuna a kwanakin nan.
30 And I will grant wonders in the sky and on earth: blood and fire and the vapor of smoke.
Zan nuna abubuwan banmamaki a cikin sammai da kuma a kan duniya, za a ga jini da wuta da murtukewar hayaƙi.
31 The sun will be turned into darkness, and the moon into blood, before the great and terrible day of the Lord shall arrive.
Rana za tă duhunta wata kuma yă zama jini kafin isowar babbar ranan nan mai banrazana ta Ubangiji.
32 And it will happen that everyone who will call upon the name of the Lord will be saved. For on Mount Zion, and in Jerusalem, and in the remnant whom the Lord will call, there will be salvation, just as the Lord has said.
Amma dukan waɗanda suka nemi Ubangiji za su tsira. Kamar yadda Ubangiji ya ce, gama a Dutsen Sihiyona da Urushalima akwai ceto, a cikin waɗannan da Ubangiji ya kira.

< Joel 2 >