< Jeremiah 51 >

1 Thus says the Lord: “Behold, I will raise up, over Babylon and over its inhabitants, who have lifted up their heart against me, something like a pestilent wind.
Ubangiji ya ce, “Ga shi, zan zuga ruhun mai hallakarwa a kan Babilon da mutanen Leb Kamai.
2 And I will send winnowers into Babylon, and they will winnow her, and they will demolish her land. For they will overwhelm her from every side in the day of her affliction.
Zan aika da baƙi zuwa Babilon su casa ta su kuma yi kaca-kaca da ƙasarta; za su yi hamayya da ita a kowane gefe a ranar masifarta.
3 Let him who draws the bow, not draw his bow. And let him who wears armor, not rise up. Do not spare her young men. Destroy her entire military.
Kada ku bar maharbi yă ja bakansa, kada kuma ku bari yă sa kayan yaƙinsa. Kada ku rage samarinta, ku hallaka sojojinta ƙaf.
4 And the slain will fall in the land of the Chaldeans, and the wounded in its regions.
Za su fāɗi matattu a ƙasar Babilon, da munanan raunuka a titunanta.
5 Yet Israel and Judah have not been widowed by their God, the Lord of hosts, though their land has been filled with transgression against the Holy One of Israel.
Gama Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila da Yahuda bai yashe su ba, ko da yake ƙasarsu cike da take da laifi a gaban Mai Tsarki na Isra’ila.
6 Flee from the midst of Babylon! And let each one save his own life. Do not be silent about her iniquity. For it is the time of revenge from the Lord. He himself will repay her, in her turn.
“Ku gudu daga cikin Babilon! Bari kowa yă ceci ransa! Kada a hallaka saboda zunubanta. Gama lokaci ne don ramuwar Ubangiji, zai sāka mata bisa ga alhakinta.
7 Babylon is a gold cup in the hand of the Lord, inebriating the entire earth. The nations have drunk from her wine, and therefore they have staggered.
Babilon ta zama ƙoƙon zinariya a hannun Ubangiji, ta sa dukan duniya ta yi maye. Ƙasashe sun sha ruwan inabinta, saboda haka yanzu sun haukace.
8 Suddenly, Babylon has fallen and been crushed. Wail over her! Take a balm to her pain, if perhaps she may be healed.”
Farat ɗaya Babilon za tă fāɗi ta farfashe. Ku yi kuka dominta! Ku samo mata magani saboda azabarta; wataƙila za a iya warkar da ita.
9 “We would have cured Babylon, but there is no cure. Let us abandon her, and let each one of us go to his own land. For her judgment has reached even to the heavens, and has been lifted up even to the clouds.
“‘Da mun warkar da Babilon, amma ba za tă warke ba; mu ƙyale ta kowane yă koma garinsu, gama hukuncinta ya kai sammai, ya yi tsawo kamar gizagizai.’
10 The Lord has brought forth our justices. Come and let us describe in Zion the work of the Lord our God.”
“‘Ubangiji ya baratar da mu; zo mu tafi mu yi shelarsa a Sihiyona mu faɗa abin da Ubangiji Allahnmu ya yi.’
11 Sharpen the arrows, fill the quivers. The Lord has raised up the spirit of the kings of the Medes. And his mind is against Babylon, so that he may destroy her. For this is the vengeance of the Lord, the vengeance of his temple.
“Ku wasa kibiyoyi, ku ɗauko garkuwoyi! Ubangiji ya zuga sarakunan Medes, domin niyyarsa ce yă hallaka Babilon. Ubangiji zai yi ramuwa, zai yi ramuwa saboda haikalinsa.
12 Upon the walls of Babylon, lift up a sign. Increase the watch! Rouse the watchmen! Prepare ambushes! For the Lord has planned and has accomplished all that he has spoken, against the inhabitants of Babylon.
Ku tā da tuta gāba da katangan Babilon! Ku ƙara matsara, ku kafa masu tsaro, ku shirya kwanto! Ga shi, Ubangiji zai aikata abin da ya faɗa umarninsa a kan mutanen Babilon.
13 You who live above many waters, rich in treasures: your end has arrived, your measure has been cut short.
Ke da kike zama kusa da ruwaye da kike kuma wadatar dukiya, ƙarshenki ya zo, lokaci ya yi da za a kau da ke.
