< Genesis 12 >

1 Then the Lord said to Abram: “Depart from your land, and from your kindred, and from your father’s house, and come into the land that I will show you.
Ubangiji ya ce wa Abram, “Tashi ka bar ƙasarka, da mutanenka, da iyalin mahaifinka, ka tafi ƙasar da zan nuna maka.
2 And I will make of you a great nation, and I will bless you and magnify your name, and you will be blessed.
“Zan mai da kai al’umma mai girma, zan kuma albarkace ka; zan sa sunanka yă zama mai girma, ka kuma zama sanadin albarka.
3 I will bless those who bless you, and curse those who curse you, and in you all the families of the earth will be blessed.”
Zan albarkaci duk wanda ya albarkace ka, in kuma la’anci duk wanda ya la’anta ka, dukan mutanen duniya za su sami albarka ta wurinka.”
4 And so Abram departed just as the Lord had instructed him, and Lot went with him. Abram was seventy-five years old when he departed from Haran.
Saboda haka Abram ya tashi yadda Ubangiji ya faɗa masa; Lot ma ya tafi tare da shi. Abram yana da shekaru 75, sa’ad da ya tashi daga Haran.
5 And he took his wife Sarai, and Lot, the son of his brother, and all the substance which they had come to possess, and the lives which they had acquired in Haran, and they departed in order to go to the land of Canaan. And when they arrived in it,
Abram ya ɗauki matarsa Saira da Lot ɗan ɗan’uwansa, da dukan mallakar da suka tattara, da kuma mutanen da suka samu a Haran, suka kama hanya zuwa ƙasar Kan’ana.
6 Abram passed through the land even to the place of Shechem, as far as the famous steep valley. Now at that time, the Canaanite was in the land.
Abram ya ratsa ƙasar har zuwa wurin babban itace na More a Shekem. A lokacin Kan’aniyawa suna a ƙasar.
7 Then the Lord appeared to Abram, and he said to him, “To your offspring, I will give this land.” And there he built an altar to the Lord, who had appeared to him.
Ubangiji ya bayyana ga Abram ya ce, “Ga zuriyarka ne zan ba da wannan ƙasa.” Saboda haka Abram ya gina bagade a can ga Ubangiji, wanda ya bayyana gare shi.
8 And passing on from there to a mountain, which was opposite the east of Bethel, he pitched his tent there, having Bethel to the west, and Hai on the east. He also built an altar there to the Lord, and he called upon his name.
Daga can, ya ci gaba zuwa wajen tuddai a gabashin Betel ya kafa tentinsa, Betel yana yamma, Ai, kuma a gabas. A can ya gina bagade ga Ubangiji ya kuma kira bisa sunan Ubangiji.
9 And Abram traveled, going out and continuing further on, toward the south.
Sa’an nan Abram ya tashi ya ci gaba da tafiya zuwa wajen Negeb.
10 But a famine occurred in the land. And Abram descended to Egypt, to sojourn there. For famine prevailed over the land.
To, a lokacin, an yi yunwa a ƙasar, sai Abram ya gangara zuwa Masar don yă zauna a can na ɗan lokaci, domin yunwa ta yi tsanani.
11 And when he was close to entering Egypt, he said to his wife Sarai: “I know you to be a beautiful woman.
Yayinda yana gab da shiga Masar, sai ya ce wa matarsa Saira, “Na sani ke kyakkyawar mace ce.
12 And when the Egyptians see you, they will say, ‘She is his wife.’ And they will put me to death, and retain you.
Sa’ad da Masarawa suka ganki, za su ce, ‘Wannan matarsa ce.’ Za su kuwa kashe ni, su bar ki da rai.
13 Therefore, I beg you to say that you are my sister, so that it may be well with me because of you, and so that my soul may live by your favor.”
Saboda haka ki ce ke’yar’uwata ce, domin ta dalilinki a mutunta ni, a kuma bar ni da rai.”
14 And so, when Abram had arrived in Egypt, the Egyptians saw that the woman was exceedingly beautiful.
Sa’ad da Abram ya isa Masar, Masarawa suka ga cewa Saira kyakkyawa mace ce ƙwarai.
15 And the princes reported it to Pharaoh, and they praised her to him. And the woman was inducted into the house of Pharaoh.
Sa’ad da fadawan Fir’auna suka gan ta kuwa, sai suka yabe ta wajen Fir’auna, aka kuwa kawo ta cikin fadarsa.
16 In truth, they treated Abram well because of her. And he had sheep and oxen and male donkeys, and men servants, and women servants, and female donkeys, and camels.
Ya mutunta Abram sosai saboda ita, Abram kuwa ya mallaki tumaki da shanu, da jakuna maza da mata, da bayi maza da mata, da kuma raƙuma.
17 But the Lord scourged Pharaoh and his house with great wounds because of Sarai, the wife of Abram.
Amma Ubangiji ya wahalar da Fir’auna da gidansa da cututtuka masu zafi saboda Saira, matar Abram.
18 And Pharaoh called Abram, and he said to him: “What is this that you have done to me? Why did you not tell me she was your wife?
Saboda haka Fir’auna ya kira Abram ya ce, “Me ke nan ka yi mini? Me ya sa ba ka faɗa mini cewa ita matarka ce ba?
19 For what reason did you claim her to be your sister, so that I would take her to me as a wife? Now therefore, behold your mate, receive her and go.”
Don me ka ruɗe ni cewa, ‘Ita’yar’uwata ce,’ har na ɗauke ta tă zama matata? To, ga matarka. Ɗauke ta ka tafi.”
20 And Pharaoh instructed his men about Abram. And they led him away with his wife and all that he had.
Sa’an nan Fir’auna ya yi wa mutanensa umarni a kan Abram, suka kuwa sallame shi tare da matarsa da kuma dukan abin da yake da shi.

< Genesis 12 >