< Jeremiah 48 >

1 Against Moab, thus says the Lord of hosts, the God of Israel: “Woe upon Nebo! For it has been devastated and confounded. Kiriathaim has been seized; the strong one has been confounded and has trembled.
Game da Mowab. Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, “Kaito ga Nebo, gama za tă lalace. Kiriyatayim za su kunyata a kuma kame ta; katagar za tă sha kunya ta kuma wargaje.
2 There is no longer any rejoicing in Moab over Heshbon. They have devised evil. ‘Come and let us destroy it as a nation.’ Then you will be utterly silenced, and the sword will pursue you.
Ba za a ƙara yabi Mowab ba; a Heshbon mutane za su shirya mata maƙarƙashiya. ‘Zo, mu tafi mu kawo ƙarshe ga wannan al’umma.’ Ke kuma, ya Madmen za ki yi shiru; takobi zai fafare ki.
3 A voice of clamor from Horonaim: devastation and great destruction!
Saurari kuka daga Horonayim, kukan risɓewa mai girma da hallaka.
4 Moab has been crushed. Announce an outcry for her little ones.
Za a karye Mowab; ƙanananta za su yi kuka.
5 For, along the ascent of Luhith, the mourner will ascend with weeping. For, on the descent of Horonaim, the enemies have heard the wailing of devastation.
Sun haura hanyar zuwa Luhit, suna kuka mai zafi yayinda suke tafiya; a hanyar da ta gangara zuwa Horonayim suna kuka a kan hallakar da aka ji.
6 Flee, save your lives! And you shall be like a saltcedar tree in the desert.
Ku gudu! Ku gudu don tserar da ranku; ku zama kamar kurmi a hamada.
7 For because you have had faith in your fortifications and in your storehouses, you too will be seized. And Chemosh will go into captivity: his priests and his leaders together.
Da yake kun dogara ga ayyukanku da arzikinku, ku ma za a kwashe ku bayi, Kemosh zai tafi bauta, tare da firistocinsa da fadawansa.
8 And the despoiler will overwhelm every city, and not a single city will be saved. And the valleys will perish, and the fields will be destroyed. For the Lord has spoken.
Mai hallakarwa zai aukar wa kowane gari, kuma ba wani garin da zai kuɓuta. Kwari zai lalace tudu kuma ya hallaka, domin Ubangiji ya faɗa.
9 Give a blossom to Moab. For it will depart when it is blossoming. And its cities will become desolate and uninhabited.
Ku sa gishiri a kan Mowab, gama za tă zama kango; garuruwanta za su zama kufai, ba mazauna a cikinsu.
10 Cursed is he who does the work of the Lord deceitfully. And cursed is he who prohibits his sword from blood.
“La’ananne ne shi wanda yake sake a yin aikin Ubangiji! La’ananne ne wanda ya janye takobinsa daga zub da jini!
11 Moab has been fertile from his youth, and he has rested amid his brood. And he has not been transferred from vessel to vessel, nor has he gone into the transmigration. Therefore, his taste has remained with him, and his scent has not changed.
“Mowab ta kasance cikin kwanciyar rai tun ƙuruciyarta, kamar ruwan inabin da aka bari lis, ba a juya daga tulu zuwa wani tulu ba ba tă tafi bauta ba. Saboda haka tana da ɗanɗanonta, kuma ƙanshinta bai canja ba.
12 Because of this, behold, the days are approaching, says the Lord, when I will send to him those who will line up and knock down his bottles, and they will knock him down and empty his vessels, and they will break their bottles against one another.
Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan aika da mutanen da za su tuntsurar da tuluna, su kuma zubar da ita waje. Za su bar tulunan ba kome a ciki su kuma farfashe tulunanta.
13 And Moab will be confounded by Chemosh, just as the house of Israel was shamed by Bethel, in which they had faith.
Sa’an nan Mowab za tă ji kunyar Kemosh, yadda gidan Isra’ila ya ji kunya sa’ad da suka dogara ga Betel.
14 How can you say: ‘We are strong and robust men of battle?’
“Yaya za ku ce, ‘Mu jarumawa ne, mutane masu ƙarfi a yaƙi?’
15 Moab has been devastated, and they have cut down her cities. And her elect young men have descended to slaughter. So says the King, whose name is the Lord of hosts.
Mowab za tă hallaka a kuma kai wa garuruwanta hari; samarinta kyawawa za su gangara cikin mayanka,” in ji Sarki, wanda sunansa Ubangiji Maɗaukaki ne.
16 The passing away of Moab draws near and arrives. Its evil will rush forward with great speed.
“Fāɗuwar Mowab ta yi kusa; bala’inta zai auku nan da nan.
