< Hosea 8 >

1 Let there be a trumpet in your throat, like an eagle over the house of the Lord, on behalf of those who have transgressed my covenant and violated my law.
“Ka sa kakaki a leɓunanka! Gaggafa tana a bisan gidan Ubangiji domin mutane sun tā da alkawarina suka kuma tayar wa dokata.
2 They will call on me: “O my God, we, Israel, know you.”
Isra’ila ta yi mini kuka, ‘Ya Allahnmu, mun yarda da kai!’
3 Israel has thrown away goodness; the enemy will overtake him.
Amma Isra’ila sun ƙi abin da yake mai kyau; abokin gāba zai fafare su.
4 They have reigned, but not by me. Leaders have emerged, and I did not recognize them. Their silver and their gold, they have made into idols for themselves, so that they might cross over.
Suna naɗa sarakuna, ba da izinina ba; sun zaɓa shugabanni ba da yardanta ba. Da azurfa da zinariya sun ƙera gumaka wa kansu wanda zai kai zuwa ga hallakarsu.
5 Your calf, Samaria, has been rejected. My fury has been enraged against them. How long will they be incapable of being cleansed?
Ku zubar da gunkin maraƙinku, ya Samariya! Fushina yana ƙuna a kansu. Sai yaushe za su rabu da gumaka?
6 For it is itself also from Israel: a workman made it, and it is not God. For the calf of Samaria will be used for the webs of spiders.
Su daga Isra’ila ne! Wannan maraƙi, mai aikin hannu ne ya yi shi; gunki ne ba Allah ba. Za a farfashe shi kucu-kucu, waccan maraƙin Samariya.
7 For they will sow wind and reap a whirlwind. It does not have a firm stalk; the bud will yield no grain. But if it does yield, strangers will eat it.
“Gama sun shuka iska don haka za su girbe guguwa. Hatsin da yake tsaye ba shi da kai, ba zai yi tsaba ba. Ko da ya yi tsaba ma, baƙi ne za su ci.
8 Israel has been devoured. Now, among the nations, it has become like an unclean vessel.
An haɗiye Isra’ila; yanzu tana cikin al’ummai kamar abin da ba shi da amfani.
9 For they have gone up to Assur, a wild ass alone by himself. Ephraim has given presents to his lovers.
Gama sun haura zuwa Assuriya kamar jakin jejin da yake yawo shi kaɗai. Efraim ya sayar da kansa ga maza.
10 But even when they will have brought the nations together for the sake of money, now I will assemble them. And they will rest for a little while from the burden of the king and the leaders.
Ko da yake sun sayar da kansu a cikin al’ummai, yanzu zan tattara su wuri ɗaya. Za su fara lalacewa a ƙarƙashi danniyar babban sarki.
11 For Ephraim multiplied altars to sin, and sanctuaries have become an offense for him.
“Ko da yake Efraim ya gina bagadai masu yawa don hadayun zunubi, waɗannan sun zama bagade don yin zunubi.
12 I will write to him my intricate laws, which have been treated like strangers.
Na rubuta musu abubuwa masu yawa na dokata, amma suka ɗauke su tamƙar wani baƙon abu ne.
13 They will offer victims, they will immolate flesh and will eat, and the Lord will not accept them. For now he will remember their iniquity, and he will repay their sins: they will be turned back to Egypt.
Suna miƙa hadayun da aka ba ni su kuma ci nama, amma Ubangiji ba ya jin daɗinsu. Yanzu zai tuna da muguntarsu yă kuma hukunta zunubansu. Za su koma Masar.
14 And Israel has forgotten his Maker and has built shrines. And Judah has increased its fortified cities. And I will send fire upon his cities, and it will devour its structures.
Isra’ila ya manta da Mahaliccinsa ya kuma gina fadodi; Yahuda ya gina katanga a yawancin garuruwansa. Amma zan aiko da wuta a bisa biranensu da zai cinye kagaransu.”

< Hosea 8 >