< Jeremiah 49 >

1 Against the sons of Ammon. Thus says the Lord: “Does Israel have no sons? Or is there no heir for him? Then why has Milcom possessed the inheritance of Gad, and why have his people lived in his cities?
Game da Ammonawa. Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Isra’ila ba shi da’ya’ya maza ne? Ba shi da magāda ne? To, me ya sa Molek ya mallaki Gad? Me ya sa mutanensa suka zama a garuruwansa?
2 Therefore, behold, the days are approaching, says the Lord, when I will cause the noise of battle to be heard over Rabbah of the sons of Ammon. And it will be scattered into a tumult, and her daughters will be burned with fire. And Israel shall possess those who had possessed him, says the Lord.
Amma kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan yi kirarin yaƙi a kan Rabba ta Ammonawa; zai zama tarin juji, za a sa wuta a ƙauyukan da suke kewayenta. Sa’an nan Isra’ila zai kori waɗanda suka kore shi,” in ji Ubangiji.
3 Wail, O Heshbon! For Ai has been devastated. Cry out, O daughters of Rabbah! Wrap yourselves with haircloth. Mourn and circle the hedges. For Milcom will be led into the transmigration: his priests and his leaders together.
“Ki yi kuka, ya Heshbon, gama an hallaka Ai! Ku tā da murya ku yi kuka, ya mazaunan Rabba! Ku sa tufafin makoki; ku ruga nan da can a cikin katanga, gama Molek zai tafi bauta, tare da firistocinsa da kuma fadawansa.
4 Why have you gloried in the valleys? Your valley has flowed away, O delicate daughter, for you had confidence in your treasures, and you were saying, ‘Who can approach me?’
Me ya sa kuke taƙama da kwarurukanku, taƙama da kwarurukanku masu amfani? Ya ke diya marar aminci, kin dogara a wadatarki kika kuma ce, ‘Wa zai iya fāɗa mini?’
5 Behold, I will lead a terror over you, says the Lord, the God of hosts, from those who are all around you. And you will be dispersed, each one from before your sight. There will be no one who will gather together those who are fleeing.
Zan kawo razana a kanki daga waɗanda suke kewaye da ke,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Za a kore kowannenku, babu wani da zai tattara masu gudun hijira.
6 And after this, I will cause the captives of the sons of Ammon to return, says the Lord.”
“Duk da haka, daga baya, zan maido da wadatar Ammonawa,” in ji Ubangiji.
7 Against Idumea. Thus says the Lord of hosts: “Is there no longer any wisdom in Teman? Counsel has perished from the sons. Their wisdom has become useless.
Game da Edom. Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Babu sauran hikima a Teman ne? Shawara ta ɓace daga masu basira ne? Hikimarsu ta ruɓe ne?
8 Flee and turn your backs! Descend into the chasm, O inhabitants of Dedan! For I have brought the perdition of Esau over him, the time of his visitation.
Ku juya ku gudu, ku ɓuya a cikin kogwanni masu zurfi, ku da kuke zama a Dedan, gama zan kawo masifa a kan Isuwa a lokacin da zan hukunta shi.
9 If those who gather grapes had passed by you, would they not have left behind a cluster? If there were thieves in the night, they would seize what was enough for themselves.
In masu tsinkar’ya’yan inabi suka zo maka, ba za su rage’ya’yan inabi kaɗan ba? In ɓarayi suka zo da dare, ba za su sata abin da kawai suke bukata ba?
10 Yet truly, I have stripped Esau bare. I have revealed his secrets, and he is not able to be concealed. His offspring has been devastated, with his brothers and his neighbors, and he himself will not exist.
Amma zan washe Isuwa sarai; zan bubbuɗe wuraren ɓuyarsa, don kada yă ɓoye kansa.’Ya’yansa, danginsa da maƙwabtansa za su hallaka, ba kuwa zai ƙara kasancewa ba.
11 Leave behind your orphans. I will make sure that they live. And your widows will hope in me.”
Ka bar marayunka; zan tsare ransu. Gwaurayenka kuma za su dogara a gare ni.”
12 For thus says the Lord: “Behold, those who judged that they would not drink the cup, will certainly drink. And so, will you be released as if you were innocent? You will not be released as if innocent. Instead, you shall certainly drink.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “In waɗanda ba su dace su sha kwaf ɗin ba suka sha shi, me ya sa za ka kuɓuta? Ba za ka kuɓuta ba, sai ka sha shi.
