< Jeremiah 50 >

1 The word that the Lord has spoken about Babylon and about the land of the Chaldeans, by the hand of Jeremiah the prophet.
Ga maganar Ubangiji da ya yi ta wurin Irmiya annabi game da Babilon da kuma ƙasar Babiloniyawa.
2 “Announce it among the Gentiles, and make it known. Lift up a sign. Proclaim it and do not conceal it. Say this: ‘Babylon has been captured. Bel has been confounded. Merodach has been conquered. Their graven things have been confounded. Their idols have not survived.’
“Ka yi shela ka kuma furta a cikin al’ummai, ka tā da tuta ka kuma furta; kada ku ɓoye kome, amma ku ce, ‘Za a ci Babilon da yaƙi; za a kunyata Bel, Marduk ya cika da tsoro. Siffofinta za su sha kunya gumakanta za su cika da tsoro.’
3 For a nation has ascended against her from the north, which will set her land in desolation. And there will be no one who may live within it, from man even to beast. For they have been removed and have gone away.
Al’umma daga arewa za tă fāɗa mata su mai da ƙasar kango. Ba wanda zai zauna a cikinta; mutane da dabbobi za su gudu.
4 In those days and in that time, says the Lord, the sons of Israel will advance, they and the sons of Judah together. Weeping as they walk, they will hurry on, and they will seek the Lord their God.
“A kwanakin nan, a wannan lokaci,” in ji Ubangiji, “mutanen Isra’ila da mutanen Yahuda gaba ɗaya za su tafi cikin hawaye su nemi Ubangiji Allahnsu.
5 They will ask the way to Zion; their faces will be set toward this place. They will arrive and will be joined to the Lord by an everlasting covenant, which nothing will wipe away into oblivion.
Za su tambayi hanyar zuwa Sihiyona su kuma juya fuskokinsu wajenta. Za su zo su haɗa kansu ga Ubangiji a madawwamin alkawari da ba za a manta da shi ba.
6 My people have become a lost flock. Their shepherds have led them astray and have caused them to wander in the mountains. They have crossed from mountain to hill. They have forgotten their resting place.
“Mutanena sun zama ɓatattun tumaki; makiyayansu sun bauɗar da su suka sa suna ta yawo a cikin duwatsu. Sun yi ta yawo a bisa dutse da tudu suka manta wurin hutunsu.
7 All whom they have found, they have devoured. And their enemies have said: ‘We have not sinned. For it is they who have sinned against the Lord, the beauty of justice, and against the Lord, the hope of their fathers.’
Duk wanda ya same su ya cinye su; abokan gābansu suka ce, ‘Ba mu da laifi, gama sun yi zunubi wa Ubangiji, wurin kiwonsu na gaske, Ubangiji, abin sa zuciyar kakanninsu.’
8 Withdraw from the midst of Babylon, and go forth from the land of the Chaldeans. And be like young goats before the flock.
“Ku gudu daga Babilon; ku bar ƙasar Babiloniyawa, ku zama kamar awakin da suke bi da garke.
9 For behold, I am raising up, and I will lead against Babylon, a congregation of great nations from the land of the north. And they will be prepared against her, and from there she will be taken. Their arrows, like those of a strong man, a killer, will not return empty.
Gama zan kuta in kuma kawo a kan Babilon haɗinkan manyan al’ummai na arewa. Za su ja dāgār gāba da ita, kuma daga arewa za a ci ta da yaƙi. Kibiyoyinsu za su zama kamar na gwanayen jarumawa waɗanda ba sa dawowa hannu wofi.
10 And Chaldea will become a prey. All who lay waste to her will be filled, says the Lord.
Saboda haka za a washe Babiloniyawa; dukan waɗanda suka washe ta za su ƙoshi,” in ji Ubangiji.
11 For you exult and you speak great things, plundering my inheritance. For you have spread out like calves upon the grass, and you have bellowed like bulls.
“Saboda kuna farin ciki kuna kuma murna, ku da kuka washe gādona, domin kuna tsalle kamar karsana mai sussuka hatsi kuna kuma haniniya kamar ingarmu.
