< Hosea 9 >

1 Do not choose to rejoice, Israel; do not celebrate as the crowds do. For you have been committing fornication against your God; you have loved a prize upon every threshing floor of wheat.
Kada ku yi farin ciki, ya Isra’ila; kada ku yi murna kamar waɗansu al’ummai. Gama kun yi rashin aminci ga Allahnku; kuna son hakkokin karuwa a kowace masussuka.
2 The threshing floor and the oil press will not feed them, and the wine will deceive them.
Masussukai da wuraren matsin inabi ba za su ciyar da mutane ba; sabon ruwan inabi zai kāsa musu.
3 They will not dwell in the land of the Lord. Ephraim has been returned to Egypt, and he has eaten polluted things among the Assyrians.
Ba za su ci gaba da zama a ƙasar Ubangiji ba; Efraim zai koma Masar yă kuma ci abinci marar tsarki a Assuriya.
4 They will not offer a libation of wine to the Lord, and they will not please him. Their sacrifices will be like the bread of mourners. All those who eat it will be defiled. For their bread is of their soul; it will not enter into the house of the Lord.
Ba za su zuba hadayun ruwan inabi ga Ubangiji ba, ba kuwa hadayunsu za su gamshe shi ba. Irin hadayun nan za su zama musu kamar burodin masu makoki; duk wanda ya ci su zai ƙazantu. Wannan abincin zai zama na kansu ne; ba zai zo cikin haikalin Ubangiji ba.
5 What will you do on the solemn day, on the day of the feast of the Lord?
Me za ku yi a ƙayyadaddiyar ranar bukukkuwarku, a ranakun bikin Ubangiji?
6 For, behold, they have been sent away by devastation. Egypt will gather them together; Memphis will bury them. Nettles will inherit their desired silver; the burr will be in their tabernacles.
Ko da sun kuɓuta daga hallaka, Masar za tă tattara su, Memfis kuma za tă binne su. Sarƙaƙƙiya za tă mamaye kayan azurfansu, ƙayayyuwa su tsiro a cikin tentunansu.
7 The days of visitation have arrived; the days of retribution are here. Know this, Israel: that the prophet was foolish, the spiritual man was mad, because of the multitude of your iniquities and the great extent of your foolishness.
Kwanakin hukunci suna zuwa, kwanakin ba da lissafi suna a kusa. Bari Isra’ila su san da wannan. Saboda zunubanku sun yi yawa ƙiyayyarku kuma ta yi yawa, har ake ɗauka annabi wawa ne, mutumin da aka iza kuwa mahaukaci.
8 The watcher of Ephraim was with my God. The prophet has become a snare of ruin over all his ways; insanity is in the house of his God.
Annabi, tare da Allahna, su ne masu tsaro a bisa Efraim, duk da haka tarko na jiransa a dukan hanyoyi, da kuma ƙiyayya a cikin gidan Allahnsa.
9 They have sinned profoundly, just as in the days of Gibeah. He will remember their iniquity, and he will repay their sin.
Sun nutse da zurfi cikin lalaci, kamar a kwanakin Gibeya. Allah zai tuna da muguntarsu yă kuma hukunta su saboda zunubansu.
10 I discovered Israel like grapes in the desert. Like the first fruits of the fig tree, I saw their fathers on the end of its branches. But they went in to Baal-peor, and they have been estranged by intermingling, and they have become abominable, just like the things that they chose to love.
“Sa’ad da na sami Isra’ila, ya zama kamar samun inabi a hamada; sa’ad da na ga kakanninku, ya zama kamar ganin’ya’yan itace na farko a itacen ɓaure. Amma sa’ad da suka zo Ba’al-Feyor, suka keɓe kansu wa gumaka bankunya sai suka zama abubuwan banƙyama kamar abubuwan da suke ƙauna.
11 Ephraim has chased away their glory like a bird: from birth, and from the womb, and from conception.
Darajar Efraim za tă yi firiya tă tafi kamar tsuntsu, ba haihuwa, ba juna biyu, ba ɗaukar ciki.
12 And even if they should nurture their sons, I will make them without children among men. Yes, and woe to them, when I have withdrawn from them.
Ko da sun yi renon’ya’ya, zan sa su yi baƙin cikin kowannensu. Kaitonsu sa’ad da na juya musu baya!
13 Ephraim, as I see it, was a Tyre, founded by beauty. And Ephraim will lead his sons to execution.
Na ga Efraim, kamar birnin Taya, da aka kafa a wuri mai daɗi. Amma Efraim zai fitar da’ya’yansu ga masu yanka.”
14 Give them, O Lord. What will you give them? Give them a womb without children, and dry breasts.
Ka ba su, ya Ubangiji Me za ka ba su? Ka ba su mahaifar da za su yi ɓarin ciki da busassun nono.
15 All their wickedness is in Gilgal, for I held them there, in their hatred. Because of the malice of their inventions, I will expel them from my house. I will no longer say that I love them; all their leaders have retreated.
“Saboda dukan muguntarsu a Gilgal, na ƙi su a can. Saboda ayyukansu na zunubi, zan kore su daga gidana. Ba zan ƙara ƙaunace su ba; dukan shugabanninsu’yan tawaye ne.
16 Ephraim has been struck; their root has been dried out: by no means will they yield fruit. And even if they should conceive, I will execute the most beloved of their womb.
An ka da Efraim, saiwarsu ta bushe, ba sa ba da amfani. Ko da sun haifi’ya’ya zan kashe waɗanda suka fi ƙauna.”
17 My God will cast them aside because they have not listened to him; and they will be wanderers among the nations.
Allahna zai ƙi su saboda ba su yi masa biyayya ba; za su zama masu yawo a cikin al’ummai.

< Hosea 9 >