13 For I have sworn by myself, says the Lord, that Bozrah will be a desolation, and a disgrace, and a wasteland, and a curse. And all her cities will be a perpetual wilderness.
Na rantse da kaina,” in ji Ubangiji, “cewa Bozra za tă zama kufai da kuma abin tsoro, abin dariya da abin la’ana; kuma dukan garuruwanta za su kasance kufai har abada.”
14 I have heard a report from the Lord, and a legate has been sent to the nations: ‘Gather yourselves together, and go forth against her, and let us rise up to battle.’
Na ji saƙo daga Ubangiji cewa; an aiki jakada zuwa ga al’ummai ya ce, “Ku tattara kanku don ku fāɗa mata! Ku tashi don yaƙi!”
15 For behold, I have made you little among the nations, contemptible among men.
“Yanzu zan mai da kai ƙanƙani a cikin al’ummai abin reni a cikin mutane.
16 Your arrogance has deceived you, by the pride of your heart, you who live in the caverns of the rock and who strive to take hold of the height of the hill. But even if you make your nest like that of an eagle, I will pull you down from there, says the Lord.
Tsoron da ka sa ake ji da kuma girman kan zuciyarka ya ruɗe ka, kai da kake zama a kogon dutse, kai da kake kan tudu. Ko da yake ka gina wa kanka sheƙa can bisa kamar na gaggafa, daga can zan sauko da kai ƙasa,” in ji Ubangiji.
17 And Idumea will be a desert. Everyone who passes by it will be stupefied and will hiss over all its wounds.
“Edom za tă zama abin tsoro; dukan wanda ya wuce zai giggice ya yi tsaki saboda dukan mikinta.
18 Just as Sodom and Gomorrah and their neighbors were overthrown, says the Lord: there will not be a man living there, and no son of man will tend it.
Kamar yadda aka tumɓuke Sodom da Gomorra, tare da garuruwan da suke maƙwabtaka da su,” in ji Ubangiji, “haka ba wanda zai zauna a can; ba wani da zai zauna a cikinta.
19 Behold, he will ascend like a lion from the arrogance of the Jordan, against the robust beauty. For I will cause him to rush against her suddenly. And who will be the elect one, whom I may appoint over her? For who is like me? And who can endure me? And who is that pastor who can withstand my countenance?
“Kamar zaki mai haurawa daga kurmin Urdun zuwa wurin kiwo mai kyau, zan kori Edom daga ƙasarta nan da nan. Wane ne zaɓaɓɓen da zan naɗa don wannan? Wane ne yake kama da ni kuma wa zai kalubalance ni? Kuma wane makiyayi ne zai yi gāba da ni?”
20 Because of this, listen to the counsel of the Lord, which he has undertaken concerning Edom, and to his thoughts, which he has devised concerning the inhabitants of Teman. Certainly, the little ones of the flock will cast them down, unless they scatter them with their habitation.
Saboda haka, ku ji abin da Ubangiji ya shirya a kan Edom, abin da ya nufa wa waɗanda suke zama a Teman. Za a ja ƙanana na garken tumaki a tafi; zai hallaka wurin kiwonsu sarai saboda su.
21 The earth has been shaken at the noise of their destruction. The outcry of their voice has been heard at the Red Sea.
Amon fāɗuwarsu zai sa ƙasa ta girgiza; za a kuma ji muryar kukansu a Jan Teku.
22 Behold, he will ascend like an eagle and will fly. And he will spread his wings over Bozrah. And in that day, the heart of the strong ones of Idumea will be like the heart of a woman giving birth.”
Duba! Gaggafa tana firiya tana kuma saukowa, tana buɗe fikafikanta a bisa Bozra. A wannan rana zukatan jarumawan Edom za su zama kamar macen da take naƙuda.
23 Against Damascus. “Hamath has been confounded, with Arpad. For they have heard a most grievous report. They have been stirred up like the sea. Because of anxiousness, they were not able to rest.
Game da Damaskus. “Hamat da Arfad sun giggice, gama sun ji mummunar labari. Suna damuwa, sun damu kamar tekun da baya hutu.
24 Damascus has been broken. She has been turned to flight. Trembling has taken hold of her. Anguish and sorrows have seized her, like a woman giving birth.
Damaskus ta karai ta juya don ta gudu tsoro kuma ya kama ta; wahala da zafi sun kama ta, zafi kamar na mace mai naƙuda.
25 How could they have abandoned the praiseworthy city, the city of rejoicing?
Me ya sa ba a tafi aka bar sanannen birnin nan ba, birnin da nake jin daɗi?
