< Genesis 16 >

1 Now Sarai, the wife of Abram, had not conceived children. But, having an Egyptian handmaid named Hagar,
To, Saira, matar Abram, ba tă haifa masa’ya’ya ba. Amma tana da wata baiwa mutuniyar Masar mai suna Hagar,
2 she said to her husband: “Behold, the Lord has closed me, lest I give birth. Enter to my handmaid, so that perhaps I may receive sons of her at least.” And when he agreed to her supplication,
saboda haka sai ta ce wa Abram, “Ubangiji ya hana mini haihuwar’ya’ya. Tafi ka kwana da baiwata; wataƙila in sami iyali ta wurinta.” Abram kuwa ya yarda da abin da Saira ta faɗa.
3 she took Hagar the Egyptian, her handmaid, ten years after they began to live in the land of Canaan, and she gave her to her husband as a wife.
Saboda haka bayan Abram ya yi zama a Kan’ana shekaru goma, Saira matarsa ta ɗauki Hagar baiwarta ta ba wa mijinta tă zama matarsa.
4 And he entered to her. But when she saw that she had conceived, she despised her mistress.
Abram kuwa ya kwana da Hagar, ta kuma yi ciki. Sa’ad da Hagar ta gane tana da ciki, sai ta fara rena uwargijiyarta.
5 And Sarai said to Abram: “You have acted unfairly against me. I gave my handmaid into your bosom, who, when she saw that she had conceived, held me in contempt. May the Lord judge between me and you.”
Sai Saira ta ce wa Abram, “Kai ne da alhakin wahalan nan da nake sha. Na sa baiwata a hannunka, yanzu da ta sani tana da ciki, sai ta fara rena ni. Bari Ubangiji yă shari’anta tsakanina da kai.”
6 Abram responded to her by saying, “Behold, your handmaid is in your hand to treat as it pleases you.” And so, when Sarai afflicted her, she took flight.
Abram ya ce, “Baiwarki tana a hannunki? Ki yi da ita yadda kika ga ya fi kyau.” Sai Saira ta wulaƙanta Hagar; saboda haka ta gudu daga gare ta.
7 And when the Angel of the Lord had found her, near the fountain of water in the wilderness, which is on the way to Shur in the desert,
Mala’ikan Ubangiji ya sami Hagar kusa da maɓulɓula a jeji, ita ce maɓulɓular da take gefen hanya zuwa Shur.
8 he said to her: “Hagar, handmaid of Sarai, where have you come from? And where will you go?” And she answered, “I flee from the face of Sarai, my mistress.”
Ya kuma ce mata, “Hagar, baiwar Saira, daga ina kika fito, kuma ina za ki?” Ta amsa ta ce, “Ina gudu ne daga wurin uwargijiyata Saira.”
9 And the Angel of the Lord said to her, “Return to your mistress, and humble yourself under her hand.”
Sai mala’ikan Ubangiji ya ce mata, “Koma wurin uwargijiyarki Saira, ki yi mata biyayya.”
10 And again he said, “I will multiply your offspring continuously, and they will not be numbered because of their multitude.”
Mala’ikan ya ƙara da cewa, “Zan ƙara zuriyarki har su yi yawan da ba wanda zai iya lasafta su.”
11 But thereafter he said: “Behold, you have conceived, and you will give birth to a son. And you shall call his name Ishmael, because the Lord has heard your affliction.
Mala’ikan Ubangiji ya kuma ce mata, “Ga shi kina da ciki za ki kuwa haifi ɗa. Za ki ba shi suna Ishmayel, gama Ubangiji ya ga wahalarki.
12 He will be a wild man. His hand will be against all, and all hands will be against him. And he will pitch his tents away from the region of all his brothers.”
Zai zama mutum mai halin jakin jeji. Hannunsa zai yi gāba da kowa, hannun kowa kuma zai yi gāba da shi. Zai yi zama gāba ga dukan’yan’uwansa.”
13 Then she called upon the name of the Lord who had spoken to her: “You are the God who has seen me.” For she said, “Certainly, here I have seen the back of the one who sees me.”
Sai ta ba wa Ubangiji wanda ya yi magana da ita, wannan suna. “Kai Allah ne wanda yake ganina,” gama ta ce, “Yanzu na ga wanda yake ganina.”
14 Because of this, she called that well: ‘The well of the one who lives and who sees me.’ The same is between Kadesh and Bered.
Shi ya sa ake kira rijiyar Beyer-Lahai-Royi tana nan har yanzu, tsakanin Kadesh da Bered.
15 And Hagar gave birth to a son for Abram, who called his name Ishmael.
Haka fa Hagar ta haifa wa Abram ɗa, Abram kuwa ya ba da suna Ishmayel ga ɗan da ta haifa.
16 Abram was eighty-six years old when Hagar gave birth to Ishmael for him.
Abram yana da shekaru 86 sa’ad da Hagar ta haifa masa Ishmayel.

< Genesis 16 >