12 Your mother has been exceedingly shamed, and she who bore you has become equal to the dust. Behold, she will be the last among the nations, a desert, impassable and dry.
Mahaifiyarku za tă sha babbar kunya; ita da ta haife ku za tă sha kunya. Za tă zama mafi ƙanƙanta na al’ummai, jeji, busasshiyar ƙasa, hamada.
13 By the wrath of the Lord, it will not be inhabited. Instead, it will be entirely desolate. Everyone who passes by Babylon will be stupefied and will hiss over all her wounds.
Saboda fushin Ubangiji ba za tă zauna a cikinta ba amma za tă zama kufai gaba ɗaya. Duk waɗanda suka wuce Babilon za su ji tsoro su kuma yi tsaki saboda dukan mikinta.
14 Prepare yourselves against Babylon, on every side, all you who bend the bow. Make war against her! You should not spare the arrows, for she has sinned against the Lord.
“Ku ja dāgā kewaye da Babilon, dukanku waɗanda kuke jan baka. Ku harbe ta! Kada ku rage kibiyoyi, gama ta yi zunubi ga Ubangiji.
15 Cry out against her! For where she has put forth a hand, her foundations have fallen, her walls have been destroyed. For it is the vengeance of the Lord. Take vengeance against her! Just as she has done, do so to her.
Ku yi kuwwa a kanta a kowane gefe! Ta miƙa wuya, hasumiyarta ta fāɗi, katangarta sun rushe. Da yake wannan sakayya ce ta Ubangiji, ku ɗauki fansa a kanta; yi mata yadda ta yi wa waɗansu.
16 Destroy the founder from Babylon, and the one who holds the sickle in the time of harvest. Before the face of the sword of the dove, each one will turn back to his people, and every one will flee to his own land.
Ku datse wa Babilon mai shuka, da mai girbi lauje a lokacin girbi. Saboda takobin mai zalunci bari kowa ya koma ga mutanensa, bari kowa ya gudu zuwa ga ƙasarsa.
17 Israel is a scattered flock. The lions have driven him away. First, the king of Assyria devoured him. And last, this Nebuchadnezzar, the king of Babylon, has taken away his bones.
“Isra’ila garke ne da ya watse da zakoki suka kora. Na farkon da ya cinye shi sarkin Assuriya ne; na ƙarshen da ya ragargaza ƙasusuwansa Nebukadnezzar sarkin Babilon ne.”
18 Because of this, thus says the Lord of hosts, the God of Israel: Behold, I will visit the king of Babylon and his land, just as I have visited the king of Assyria.
Saboda haka ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, “Zan hukunta sarkin Babilon da ƙasarsa yadda na hukunta sarkin Assuriya.
19 And I will lead back Israel to his habitation. And he will pasture on Carmel and Bashan, and his soul will be satiated at mount Ephraim and Gilead.
Amma zan komo da Isra’ila zuwa wurin kiwonsa zai kuwa yi kiwo a Karmel da Bashan; zai ƙosar da marmarinsa a tuddan Efraim da Gileyad.
20 In those days and at that time, says the Lord, the iniquity of Israel will be sought, and there will be none. And the sin of Judah will be sought, and none will be found. For I will be forgiving to them, whom I will leave behind.
A kwanakin nan, da kuma a lokacin nan,” in ji Ubangiji, “za a yi bincike don laifin Isra’ila, amma ba za a samu ba, kuma don zunubin Yahuda, amma ba za a sami wani abu ba, gama zan gafarta wa raguwar da na rage.
21 Ascend against the land of the rulers, and visit against its inhabitants! Scatter and destroy whatever has been left behind them, says the Lord, and act according to all that I have instructed you.
“Ku fāɗa wa ƙasar Meratayim da waɗanda suke zama a Fekod. Ku fafara, ku kashe kuma hallaka su sarai,” in ji Ubangiji. “Ku aikata dukan abin da na umarce ku.
22 A voice of war in the land, and great destruction!
Hargowar yaƙi tana a ƙasar, hargowar babbar hallaka!
23 How has the mallet of the entire earth been broken and crushed? How has Babylon been turned into a desert among the nations?
