< Joel 3 >

1 For, behold, in those days and in that time, when I will have converted the captivity of Judah and Jerusalem,
“A waɗancan kwanaki da kuma a wancan lokaci, sa’ad da zan maido da arzikin Yahuda da Urushalima,
2 I will gather all the Gentiles, and will lead them into the valley of Jehoshaphat. And there I will dispute with them over my people, and over Israel, my inheritance, for they have scattered them among the nations and have divided my land.
zan tattara dukan al’ummai in kuma kawo su Kwarin Yehoshafat Can zan yi musu shari’a game da gādona, mutanena Isra’ila, gama sun warwatsar da mutanena a cikin al’ummai sun kuma raba ƙasata.
3 And they have cast lots over my people; and the boy they have placed in the brothel, and the girl they have sold for wine, so that they might drink.
Sun jefa ƙuri’a a kan mutanena suna kuma sayar da yara maza don karuwanci, sun sayar da’yan matan domin ruwan inabi wanda za su sha.
4 Truly, what is there between you and me, Tyre and Sidon and all the distant places of the Philistines? How will you take vengeance on me? And if you were to revenge yourselves against me, I would deliver a repayment to you, quickly and soon, upon your head.
“Yanzu mene ne damuwarku da ni, ya Taya da Sidon da kuma dukan mazaunan yankunan Filistiya? Kuna ƙoƙari ku sāka mini don abin da na yi ne? In kuna sāka mini ne, to, da gaggawa zan mayar muku da sakayya a kanku.
5 For you have carried away my silver and gold. And my desirable and most beautiful, you have taken into your shrines.
Gama kun kwashe azurfata da zinariyata kun kuma washe dukiyata mafi kyau kun kai cikin haikalinku.
6 And you, sons of Judah and sons of Jerusalem, you have sold the sons of the Greeks, so that you might drive them far from their own territory.
Kun sayar da mutanen Yahuda da na Urushalima ga mutanen Hellenawa, don ku aika da su nesa da ƙasarsu.
7 Behold, I will raise them up from the place into which you have sold them, and I will turn back your retribution on your own head.
“Duba, zan dawo da su daga wuraren da kuka sayar da su, in kuma yi muku abin da kuka yi musu.
8 And I will sell your sons and your daughters into the hands of the sons of Judah, and they will sell them to the Sabeans, a distant nation, for the Lord has spoken.
Zan sayar da’ya’yanku maza da mata ga mutanen Yahuda, su kuma za su sayar da su ga mutanen Sabenawa, al’umma da take nesa da ku.” Ubangiji ya faɗa.
9 Proclaim this among the Gentiles: “Sanctify a war, raise up the strong. Approach, ascend, all men of war.
Ku yi shelar wannan ga al’ummai. Ku yi shirin yaƙi! Ku tā da jarumawa! Bari mayaƙa su ja kusa su kai hari.
10 Cut your ploughs into swords and your hoes into spears. Let the weak say, ‘For I am strong.’
Ku bubbuge garemaninku su zama takuba da kuma laujenku su zama māsu. Bari raunana su ce, “Ni mai ƙarfi ne!”
11 Break out and advance, all nations of the world, and gather together. There the Lord will cause all your strong ones to meet death.”
Ku gaggauta, dukanku al’ummai daga kowane ɓangare, ku tattaru a can. Ka sauko da mayaƙanka, ya Ubangiji!
12 Let them arise and ascend to the valley of Jehoshaphat. For there I will sit, so as to judge all the nations of the world.
“Bari a tā da dukan al’ummai; bari su kutsa zuwa Kwarin Yehoshafat gama a can zan zauna in shari’anta dukan al’ummai daga kowane ɓangare.
13 Send forth the sickles, because the harvest has matured. Advance and descend, for the press is full, the pressing room is overflowing. For their malice has been increasing.
Ku fito da lauje, gama girbi ya nuna. Ku zo, ku tattaka inabin, gama wurin matsewar ruwan inabi ya cika randunan tarawa kuma sun cika har suna zuba, muguntarsu da girma take!”
14 Nations, nations in the valley of being cut to pieces: for the day of the Lord fittingly takes place in the valley of being cut to pieces.
Dubun dubbai suna a cikin kwarin yanke shawara! Gama ranar Ubangiji ta yi kusa a cikin kwarin yanke shawara.
15 The sun and the moon have been darkened, and the stars have withdrawn their splendor.
Za a duhunta rana da wata, taurari kuma ba za su ba da haske ba.
16 And the Lord will roar from Zion and utter his voice from Jerusalem. And the heavens and the earth will be moved. And the Lord will be the hope of his people and the strength of the sons of Israel.
Ubangiji zai yi ruri daga Sihiyona tsawa kuma daga Urushalima; duniya da sararin sama za su yi rawan jiki. Amma Ubangiji zai zama mafakar mutanensa, mafaka ga mutanensa Isra’ila.
17 And you will know that I am the Lord your God, dwelling on Zion, my holy mountain. And Jerusalem will be holy, and strangers will not cross through it anymore.
“Sa’an nan za ku san cewa ni, Ubangiji Allahnku, ina zaune a Sihiyona, dutsena mai tsarki. Urushalima za tă zama mai tsarki; baƙi ba za su ƙara mamaye ta ba.
18 And it will happen, in that day, that the mountains will drip sweetness, and the hills will flow with milk. And the waters will pass through all the rivers of Judah. And a fountain will go forth from the house of the Lord, and it will irrigate the desert of thorns.
“A wannan rana duwatsu za su ɗiga da sabon ruwan inabi, tuddai kuma za su malmalo madara; dukan rafuffukan Yahuda za su yi ta gudano da ruwa. Maɓulɓula kuma za tă fito daga gidan Ubangiji haka ma ruwa a kwarin itatuwan ƙirya.
19 Egypt will be in desolation, and Edom will be a wilderness destroyed, because of what they have unfairly done to the sons of Judah, and because they have shed innocent blood in their land.
Amma Masar za tă zama kango, Edom kuma hamada marar amfani, saboda kama-karyar da aka yi wa mutanen Yahuda, a ƙasar da aka zub da jinin marasa laifi.
20 And Judea will be inhabited forever, and Jerusalem for generation upon generation.
Za a zauna a Yahuda har abada Urushalima kuma daga tsara zuwa tsara.
21 And I will cleanse their blood, which I had not cleansed. And the Lord will remain in Zion.
Alhakin jininsu, wanda ban gafarta ba, zan gafarta.”

< Joel 3 >