< Daniel 1 >

1 In the third year of the reign of Jehoiakim king of Judah, Nebuchadnezzar king of Babylon came to Jerusalem and besieged it.
A Shekara ta uku ta mulki Yehohiyakim sarkin Yahuda, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya zo Urushalima ya kuma yi mata ƙawanya.
2 And the Lord delivered into his hand Jehoiakim the king of Judah and a portion of the vessels of the house of God. And he carried them away into the land of Shinar, to the house of his god, and he brought the vessels into the treasure chamber of his god.
Sai Ubangiji ya bashe Yehohiyakim sarkin Yahuda a hannunsa, tare da waɗansu kayayyakin haikalin Allah. Ya ɗauki waɗannan kayan zuwa cikin haikalin allahnsa a Babilon cikin ma’ajin gidan allahnsa.
3 And the king told Ashpenaz, the chief of the eunuchs, that he should bring in some of the sons of Israel, and some of the offspring of the king and of the sovereigns:
Sa’an nan sarkin ya umarci Ashfenaz, shugaban fadarsa yă kawo waɗansu daga cikin Isra’ilawan da suka fito daga gidan sarauta da kuma na fitattun mutane.
4 young men, in whom there was no blemish, noble in appearance, and accomplished in all wisdom, cautious in knowledge, and well-educated, and who could stand in the palace of the king, so that he might teach them the letters and the language of the Chaldeans.
Matasa maza waɗanda ba su da wata naƙasa kuma kyawawa, hazikai ta kowace hanyar koyo, sanannu, masu saurin fahimtar abu, da kuma waɗanda suka cancanci su yi aiki a fadar sarki. Zai koya musu harshen Babiloniyawa da kuma littattafansu.
5 And the king appointed for them provisions for each day, from his own food and from the wine which he himself drank, so that, after being nourished for three years, they would stand in the sight of the king.
Sarki kuma ya sa a ba su abinci da ruwan inabi kowace rana daga cikin abincin sarki. Za a koyar da su har shekaru uku, bayan haka kuma su shiga yin wa sarki hidima.
6 Now, among those of the sons of Judah, there were Daniel, Hananiah, Mishael, and Azariah.
Daga cikin waɗannan da aka zaɓa akwai waɗansu daga Yahuda, Daniyel, Hananiya, Mishayel da kuma Azariya.
7 And the chief of the eunuchs assigned names to them: to Daniel, Belteshazzar; to Hananiah, Shadrach; to Mishael, Meshach; and to Azariah, Abednego.
Sai sarkin fada ya raɗa musu sababbin sunaye, ga Daniyel ya raɗa masa Belteshazar; ga Hananiya ya raɗa masa Shadrak; ga Mishayel ya raɗa masa Meshak; ga Azariya kuma ya raɗa masa Abednego.
8 But Daniel resolved in his heart that he would not be polluted with the king’s meal, nor with the wine he drank, and he requested of the chief of the eunuchs that he might not be contaminated.
Amma Daniyel ya ƙudura a zuciyarsa ba zai ƙazantar da kansa da abinci da ruwan inabin sarki ba, sai ya tambayi sarkin fada don a ba shi izinin kada yă ƙazantar da kansa ta wannan hanya.
9 And so God gave Daniel grace and mercy in the sight of the leader of the eunuchs.
Sai Allah ya sa sarkin fada ya nuna masa tagomashi ya kuma ƙaunaci Daniyel,
10 And the leader of the eunuchs said to Daniel, “I am afraid of my lord the king, who has appointed food and drink for you, who, if he should see that your faces are leaner than those of the other youths your age, you would condemn my head to the king.”
amma sai sarkin fada ya ce wa Daniyel, “Ina jin tsoron ranka yă daɗe, sarkina wanda ya sa a ba ku abinci da ruwan inabi. Me zai sa yă ga kuna ramewa fiye da sauran samari, tsaranku? Sarki zai sa a fille mini kai saboda ku.”
11 And Daniel said to Malasar, whom the leader of the eunuchs had appointed over Daniel, Hananiah, Mishael, and Azariah,
Sai Daniyel ya ce wa mai gadi wanda sarkin fada ya sa yă kula da Daniyel, Hananiya, Mishayel da Azariya,
12 “I beg you to test us, your servants, for ten days, and let roots be given to us to eat and water to drink,
“Ina roƙonka ka gwada bayinka kwana goma. Kada ka ba mu kome sai kayan lambu mu ci da kuma baƙin ruwa mu sha.
13 and then observe our faces, and the faces of the children who eat the king’s food, and then deal with your servants according to what you see.”
Sa’an nan sai ka dubi fuskokinmu da na sauran samarin da suke ci daga abincin sarki; sa’an nan ka yi da bayinka bisa ga abin da ka gani.”
14 When he had heard these words, he tested them for ten days.
Sai ya amince da haka ya kuma gwada su har kwana goma.
15 But, after ten days, their faces appeared better and fatter than all the children who had eaten from the king’s food.
A ƙarshen kwana goma sai aka ga fuskokinsu suna sheƙi, sun kuma yi ƙiba fiye da samarin da suke cin abinci irin na sarki.
16 Thereafter, Malasar took away their portions and their wine for drinking, and he gave them roots.
Sai mai gadinsu ya janye abinci da ruwan inabi irin na sarki, ya ci gaba da ba su kayan lambu.
17 Yet, to these children, God gave knowledge and instruction in every book, and wisdom, but to Daniel, also the understanding of all visions and dreams.
Ga samarin nan guda huɗu Allah ya ba su sani da ganewar dukan irin littattafai da kuma koyarwa. Daniyel kuma ya iya gane wahayi da kowane irin mafarki.
18 And when the time was completed, after which the king had said that they would be brought in, the chief of the eunuchs brought them in before the sight of Nebuchadnezzar.
A ƙarshen lokacin da sarki ya sa da za a kawo su ciki, sai sarkin fada ya gabatar da su ga Nebukadnezzar.
19 And, when the king conversed with them, there had not been found any so great in all the world as Daniel, Hananiah, Mishael, and Azariah; and so they stood in the sight of the king.
Sarki kuwa ya yi magana da su, sai ya gano cewa babu wani kamar Daniyel, Hananiya, Mishayel da kuma Azariya; don haka sai suka shiga yi wa sarki hidima.
20 And in every concept of wisdom and understanding, about which the king consulted with them, he found them to be ten times better than all the seers and astrologers put together, who were in his entire kingdom.
A dukan al’amuran hikima da na fahimta wanda sarki ya tambaye su, ya tarar sun fi dukan masu sihiri da bokaye waɗanda suke cikin mulkinsa sau goma.
21 And so Daniel remained, even until the first year of king Cyrus.
Daniyel kuwa ya kasance a nan har shekara ta farko ta mulkin sarki Sairus.

< Daniel 1 >