< Joel 1 >

1 The word of the Lord that came to Joel, the son of Pethuel.
Maganar Ubangiji wadda ta zo wurin Yowel ɗan Fetuwel.
2 Listen to this, elders, and pay close attention, all inhabitants of the land. Did this ever happen in your days or in the days of your fathers?
Ku ji wannan, ku dattawa, ku kasa kunne, dukan waɗanda suke zaune a ƙasar. Ko wani abu makamancin haka ya taɓa faruwa a kwanakinku ko a kwanakin kakanninku?
3 Talk this over with your sons, and your sons with their sons, and their sons with another generation.
Ku faɗa wa’ya’yanku, bari kuma’ya’yanku su faɗa wa’ya’yansu,’ya’yansu kuma su faɗa wa tsara ta gaba.
4 The locust has eaten what the caterpillar has left, and the beetle has eaten what the locust has left, and the mildew has eaten what the beetle has left.
Abin da ɗango ya bari fāri masu girma sun cinye; abin da fāri masu girma suka bari, burduduwa ta cinye; abin da burduduwa ta bari sauran kwari sun cinye.
5 Rouse yourselves, you drunkards, and weep and wail, all you who delight in drinking wine; for it has been cut off from your mouth.
Ku farka, ku bugaggu, ku yi kuka! Ku yi kuka da ƙarfi, ku dukan mashayan ruwan inabi; ku yi kuka mai ƙarfi saboda sabon ruwan inabi, gama an riga an ƙwace ta daga leɓunanku.
6 For a nation has ascended over my land: strong and without number. His teeth are like the teeth of a lion, and his molars are like that of a lion’s young.
Wata al’umma ta mamaye ƙasata, tana da ƙarfi ba ta kuma ƙidayuwa; tana da haƙoran zaki, da zagar zakanya.
7 He has put my vineyard into desolation, and he has pulled off the bark of my fig tree. He has stripped it bare and cast it away; its branches have become white.
Ta mayar da kuringar inabina kango ta kuma lalatar da itatuwan ɓaurena. Ta ɓamɓare bayansu duka ta kuma jefar da su ta bar rassansu fari fat.
8 Lament like a betrothed virgin, wrapped in sackcloth at the loss of the husband of her youth.
Ku yi makoki kamar budurwa a cikin tsummoki tana baƙin ciki domin mijinta na ƙuruciyarta.
9 Sacrifice and libation have perished from the house of the Lord; the priests who are ministers of the Lord have mourned.
Hadayun hatsi da hadayun sha an yanke su daga gidan Ubangiji. Firistoci suna makoki, su waɗanda suke yi wa Ubangiji hidima.
10 The region has been depopulated, the soil has mourned. For the wheat has been devastated, the wine has been disfigured, the oil has languished.
Filaye sun zama marasa amfani, ƙasa ta bushe; an lalatar da hatsi, sabon ruwan inabin ya bushe, mai kuma ba amfani.
11 The farmers have been confounded, the vineyard workers have wailed over the crop and the barley, because the harvest of the field has perished.
Ku fid da zuciya, ku manoma, ku yi ihu, ku masu noma inabi; ku yi baƙin ciki saboda alkama da sha’ir, saboda an lalata girbin filaye.
12 The vineyard is in ruin, and the fig tree has languished. The pomegranate tree, and the palm tree, and the fruit tree, and all the trees of the field have withered. For joy has been thrown into disorder before the sons of men.
Kuringar inabin ta bushe itacen ɓaure kuma ya yi yaushi,’ya’yan rumman, itacen dabino da itacen gawasa, dukan itatuwan filaye, sun bushe. Tabbatacce farin cikin’yan adam ya bushe.
13 Priests, gird yourselves and lament. Ministers of the altars, wail. Enter, ministers of my God, lie in sackcloth. For sacrifice and libation have passed away from the house of your God.
Ku sa tsummoki, ya firistoci, ku yi makoki; ku yi ihu, ku da kuke yin hidima a gaban bagade. Zo, ku kwana saye da tsummoki, ku waɗanda kuke yi wa Allahna hidima, gama an yanke hadayun hatsi da hadayun sha daga gidan Allahnku.
14 Sanctify a fast, call an assembly, gather the elders and all the inhabitants of the land into the house of your God. And cry out to the Lord:
Ku yi shelar azumi mai tsarki; ku kira tsarkakan taro. Ku kira dattawa da kuma dukan mazaunan ƙasar zuwa gidan Ubangiji Allahnku, ku kuma yi kuka ga Ubangiji.
15 “Ah, ah, ah, the day!” For the day of the Lord is near, and it will arrive, like a devastation, before the powerful.
Kaito saboda wannan rana! Gama ranar Ubangiji ta kusa, za tă zo kamar hallaka daga wurin Maɗaukaki.
16 Has not your nourishment perished from before your eyes, joy and gladness from the house of our God?
Ba a yanke abinci a idanunmu, farin ciki da kuma murna daga gidan Allahnmu ba?
17 The mules have rotted in their own manure, the barns have been demolished, the wine cellars have been destroyed, because the grain has been ruined.
Iri suna ta yanƙwanewa a busasshiyar ƙasa Ɗakunan ajiya sun lalace, an rurrushe rumbunan hatsin, gama hatsi ya ƙare.
18 Why have the animals groaned, the herds of cattle bellowed? because there is no pasture for them. Yes, and even the flocks of sheep have been lost.
Ji yadda dabbobi suke nishi! Garkunan shanu sun ruɗe saboda ba su da ciyawa, har garkunan tumaki ma suna shan wahala.
19 To you, O Lord, I will cry out, because fire has devoured the beauty of the wilderness, and the flame has burned all the trees of the countryside.
A gare ka, ya Ubangiji, nake kira, gama wuta ta cinye wurin kiwo harshen wuta kuma ya ƙone dukan itatuwan jeji.
20 Yes, and even the beasts of the field have gazed up at you, like the dry ground thirsting for rain, because the fountains of waters have dried up, and fire has devoured the beauty of the wilderness.
Har ma namun jeji suna haki gare ka; rafuffuka sun bushe wuta kuma ta cinye wurin kiwo a jeji.

< Joel 1 >