17 Console him, all you who surround him and all you who know his name. Say: ‘How has the strong staff become broken, the glorious staff?’
Yi kuka saboda ita, dukanku mazaunan kewayenta, duk waɗanda suka san shahararta; ku ce, ‘Dubi yadda sandan sarauta mai iko ya karye, dubi yadda sanda mai daraja ya karye!’
18 Descend from your glory, and sit in thirst, O habitation of the daughter of Dibon! For the destroyer of Moab has ascended to you; he has dissipated your fortifications.
“Sauko daga darajarku ku zauna a busasshiyar ƙasa, Ya mazaunan Diyar Dibon, gama shi mai hallaka Mowab zai haura a kanku zai kuma lalace biranenku masu kagarai.
19 Stand in the way, and gaze out, O habitation of Aroer! Question him who is fleeing, and say to him who has escaped: ‘What has happened?’
Ku tsaya a bakin hanya ku duba, ku da kuke zama a Arower. Ku tambayi mutumin da yake gudu da macen da take tserewa, tambaye su, ‘Me ya faru?’
20 Moab has been confounded, because he has been conquered. Wail and cry out! Announce it in Arnon: Moab has been devastated,
An kunyata Mowab, gama ta wargaje. Ku yi kuka ku kuma tā da murya! Ku yi shela kusa da Arnon cewa an hallaka Mowab.
21 and judgment has arrived upon the land of the plains: upon Holon, and upon Jahzah, and upon Mephaath,
Hukunci ya zo wa tudu, zuwa Holon, Yahza da Mefa’at,
22 and upon Dibon, and upon Nebo, and upon the house of Deblathaim,
zuwa Dibon, Nebo da Bet-Dibilatayim,
23 and upon Kiriathaim, and upon the house of Gamul, and upon the house of Meon,
zuwa Kiriyatayim, Bet-Gamul da Bet-Meyon,
24 and upon Kerioth, and upon Bozrah, and upon all the cities of the land of Moab, those far away and those nearby.
zuwa Keriyot da Bozra zuwa dukan garuruwan Mowab, nesa da kusa.
25 The horn of Moab has been cut away, and his arm has been crushed, says the Lord.
An karye ƙahon Mowab; an karye hannunta,” in ji Ubangiji.
26 Inebriate him, for he has lifted himself up against the Lord. And Moab will thrust his hand into his own vomit, and also now he himself will become a derision.
“Ku bugar da ita domin ta tayar wa Ubangiji. Bari Mowab tă yi ta birgima a cikin amanta; bari tă zama abin dariya.
27 For Israel had been a derision to them. It was as if you had discovered him among thieves. Because of your own words, then, which you have spoken against him, you will be led away captive.
Isra’ila ma bai zama abin dariya a gare ki ba? Ba a kama shi cikin ɓarayi, har kaɗa kai na ba’a kike yi a duka sa’ad da kike magana game da shi?
28 Relinquish the cities, and live upon a rock, O inhabitants of Moab, and be like a dove nesting at the mouth of an opening at the summit.
Ku bar garuruwanku ku zauna a cikin duwatsu, ku da kuke zama a Mowab. Ku zama kamar kurciyar da take sheƙarta a bakin kogo.
29 We have listened to the arrogance of Moab; he is very proud: his exaltation, and arrogance, and pride, and the loftiness of his heart.
“Mun ji labarin girman kan Mowab mun ji alfarma girmankanta da kumburinta girmankanta da fariyarta da renin zuciyarta.
30 I myself know, says the Lord, his boasting, and that his ability is not in accord with it, nor is it in accord with what he has been striving to do.
Na san alfarmanta amma a banza ne,” in ji Ubangiji, “kuma taƙamarta ba ya cimma kome.
31 For this reason, I will wail over Moab, and I will cry out to all of Moab, to the men on the brick wall who are lamenting.
Saboda haka zan yi kuka a kan Mowab gama dukan Mowab zan yi kuka, Zan yi gurnani don mutanen Kir Hareset.
32 O vineyard of Sibmah, I will weep for you, with the mourning of Jazer. Your offshoots have crossed over the sea. They have reached even to the sea of Jazer. The despoiler has rushed over your harvest and your vintage.
Zan yi kuka saboda kai, yadda Yazer ya yi kuka Ya kuringar Sibma. Rassanki sun kai har teku; sun kai har tekun Yazer. Mai hallakarwa ya fāɗo a kan’ya’yan itatuwanku da kuma inabinku da suka nuna.
33 Rejoicing and exultation has been taken away from Carmel and from the land of Moab. And I have taken the wine from the winepresses. The treader of grapes will no longer sing the usual rhythmic chant.