Dubi yadda aka karya aka kuma ragargaza gudumar dukan duniya! Dubi yadda Babilon ta zama kufai a cikin al’ummai!
24 I have ensnared you, and you have been captured, O Babylon, and you did not realize it. You have been discovered and seized, because you provoked the Lord.
Na sa miki tarko, Babilon, kika kuwa kamu kafin ki sani; aka same ki aka kuma kama ki domin kin tayar wa Ubangiji.
25 The Lord has opened his storehouse, and he has brought forth the instruments of his wrath. For there is work for the Lord, the God of hosts, within the land of the Chaldeans.
Ubangiji ya buɗe taskar makamansa ya fitar da makaman fushinsa, gama Maɗaukaki Ubangiji Mai Iko Duka yana da aikin da zai yi a ƙasar Babiloniyawa.
26 Advance against her from the furthest regions! Open, so that those who will trample her may go out! Take stones from the road, and gather them into piles, and destroy her. And let there be nothing left of her.
Ku zo ku yi gāba da ita daga nesa. Ku buɗe rumbunanta; ku jibga ta kamar tsibin hatsi. Ku hallaka ta sarai kada ku bar mata raguwa.
27 Scatter all her strong ones. Let them descend to the slaughter. Woe to them! For their day has arrived, the time of their visitation.
Ku kashe dukan’yan bijimanta bari su gangara zuwa mayanka! Kaitonsu! Gama ranansu ta zo, lokaci ya yi da za a hukunta su.
28 It is the voice of those who are fleeing and of those who have escaped from the land of Babylon: to announce in Zion the revenge of the Lord our God, the revenge of his Temple.
Ku saurari masu gudun hijira da masu neman mafaka daga Babilon suna furtawa a Sihiyona yadda Ubangiji Allahnmu ya ɗauki fansa, fansa domin haikalinsa.
29 Announce it to the many in Babylon, to all who bend the bow. Stand together against her all around, and let no one escape. Repay her according to her work. In accord with all that she has done, do to her. For she has raised herself up against the Lord, against the Holy One of Israel.
“Ku kira’yan baka a kan Babilon, dukan waɗanda suke jan baka. Ku yi sansani kewaye da ita duka; kada ku bar wani ya tsira. Ku sāka mata don ayyukanta; ku yi mata yadda ta yi. Gama ta tayar wa Ubangiji, Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
30 For this reason, her young men will fall in her streets. And all her men of war will be silenced, in that day, says the Lord.
Saboda haka, samarinta za su fāɗi a tituna; za a kawar da dukan sojojinta a wannan rana,” in ji Ubangiji.
31 Behold, I am against you, O proud one, says the Lord, the God of hosts. For your day has arrived, the time of your visitation.
“Ga shi, ina gāba da ke, ya ke mai girman kai,” in ji Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, “gama ranarki ta zo, lokacin da za a hukunta ki.
32 And the proud one will fall and be ruined. And there will be no one who may lift him up. And I will kindle a fire in his cities, and it will devour everything around him.”
Mai ɗaga kai za tă yi tuntuɓe ta kuma fāɗi kuma ba wanda zai taimake ta tă tashi; zan hura wuta a garuruwanta da za tă cinye duk waɗanda suke kewaye da ita.”
33 Thus says the Lord of hosts: “The sons of Israel and the sons of Judah have endured calumny together. All who have seized them are holding them and refusing to release them.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “An danne mutanen Isra’ila, haka ma mutanen Yahuda. Dukan waɗanda suka kama su suna riƙe su kankan, suna kin barinsu su tafi.
34 Their redeemer is strong. The Lord of hosts is his name. He will defend their case in judgment, so that he may terrify the land and disturb the inhabitants of Babylon.
Duk da haka Mai Fansarsu yana da ƙarfi; Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa. Zai kāre muradunsu gabagadi don yă kawo hutu ga ƙasarsu, amma rashin hutu ga waɗanda suke zaune a Babilon.
35 A sword is for the Chaldeans, says the Lord, and for the inhabitants of Babylon, and for her leaders, and for her wise ones.