14 The Lord of hosts has sworn by himself, saying: “For I will fill you with men as with locusts, and they will sing a rhythmic chant against you.”
Ubangiji Maɗaukaki ya rantse da zatinsa, ya ce Tabbatacce zan cika ka da mutane kamar fāra, za su kuwa yi sowa don nasara a kanka.
15 The One who made the earth by his strength, who prepared the world by his wisdom, and who stretched out the heavens by his prudence:
“Ya halicci ƙasa ta wurin ikonsa; ya kafa duniya ta wurin hikimarsa, ya kuma shimfiɗa sammai ta wurin fahiminsa.
16 when he utters his voice, the waters will be multiplied in the heavens. The One who lifts up the clouds from the ends of the earth: he has turned lightning into rain, and he has brought forth wind from his storehouses.
Sa’ad da ya yi tsawa ruwan da suke sammai sukan yi ruri; yakan sa gizagizai su tashi daga ƙarshen duniya. Yakan tura walƙiya tare da ruwan sama yakan kuma saki iska daga cikin taskokinsa.
17 Each man has become foolish before his own knowledge. Each sculptor has been confounded by his own sculpture. For what he has formed of them is a lie, and there is no spirit in them.
“Kowane mutum marar azanci ne kuma ba shi da sani; kowane maƙerin zinariya yakan sha kunya daga wurin gumakansa. Siffofinsa na ƙarya ne; babu numfashi a cikinsu.
18 They are empty works, deserving of ridicule. In the time of their visitation, they will perish.
Su marasa amfani ne, abubuwan ba’a ne kawai; sa’ad da lokacin hukuncinsu ya kai, za su hallaka.
19 The portion of Jacob is not like their portion. For the One who made all things is his portion, and Israel is the scepter of his inheritance. The Lord of hosts is his name:
Wanda yake na wajen Yaƙub ba kamar waɗannan ba ne, gama shi ne Mahalicci dukan abu, har da kabilar abin gādonsa, Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa.
20 “For me, you strike together the instruments of war; and with you, I will strike together nations; and with you, I will scatter the kingdoms.
“Kai ne kulkin yaƙina, kayan yaƙina, da kai ne na ragargaza ƙasashe, da kai ne na hallaka mulkoki,
21 And with you, I will strike together the horse and his rider; and with you, I will strike together the chariot and its rider.
da kai ne na ragargaza doki da mahayi, da kai ne na ragargaza keken yaƙin da matuƙi,
22 And with you, I will strike together man and woman; and with you, I will strike together the old man and the boy; and with you, I will strike together the young man and the virgin.
da kai ne na ragargaza miji da mata, da kai ne na ragargaza tsoho da saurayi, da kai ne na ragargaza saurayi da budurwa,
23 And with you, I will strike together the pastor and his flock; and with you, I will strike together the farmer and his yoke of oxen; and with you, I will strike together military leaders and civil leaders.
da kai ne na ragargaza makiyayi da garke, da kai ne na ragargaza manoma da dawakan noma, da kai ne na ragargaza masu mulki da shugabanni.
24 And I will repay Babylon and all the inhabitants of Chaldea for all their evil that they have done in Zion, before your eyes, says the Lord.
“Zan sāka wa Babilon da dukan mazaunan Babilon a idanunku saboda dukan muguntar da suka aikata a Sihiyona,” in ji Ubangiji.
25 Behold, I am against you, you pestilent mountain, says the Lord, for you are corrupting the entire earth. And I will extend my hand over you, and I will roll you down from the rocks, and I will make you into a burning mountain.
“Ga shi, ina gāba da kai, ya ke dutse mai hallakarwa, wadda ta hallaka duniya duka,” in ji Ubangiji. “Zan miƙa hannuna gāba da ke, zan mirgina ƙasa daga ƙwanƙolin dutse, zan maishe ki ƙonannen dutse.
26 And they will not take from you a stone for the corner, nor a stone for the foundations. Instead, you will be destroyed unto eternity,” says the Lord.
Ba za a ɗauki dutsen yin kusurwa daga gare ki ba ko na kafa harsashen gini, gama za ki zama marar amfani har abada,” in ji Ubangiji.