26 For this reason, her young men will fall in her streets. And all the men of battle will be silenced in that day, says the Lord of hosts.
Tabbatacce, samarinta za su fāɗi a tituna; dukan sojojinta za su yi shiru a wannan rana,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
27 And I will kindle a fire at the wall of Damascus, and it will devour the defensive walls of Ben-hadad.”
“Zan cinna wa katangar Damaskus wuta; za tă ci kagaran Ben-Hadad.”
28 Against Kedar and against the kingdoms of Hazor, which Nebuchadnezzar, the king of Babylon, has struck down. Thus says the Lord: “Rise up and ascend to Kedar, and lay waste to the sons of the East.
Game da Kedar da mulkokin Hazor, waɗanda Nebukadnezzar sarkin Babilon ya fāɗa wa. Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Tashi, ku fāɗa wa Kedar ku kuma hallaka mutanen Gabas.
29 They will seize their tabernacles and their flocks. And they will take for themselves their tents, and all their vessels, and their camels. And they will call down a terror upon them on every side.
Za a ƙwace tentunansu da garkunansu; za a tafi da mafakanta tare da dukan kayayyakinsu da raƙumansu. Mutane za su yi musu ihu, ‘Razana ko’ina!’
30 Flee, go away urgently! Sit in deep pits, you who inhabit Hazor, says the Lord. For Nebuchadnezzar, the king of Babylon, has undertaken a counsel against you, and he has devised plans against you.
“Ku yi maza ku gudu! Ku zauna a kogo masu zurfi, ku da kuke zama a Hazor,” in ji Ubangiji. “Nebukadnezzar sarkin Babilon ya shirya muku maƙarƙashiya; ya ƙulla maƙarƙashiya a kanku.
31 Rise up, and ascend to a nation that is quiet and lives in confidence, says the Lord. They have neither gates nor bars. They dwell alone.
“Ku tashi ku kuma fāɗa wa al’umma da sauƙi wadda take zama da ƙarfin hali,” in ji Ubangiji, “al’ummar da ba ta da ƙofofi ko ƙyamare; mutanenta suna zama su kaɗai.
32 And their camels will be a spoil, and the multitude of their cattle will be a prey. And I will disperse, into every wind, those who have shaved their hair. And from all their confines, I will lead great destruction over them, says the Lord.
Za a washe raƙumansu, garkunansu mai girma za su zama ganima. Zan watsar da waɗanda suke a wurare masu nesa a ko’ina zan kuma kawo musu masifa a kowane gefe,” in ji Ubangiji.
33 And Hazor will be a habitation for serpents, deserted even unto eternity. No man will abide there, nor will a son of man tend it.”
“Hazor za tă zama mazaunin diloli, kufai har abada. Ba wanda zai zauna a can; ba wanda zai zauna a cikinta.”
34 The word of the Lord that came to Jeremiah the prophet against Elam, in the beginning of the reign of Zedekiah, the king of Judah, saying:
Ga maganar Ubangiji da ta zo wa Irmiya annabi game da Elam, a farkon mulkin Zedekiya sarkin Yahuda.
35 “Thus says the Lord of hosts: Behold, I will break the bow of Elam, and the summit of their strength.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Ga shi, zan karye ƙarfin Elam, zaunannen ƙarfinsu.
36 And I will lead the four winds over Elam, from the four corners of heaven. And I will scatter them into all these winds. And there will be no nation to which the fugitives of Elam will not travel.
Zan kawo a kan Elam a kusurwoyi huɗu daga kusurwoyi huɗu na duniya; zan watsar da su zuwa kusurwoyi huɗu, kuma ba al’ummar da masu gudun hijirar Elam ba za su kai ba.
37 And I will cause Elam to be terrified before their enemies and in the sight of those who seek their life. And I will lead an evil over them, the wrath of my fury, says the Lord. And I will send the sword after them, until I consume them.
Zan ragargaza Elam a gaban maƙiyansu, a gaban waɗanda suke neman ransu; zan kawo masifa a kansu, da zafin fushina,” in ji Ubangiji. “Zan runtume su da takobi sai na kawo ƙarshensu.
38 And I will set my throne in Elam, and I will perish the kings and princes from there, says the Lord.
Zan sa kursiyina a Elam in kuma hallaka sarkinta da fadawanta,” in ji Ubangiji.
39 But in the last days, I will cause the captives of Elam to return, says the Lord.”
“Duk da haka zan maido da wadatar Elam a kwanaki masu zuwa,” in ji Ubangiji.

< Jeremiah 49 >