“Akwai takobi a kan Babiloniyawa!” In ji Ubangiji “a kan waɗanda suke zama a Babilon da kuma a kan fadawanta da masu hikimarta!
36 A sword is for her diviners, who will be fooled. A sword is for her strong ones, who will be afraid.
Akwai takobi a kan annabawan ƙaryanta! Za su zama wawaye. Akwai takobi a kan jarumawanta! Za su cika da tsoro.
37 A sword is for their horses, and for their chariots, and for all the common people who are in her midst. And they will be like women. A sword is for her storehouses, and they will be plundered.
Akwai takobi a kan dawakanta da kekunan yaƙinta da kuma dukan baƙin da suke cikin mayaƙanta! Za su zama mata. Akwai takobi a kan dukiyarta! Za a washe su.
38 A drought is over her waters, and they will be dried up. For it is a land of graven images, and they glory in portents.
Fări a kan ruwanta! Za su bushe ƙaf. Gama ƙasa ce ta gumaka, gumakan da za su haukace da tsoro.
39 Because of this, dragons will live there with the fig fauns, and ostriches will live in it. And it will no longer be inhabited, even in perpetuity, nor will it be raised up, even from generation to generation.
“Saboda haka halittun hamada da kuraye za su zauna a can, a can kuma mujiya za tă zauna. Ba za a ƙara zauna ko a yi zama a cikinta ba daga tsara zuwa tsara.
40 Just as the Lord overthrew Sodom and Gomorrah, and their neighboring towns, says the Lord, no man will live there, and a son of man will not tend it.
Yadda Allah ya tumɓuke Sodom da Gomorra tare da maƙwabtan garuruwansu,” in ji Ubangiji “haka ma ba wanda zai zauna a can; ba wani da zai zauna a cikinta.
41 Behold, a people arrives from the north, and a great nation. And many kings will rise up from the ends of the earth.
“Duba! Ga sojoji suna zuwa daga arewa; babbar al’umma da sarakuna masu yawa suna tahowa daga iyakokin duniya.
42 They will take up the bow and the shield. They are cruel and merciless. Their voice will sound out, like the sea, and they will ride upon horses, like a man prepared for battle against you, O daughter of Babylon.
Suna riƙe da baka da māshi; mugaye ne marasa tausayi. Amonsu ya yi kamar rurin teku yayinda suke hawan dawakansu; suna zuwa kamar mutane a dāgār yaƙi don su fāɗa miki, ya Diyar Babilon.
43 The king of Babylon has heard the report about them, and his hands have been weakened. Anguish has overtaken him, like the pains of a woman giving birth.
Sarkin Babilon ya ji rahotanni game da su, hannunsa kuma ya yi laƙwas. Wahala ta kama shi, zafi kamar na mace mai naƙuda.
44 Behold, he will ascend like a lion from the arrogance of the Jordan to the robust beauty. For I will cause him to rush upon her suddenly. And who will be the elect one, whom I may appoint over her? For who is like me? And who can endure me? And who is that pastor who can withstand my countenance?”
Kamar zaki mai haurawa daga kurmin Urdun zuwa wurin kiwo mai dausayi, zan fafare Babilon daga ƙasan nan da nan. Wane ne zaɓaɓɓen da zan naɗa domin wannan? Wane ne kamar ni da zai kalubalance ni? Kuma wanda makiyayi zai iya tsaya gāba da ni?”
45 Because of this, listen to the counsel of the Lord, which he has conceived in his mind against Babylon, and to his thoughts, which he has devised against the land of the Chaldeans: “Certainly the little ones of the flocks will pull them down, unless their habitation will have been destroyed with them.
Saboda haka, ku ji abin da Ubangiji ya shirya a kan Babilon, abin da ya nufa gāba da ƙasar Babiloniyawa. Za a kwashe ƙananan garkensu a tafi; zai hallaka wurin kiwonsu sarai saboda su.
46 At the voice of the captivity of Babylon, the earth has been moved, and an outcry has been heard among the nations.”
Da jin an ci Babilon da yaƙi sai duniya ta girgiza; za a ji kukanta cikin al’ummai.

< Jeremiah 50 >