27 Lift up a sign in the land! Sound the trumpet among the nations! Sanctify the nations against her. Announce against her the kings of Ararat, Minni, and Ashkenaz. Number against her Taphsar. Lead in the horse, like the stinging locust.
“Ku tā da tuta a ƙasa! Ku busa ƙahoni a cikin ƙasashe! Ku shirya ƙasashe don yaƙi da ita, ku kira waɗannan mulkokin gāba da ita. Ararat, Minni, da Ashkenaz. A naɗa shugaba gāba da ita; ku shirya dawakai kamar fāra.
28 Sanctify the nations against her: the kings of Media, their military leaders, and all their civil leaders, and the entire land under their authority.
Ku shirya ƙasashe don yaƙi da ita, sarakunan Medes, gwamnoninsu da dukan masu shugabancinsu da kowace ƙasar da take ƙarƙashin mulkinsu.
29 And the earth will be shaken and will be disturbed. For the plan of the Lord against Babylon will awaken, so that he may make the land of Babylon desolate and uninhabitable.
Ƙasa ta girgiza tana makyarkyata saboda nufin Ubangiji na gāba da Babilon ya tabbata, nufinsa na mai da ƙasar Babilon kufai don kada kowa yă zauna a can.
30 The strong ones of Babylon have ceased to do battle. They have lived in fortresses. Their health has been devoured, and they have become like women. Her tabernacles have been set ablaze; her bars have been broken.
Sojojin Babilon sun daina yaƙi, suna zaune a cikin kagaransu. Ƙarfinsu ya ƙare, sun zama mata. An sa wa wuraren zamanta wuta, an karya ƙyamaren ƙofofin garinta.
31 Runner will go forth to meet runner, and messenger will meet messenger, so as to tell the king of Babylon that his city has been captured, from one end to the other,
Maguji yana biye da maguji a guje, jakada yana biye da jakada, don su faɗa wa sarkin Babilon, cewa an ci birninsa a kowane gefe.
32 and that the fords were seized in advance, and that the marshes have been burned with fire, and that the men of war have been set in disarray.
An ƙwace mashigai aka ƙone fadamu da wuta, sojoji kuma suka giggice.”
33 For thus says the Lord of hosts, the God of Israel: “The daughter of Babylon is like a threshing floor. This is the time of her threshing. A little while longer, and the time of her harvest will arrive.”
Ni Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila na ce, “’Yar Babilon kamar daɓen masussuka a lokacin da ake sussuka, ba da daɗewa ba lokacin girbe ta zai zo.”
34 “Nebuchadnezzar, the king of Babylon, has consumed me, has devoured me. He has made me like an empty vessel. He has swallowed me like a dragon. He has filled his belly with my tender ones, and he has cast me out.
“Nebukadnezzar sarkin Babilon ya cinye mu, ya sa muka rikice, ya maishe mu kamar tulun da babu kome a cikinsa. Ya cinye mu kamar yadda dodon ruwa yakan yi ya kuma cika cikinsa da kayan marmarinmu, sa’an nan kuma ya yi amanmu.
35 This iniquity is against me, and so my flesh is upon Babylon,” says the habitation of Zion. “And my blood is upon the inhabitants of Chaldea,” says Jerusalem.
Bari abin da aka yi wa jikinmu yă kasance a bisa Babilon,” in ji mazaunan Sihiyona. “Bari jininmu yă kasance a kan waɗanda suke zama a Babilon,” in ji Urushalima.
36 Because of this, thus says the Lord: “Behold, I will judge your case, and I will avenge your vengeance, and I will make her sea into a desert, and I will dry up her spring.
Saboda haka ga abin da Ubangiji ya ce, “Duba, zan tsaya muku, zan ɗaukar muku fansa, zan sa tekunta kafe in kuma sa maɓulɓulanta su ƙafe.
37 And Babylon will become a tumult, the habitation of dragons, an astonishment, and a hissing, because there is no inhabitant.
Babilon za tă zama tarin juji, wurin zaman diloli, abin ƙyama da abar ba’a, inda ba kowa.
38 They will roar together, like lions, they will shake their manes, like young lions.
Mutanenta duk suna ruri kamar zakoki, suna gurnani kamar’ya’yan zaki.
39 In their heat, I will give them a drink, and I will inebriate them, so that they become drowsy, and sleep an everlasting sleep, and do not rise up, says the Lord.
