< Hosea 14 >

1 Israel, convert to the Lord your God. For you have been ruined by your own iniquity.
Ku dawo, ya Isra’ila, ga Ubangiji Allahnku. Zunubanku ne sun zama sanadin fāɗuwarku!
2 Take these words with you and return to the Lord. And say to him, “Remove all iniquity and accept the good. And we will repay the calves of our lips.
Ku ɗauki magana tare da ku ku komo wurin Ubangiji. Ku ce masa, “Ka gafarta mana dukan zunubanmu ka kuma karɓe mu da alheri, don mu iya yabe ka da leɓunanmu.
3 Assur will not save us; we will not ride on horses. Neither will we say any more, ‘The works of our hands are our gods,’ for those that are in you will have mercy on the orphan.”
Assuriya ba za su iya cece mu ba; ba za mu hau dawakan yaƙi ba. Ba za mu ƙara ce, ‘Allolinmu’ wa abin da hannuwanmu suka yi ba, gama a gare ka ne maraya yakan sami jinƙai.”
4 I will heal their contrition; I will love them spontaneously. For my wrath has been turned away from them.
“Zan gyara ɓatancinsu in kuma ƙaunace su a sake, gama fushina ya juya daga gare su.
5 I will be like the dew; Israel will spring forth like the lily, and his root will spread out like that of the cedars of Lebanon.
Zan zama kamar raɓa ga Isra’ila zai yi fure kamar lili. Kamar al’ul na Lebanon zai sa saiwarsa zuwa ƙasa;
6 His branches will advance, and his glory will be like the olive tree, and his fragrance will be like that of the cedars of Lebanon.
tohonsa za su yi girma. Darajarsa za tă zama kamar itacen zaitun, ƙanshinsa kamar al’ul na Lebanon.
7 They will be converted, sitting in his shadow. They will live on wheat, and they will grow like a vine. His memorial will be like the wine of the cedars of Lebanon.
Mutane za su sāke zauna a inuwarsa. Zai haɓaka kamar ƙwayar hatsi. Zai yi fure kamar kuringa, zai zama sananne kamar ruwan inabi daga Lebanon.
8 Ephraim will say, “What are idols to me anymore?” I will listen to him, and I will set him straight like a healthy spruce tree. Your fruit has been found by me.
Efraim zai ce, me kuma zai haɗa ni da gumaka? Zan amsa masa in kuma lura da shi. Ni kamar koren itacen fir ne; amincinka yana fitowa daga gare ni ne.”
9 Who is wise and will understand this? Who has understanding and will know these things? For the ways of the Lord are straight, and the just will walk in them, but truly, the traitors will fall in them.
Wane ne yake da hikima? Zai gane waɗannan abubuwa. Hanyoyin Ubangiji daidai ne; masu adalci sukan yi tafiya a kansu, amma’yan tawaye sukan yi tuntuɓe a kansu.

< Hosea 14 >