Farin ciki da murna su ɓace daga lambunan itatuwa da kuma gonakin Mowab. Na dakatar da malalar ruwan inabi daga wurin matsi; ba wanda zai matse su da ihun farin ciki. Ko da yake akwai sowa sowar ba ta farin ciki ba ce.
34 From the outcry of Heshbon, even to Elealeh and Jahzah, they have uttered their voice; from Zoar, even to Horonaim, like a three year old calf. So too, the waters of Nimrim will be very bad.
“Muryar kukansu na tashi daga Heshbon zuwa Eleyale da Yahaz, daga Zowar har zuwa Horonayim da Eglat Shelishiya, gama har ruwan Nimrim ma sun bushe.
35 And I will take away from Moab, says the Lord, the one who makes offerings in exalted places, and the one who sacrifices to his gods.
A Mowab zan kawo ƙarshen waɗanda suke miƙa hadayu a masujadan kan tudu suna kuma ƙone turare ga allolinsu,” in ji Ubangiji.
36 Because of this, my heart will resound for Moab, like the pipes, and my heart will make a sound like the pipes for the men on the brick wall. For he has done more than he was able, yet still they have perished.
“Saboda haka zuciyata na makoki don Mowab kamar busa; tana makoki kamar busa saboda mutanen Kir Hareset. Arzikin da suka samu ta ƙare.
37 For every head will be bald, and every beard will be shaved. All the hands will be bound together, and there will be haircloth on every back.
An aske kowane kai aka kuma yanke kowane gemu aka kuma sa wa kowane kwankwaso rigar makoki.
38 Over all the rooftops of Moab, and in its streets, everyone will mourn. For I have crushed Moab like a useless vessel, says the Lord.
A kan dukan rufi a Mowab da kuma a dandalin jama’a babu wani abu sai kuka gama na karye Mowab kamar tulun da babu mai so,” in ji Ubangiji.
39 How was it conquered, so that they would wail? How is it that Moab has cast down his neck and been confounded? And Moab will be a derision and an example to everyone around him.”
“Duba yadda aka ragargazar ta ita! Duba yadda suke kuka! Duba yadda Mowab ta juya bayanta da kunya! Mowab ta zama abin ba’a abin tsoro ga dukan waɗanda suke kewaye da ita.”
40 Thus says the Lord: “Behold, he will fly like the eagle, and he will extend his wings to Moab.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ga shi! Gaggafa tana firiya zuwa ƙasa, tana shimfiɗa fikafikanta a kan Mowab.
41 Kerioth has been captured, and the fortifications have been taken. And in that day, the heart of the strong ones of Moab will be like the heart of a woman giving birth.
Za a ci Keriyot a kuma kame kagarai. A wannan rana zukatan jarumawan Mowab za su zama kamar zuciyar macen da take naƙuda.
42 And Moab will cease to be a people. For he has been glorified against the Lord.
Za a hallakar da Mowab a matsayin al’umma domin ta tayar wa Ubangiji.
43 Terror and the pit and the snare will overwhelm you, O inhabitant of Moab, says the Lord.
Razana da rami da tarko suna jiranku, Ya mutanen Mowab,” in ji Ubangiji.
44 Whoever flees from the terror will fall into the pit. And whoever climbs out of the pit will be seized by the snare. For I will lead over Moab the year of their visitation, says the Lord.
“Duk wanda ya gudu daga razana zai fāɗa cikin rami, duk wanda ya haura daga rami zai fāɗa cikin tarko; gama zan kawo wa Mowab shekarar hukuncinta,” in ji Ubangiji.
45 Those fleeing from the snare stood in the shadow of Heshbon. For a fire has gone forth from Heshbon, and a flame from the midst of Sihon, and it will devour the portion of Moab, and the top of the head of the sons of tumult.
“A ƙarƙashin Heshbon masu gudun hijira suna tsaye ba mai taimako, gama wuta ta mutu daga Heshbon, harshen wuta daga tsakiyar Sihon; ta ƙone goshin Mowab, ƙoƙon kai na’yan tayarwa masu surutu.
46 Woe to you, O Moab! You have been ruined, O people of Chemosh! For your sons and your daughters have been taken into captivity.
Kaitonki, ya Mowab! Mutanen Kemosh sun hallaka; an kai’ya’yanki maza daurin talala’ya’yanki mata zaman bauta.
47 But I will convert the captivity of Moab in the last days, says the Lord.” Such are the judgments of Moab thus far.
“Duk da haka zan maido da wadatar Mowab a kwanaki masu zuwa,” in ji Ubangiji. A nan hukuncin Mowab ya ƙare.

< Jeremiah 48 >