Amma sa’ad da aka farkar da su, zan yi musu biki in sa su sha su bugu, domin yi sowa da dariya, sa’an nan su shiga barcin da ba za su farka ba,” in ji Ubangiji.
40 I will lead them away, like lambs to the slaughter, and like rams with young goats.
“Zan sauko da su kamar tumaki zuwa mayanka, kamar raguna da bunsurai.
41 How was Sesac captured, and how was the renowned one of all the earth seized? How has Babylon become an astonishment among the nations?
“Yadda za a ci Sheshak, taƙamar duniya duka za tă daina! Babilon za tă zama abar ƙyama a cikin al’ummai!
42 The sea has ascended over Babylon; she has been covered by the multitude of its waves.
Teku zai malalo a kan Babilon, raƙumansa masu hauka za su rufe ta.
43 Her cities have become an astonishment, an uninhabited and desolate land, a land in which no one may live, nor may a son of man pass through it.
Garuruwanta sun zama abin kufai, za tă zama hamada inda ba ruwa, ƙasar da ba mazauna, ba kuma mutumin da zai ratsa ta cikinta.
44 And I will visit against Bel in Babylon, and I will cast from his mouth what he has swallowed. And the nations will no longer flow together before him. For even the wall of Babylon will also fall.
Zan hukunta Bel a Babilon, in sa ya yi aman abin da ya haɗiye. Ƙasashe ba za su ƙara bumbuntowa wurinsa ba. Katangan Babilon kuwa za tă rushe!
45 Go forth from her midst, my people, so that each one may save his life from the wrath of the fury of the Lord.
“Ku fito daga cikinta, jama’ata! Ku tsere da ranku! Ku tsere daga zafin fushin Ubangiji.
46 For otherwise, your heart may faint, and you may be afraid at the news that is heard in the land. And the news will arrive within a year, and after that year more news will arrive. And iniquity will be in the land, and one ruler will be over another ruler.
Kada zuciyarku tă yi suwu ko ku ji tsoro sa’ad da aka ji labarin a ƙasar, labari guda a wannan shekara, wani kuma a ta biye, labarin hargitsi a ƙasar mai mulki ya tasar wa mai mulki.
47 Because of this, behold, the days are approaching, when I will visit against the graven images of Babylon. And her entire land will be confounded, and all her slain will fall in her midst.
Gama kwanaki tabbatacce suna zuwa, sa’ad da zan hukunta gumakan Babilon, zan kunyatar da dukan ƙasar kuma matattunta duk za su kwanta a cikinta.
48 And the heavens and the earth, and all the things that are in them, will give praise over Babylon. For despoilers will approach her from the north, says the Lord.
Sa’an nan sama da ƙasa da dukan abin da yake cikinsu, za su yi sowa ta murna a kan Babilon, gama daga arewa masu hallakarwa su auko mata,” in ji Ubangiji.
49 And in the manner that Babylon has caused the slain to fall in Israel, so the slain of Babylon will fall over the entire earth.
“Babilon za tă fāɗi saboda kisassun mutanen Isra’ila, kamar dai yadda kisassu dukan duniya suka fāɗi saboda Babilon.
50 You who have fled from the sword, approach, do not stand still. Remember from afar the Lord, and let Jerusalem rise up in your heart.
Ku waɗanda kuka tsere wa takobi, ku gudu kada ku tsaya! Ku tuna da Ubangiji a ƙasa mai nesa, ku kuma yi ta tunani a kan Urushalima.”
51 We have been confounded, for we heard reproach. Shame has covered our faces, for strangers have overwhelmed the holiness of the house of the Lord.
“Mun sha kunya saboda zargin da ake yi mana kunya ta rufe mu, domin baƙi sun shiga tsarkakan wurare na gidan Ubangiji.”
52 Because of this, behold, the days are approaching, says the Lord, when I will visit against her graven images, and within all her land the wounded will groan.
“Amma kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan hukunta gumakanta, da kuma a dukan ƙasarta waɗanda aka yi wa rauni, za su yi nishi.
53 If Babylon were to ascend to heaven, and establish her strength on high, her despoilers would go forth from me, says the Lord.”
