< Hosea 10 >

1 Israel is a leafy vine, its fruit has been suitable to him. According to the multitude of his fruit, he has multiplied altars; according to the fertility of his land, he has abounded with graven images.
Isra’ila kuringa ce mai yaɗuwa; ya fitar da’ya’ya wa kansa. Yayinda’ya’yan suka ƙaru, ya gina ƙarin bagadai; da ƙasarsa ta wadata, ya yi wa keɓaɓɓun duwatsu ado.
2 His heart has been divided, so now they will cross the divide. He will break apart their images; he will plunder their sanctuaries.
Zuciyarsu masu ruɗu ne, yanzu kuwa dole su ɗauki laifinsu. Ubangiji zai rushe bagadansu yă kuma hallaka keɓaɓɓun duwatsunsu.
3 For now they will say, “We have no king. For we do not fear the Lord. And what would a king do for us?”
Sa’an nan za su ce, “Ba mu da sarki domin ba mu girmama Ubangiji ba. Amma ko da ma muna da sarki, me zai yi mana?”
4 You speak words about a useless vision, and you will strike a deal. And judgment will spring up like bitterness in the furrows of the field.
Sun yi alkawura masu yawa, suka yi rantsuwar ƙarya da kuma yarjejjeniyoyi; saboda haka ƙararraki suka taso kamar ciyayi masu dafi da aka nome a gona.
5 The inhabitants of Samaria have worshipped the calf of Bethaven. For the keepers of its temple, who had exulted over it in its glory, and its people, have mourned over it because it migrated from there.
Mutanen da suke zama a Samariya suna tsoro saboda gunki maraƙin Bet-Awen. Mutanensa za su yi makokinsa, haka ma firistocinsa matsafa, waɗanda suka yi farin ciki a kan darajarsa, don an ɗauke ta daga gare su aka kai ta zaman bauta.
6 If, indeed, it also has been offered to Assur, as a gift for the Avenging king, confusion will seize Ephraim, and Israel will be confounded by his own will.
Za a ɗauke shi a kai Assuriya kamar gandu wa babban sarki. Efraim zai sha kunya; Isra’ila zai sha kunya saboda gumakan itacensa.
7 Samaria has required her king to pass by, like foam on the face of the water.
Samariya da sarkinta za su ɓace kamar kumfa a bisa ruwaye.
8 And the heights of the idol, the sin of Israel, will be utterly destroyed. The burr and the thistle will rise up over their altars. And they will say to the mountains, ‘Cover us,’ and to the hills, ‘Fall on us.’
Za a hallaka masujadai kan tudu na mugunta zunubin Isra’ila ne. Ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya za su yi girma su rufe bagadansu. Sa’an nan za su ce wa duwatsu, “Ku rufe mu!” Ga tuddai kuma, “Ku fāɗo a kanmu!”
9 From the days of Gibeah, Israel has sinned; in this, they remained firm. The battle in Gibeah against the sons of iniquity will not take hold of them.
“Tun daga kwanakin Gibeya, kun yi zunubi, ya Isra’ila, a can kuwa kuka ci gaba. Yaƙi bai cimma masu aikata mugunta a Gibeya ba?
10 According to my desire, I will correct them. And the peoples will be gathered together over them, while they are chastised for their two iniquities.
Sa’ad da na ga dama, zan hukunta su; al’ummai za su taru su yi gāba da su don su daure su saboda zunubansu da suka riɓanya.
11 Ephraim is a heifer that has been taught to love treading out the grain, but I passed over the beauty of her neck. I will rise over Ephraim. Judah will plough; Jacob will break up the soil for himself.
Efraim horarriyar karsana ce mai son sussuka; saboda haka zan sa karkiya a kyakkyawan wuyanta. Zan bi da Efraim, Dole Yahuda yă yi noma, dole kuma Yaƙub yă ja garman noma.
12 Sow for yourselves in justice, and harvest in the mouth of mercy; renew your fallow land. But the time when you will seek the Lord is the time when he will arrive who will teach you justice.
Ku shuka wa kanku adalci, ku girbe’ya’yan jinƙai marar ƙarewa, ku kuma nome ƙasar da ba a nome ba; gama lokaci ne na neman Ubangiji, sai ya zo ya zubo adalci a kanku.
13 You have ploughed impiety; you have harvested iniquity; you have eaten the fruit of lies. For you had confidence in your ways, in the multitude of your good fortunes.
Amma kun shuka mugunta, kuka girbe mugu kuka ci’ya’yan ruɗu. Domin kun dogara da ƙarfinku da kuma a jarumawanku masu yawa,
14 A tumult will arise among your people. And all your fortifications will be laid waste, just as Salman was destroyed by the house of him that judged Baal on the day of the battle, the mother having been crushed against her sons.
hayaniyar yaƙi za tă tashi gāba da mutanenku, saboda a ragargaza kagaranku, kamar yadda Shalman ya ragargaza Bet-Arbel a ranar yaƙi, sa’ad da aka fyaɗa uwaye tare da’ya’yansu da ƙasa.
15 So has Bethel done to you, before the face of your malicious wickedness.
Haka zai faru da kai, ya Betel, domin muguntarka ta yi yawa. Sa’ad da wannan rana ta zo, za a hallaka sarkin Isra’ila ƙaƙaf.

< Hosea 10 >