< Hosea 13 >

1 While Ephraim was speaking, a horror entered Israel, and he offended by Baal, and he died.
Sa’ad da Efraim ya yi magana, mutane sun yi rawan jiki; an girmama shi a cikin Isra’ila. Amma sai ya zama mai laifi na yin wa Ba’al sujada, ya kuwa mutu.
2 And now they add that they will be sinning more. And they have made themselves an image cast from their silver, just like the image of idols; but the whole thing has been made by craftsmen. These say to them, “Sacrifice men, you who adore calves.”
Yanzu sai yin zunubi a kai a kai suke; suna yin gumaka wa kansu daga azurfansu, da wayo suna sarrafa siffofi, dukansu aikin masu aikin hannu ne. Ana magana waɗannan mutane cewa, “Suna miƙa hadayar mutum su kuma sumbaci gumakan maruƙa.”
3 For this reason, they will be like the morning clouds, and like the morning dew that passes away, just like the dust that is driven by a whirlwind away from the threshing floor, and like the smoke from a chimney.
Saboda haka za su zama kamar hazon safiya, kamar raɓar safen da yakan kakkaɓe, kamar ƙaiƙayin da ake tankaɗe daga masussuka, kamar hayaƙin da yake fita daga taga.
4 But I am the Lord your God from the land of Egypt, and you will not know God apart from me, and there is no Savior except me.
“Amma ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar. Ba za ku yarda da wani Allah ba sai ni, ba wani Mai Ceto in ban da ni.
5 I knew you in the desert, in the land of solitude.
Na lura da ku a hamada, cikin ƙasar mai ƙunar zafi.
6 According to their pastures, they have been filled up and have been satisfied. And they have lifted up their heart, and they have forgotten me.
Sa’ad da na ciyar da su sun ƙoshi; sa’ad da suka ƙoshi, sai suka fara taƙama; sai suka manta da ni.
7 And I will be to them like a lioness, like a leopard in the way of the Assyrians.
Saboda haka zan hau kansu kamar zaki, zan ɓuya a bakin hanya kamar damisa.
8 I will run to meet them like a bear that has been robbed of her young, and I will split open the middle of their liver. And I will devour them there like a lion; the beast of the field will tear them apart.
Kamar beyar da aka ƙwace mata’ya’yanta, zan fāɗa musu in ɓarke su. Kamar zaki zan cinye su; kamar naman jeji zan yayyage su.
9 Perdition is yours, Israel. Your help is only in me.
“An hallaka ku, ya Isra’ila, domin kun tayar mini, kun tayar wa mai taimakonku.
10 Where is your king? Now, especially, let him save you in all your cities, and from your judges, about whom you said, “Give me kings and princes.”
Ina sarkinku, da zai cece ku? Ina masu mulkinku cikin dukan garuruwanku, waɗanda kuka ce, ‘Ba mu sarki da shugabanni’?
11 I will give you a king in my wrath, and I will take him away in my indignation.
Saboda haka cikin fushina na ba ku sarki, kuma cikin hasalata na ɗauke shi.
12 The iniquity of Ephraim has been bound; his sin has been engulfed.
An yi ajiyar laifin Efraim, aka lissafta zunubansa.
13 The pains of giving birth will reach him. He is an unwise son. For now he will not remain firm during the contrition of his sons.
Naƙuda ta zo masa kamar a mace mai haihuwa, amma shi yaro ne marar hikima; sa’ad da lokaci ya kai, ba ya zuwa inda mahaifa ta buɗe.
14 I will free them from the hand of death; from death I will redeem them. Death, I will be your death. Hell, I will be your deadly wound. Consolation is hidden from my eyes. (Sheol h7585)
“Zan fanshe su daga ikon kabari; zan cece su daga mutuwa. Ina annobanki, ya mutuwa? Ina hallakarka, ya kabari? “Ba zan ji tausayi ba, (Sheol h7585)
15 For he will make a division among brothers. The Lord will bring a burning wind, rising up from the desert, and it will dry up his streams, and it will make his fountain desolate, and he will tear apart every collection of desirable useful things.
ko da ma ya ci gaba cikin’yan’uwansa. Iskar gabas daga Ubangiji za tă zo, tana hurawa daga hamada; maɓulɓularsa za tă kafe rijiyarsa kuma ta bushe. Za a kwashi kaya masu daraja na ɗakin ajiyarsa ganima.
16 Let Samaria perish, because she has urged her God towards bitterness. Let them perish by the sword, let their little ones be thrown down, and let their pregnant women be cut in two.
Dole mutanen Samariya su ɗauki laifinsu, domin sun tayar wa Allahnsu. Za a kashe su da takobi; za a fyaɗa ƙananansu da ƙasa, za a ɓarke matansu masu ciki.”

< Hosea 13 >