Ko da Babilon za tă kai sararin sama ne, ta gina kagaranta mai ƙarfi, duk da haka zan aiki masu hallakarwa a kanta,” in ji Ubangiji.
54 A voice of outcry from Babylon, and great destruction from the land of the Chaldeans!
“Ku ji muryar kuka daga Babilon, Da hargowar babbar hallakarwa daga ƙasar Babiloniyawa!
55 For the Lord has despoiled Babylon, and he has perished the great voice from her. And their wave will make a sound like many waters. Their voice has uttered a noise.
Gama Ubangiji zai rushe Babilon, zai sa ta ƙame bakinta na alfarma. Sojoji za su yi ta kutsawa kamar raƙuman ruwa; suna tā da muryoyinsu.
56 For the despoiler has overwhelmed her, that is, Babylon, and her strong ones have been apprehended, and their bow has been weakened. For the Lord, the powerful revenger, will certainly repay.
Gama mai hallakarwa ya auka wa Babilon, a kama sojojinta, a kuma kakkarya bakkunansu. Gama Ubangiji shi Allah ne mai sakayya; zai yi sakayya sosai.
57 “And I will inebriate her leaders, and her wise ones, and her military rulers, and her civil rulers, and her strong ones. And they will sleep an everlasting sleep, and they will not awaken,” says the King: the Lord of hosts is his name.
Zan sa mahukuntanta da masu hikimarta, gwamnoninta, shugabanninta da sojojinta su sha su bugu; za su dinga yin barcin da ba za su farka ba,” in ji Sarkin, mai suna Ubangiji Maɗaukaki.
58 Thus says the Lord of hosts: “That very wide wall of Babylon will be utterly overturned, and her exalted gates will be burned with fire, and the labors of the people will be as nothing, and the labors of the nations will be sent into the fire and will perish.”
Ni Ubangiji Maɗaukaki, na ce, “Za a baje katangan nan na Babilon mai kauri za a kuma ƙone dogayen ƙyamarenta da wuta; mutane sun wahalar da kansu a banza, al’umma sun yi wahala kawai domin wutar lalata.”
59 The word that Jeremiah, the prophet, instructed to Seraiah, the son of Neriah, the son of Mahseiah, when he traveled with king Zedekiah into Babylon, in the fourth year of his reign. Now Seraiah was the leader of the prophets.
Jawabin da annabi Irmiya ya ba Serahiya, ɗan Neriya, wato, jikan Ma’asehiya, lokacin da ya tafi tare da Zedekiya, Sarkin Yahuda, zuwa Babilon a shekara ta huɗu ta mulkinsa. Serahiya shi ne shugaba mai lura da gidajen saukar baƙi.
60 And Jeremiah wrote in one book all the evil that was to overwhelm Babylon; all these words were written against Babylon.
Irmiya ya rubuta a littafi dukan masifun da za su auko wa Babilon, wato, dukan wannan magana da aka rubuta a kan Babilon.
61 And Jeremiah said to Seraiah: “When you will enter into Babylon, and you will see and read all these words,
Irmiya kuwa ya ce wa Serahiya, “Lokacin da ka kai Babilon, sai ka karanta dukan maganan nan.
62 you will say: ‘O Lord, you have spoken against this place so that you may destroy it, so that there would not be anyone, from man even to beast, who may live in it, and so that it may be desolate forever.’
Ka kuma ce, ‘Ya Ubangiji, kai ne ka yi magana a kan wannan wuri, cewa za ka lalatar da shi, har ba abin da zai zauna a ciki, mutum ko dabba. Wurin zai zama kufai har abada.’
63 And when you will have completed reading this book, you will tie a stone to it, and you will cast it into the midst of the Euphrates.
Sa’ad da ka gama karanta wannan littafi, sai ka ɗaura wa littafin dutse, sa’an nan ka jefar da shi tsakiyar Kogin Yuferites.
64 And you will say: ‘So shall Babylon be submerged! And she will not rise up before the face of the affliction that I will lead over her. And she will be broken.’” The words of Jeremiah thus far.
Sa’an nan ka ce, ‘Haka Babilon za tă nutse, ba za tă ƙara tashi ba saboda masifar da zan kawo mata. Mutanenta kuwa za su fāɗi.’” Wannan shi ne ƙarshen kalmomin Irmiya.

< Jeremiah 51 >