< Genesis 18 >

1 Then the Lord appeared to him, in the steep valley of Mamre, when he was sitting at the door of his tent, in the very heat of the day.
Ubangiji ya bayyana ga Ibrahim kusa da manyan itatuwan Mamre yayinda yake zaune a mashigin tentinsa da tsakar rana.
2 And when he had lifted up his eyes, there appeared to him three men, standing near him. When he had seen them, he ran to meet them from the door of his tent, and he reverenced them on the ground.
Da Ibrahim ya ɗaga ido, sai ya ga mutum uku suna tsaye kusa da shi. Sa’ad da ya gan su, sai ya tashi nan da nan daga mashigin tentinsa, ya tarye su, ya rusuna har ƙasa.
3 And he said: “If I, O lord, have found grace in your eyes, do not pass by your servant.
Ya ce, “Ranka yă daɗe, in na sami tagomashi daga gare ku kada ku wuce bawanku.
4 But I will bring a little water, and you may wash your feet and rest under the tree.
Bari a kawo ruwa ku wanke ƙafafunku, ku huta a ƙarƙashin wannan itace.
5 And I will set out a meal of bread, so that you may strengthen your heart; after this you will pass on. It is for this reason that you have turned aside to your servant.” And they said, “Do as you have spoken.”
Bari in samo muku wani abu ku ci don ku wartsake, sa’an nan ku ci gaba da tafiyarku; da yake kun biyo wurin bawanku.” Suka ce, “To, sai ka yi abin da ka ce.”
6 Abraham hurried into the tent to Sarah, and he said to her, “Quickly, mix together three measures of the finest wheat flour and make loaves baked under the ashes.”
Saboda haka Ibrahim ya ruga zuwa wurin Saratu a cikin tenti ya ce, “Yi sauri, ki shirya mudu uku na gari mai laushi, ki cuɗa shi, ki yi burodi.”
7 In truth, he himself ran to the herd, and he took a calf from there, very tender and very good, and he gave it to a servant, who hurried and boiled it.
Sa’an nan Ibrahim ya yi gudu zuwa garkensa, ya zaɓi ɗan maraƙi ya ba wa bawansa, bawansa kuma ya yi sauri ya gyara shi.
8 Likewise, he took butter and milk, and the calf which he had boiled, and he placed it before them. Yet truly, he himself stood near them under the tree.
Sa’an nan Ibrahim ya ɗauko dambu da madara da naman ɗan maraƙin da aka gyara, ya kawo a gabansu. Yayinda suke ci, ya tsaya a gindin itace kusa da su.
9 And when they had eaten, they said to him, “Where is Sarah your wife?” He answered, “Behold, she is in the tent.”
Sai suka ce masa, “Ina Saratu matarka?” Ibrahim ya ce, “Tana can cikin tenti.”
10 And he said to him, “When returning, I will come to you at this time, with life as a companion, and your wife Sarah will have a son.” Hearing this, Sarah laughed behind the door of the tent.
Sa’an nan ɗayansu ya ce, “Lalle zan komo wurinka war haka shekara mai zuwa. Saratu matarka kuwa za tă haifi ɗa.” Saratu kuwa tana a bayansu tana ji daga mashigin tenti.
11 Now they were both old, and in an advanced state of life, and it had ceased to be with Sarah after the manner of women.
Ibrahim da Saratu dai sun riga sun tsufa sosai. Saratu kuma ta wuce shekarun haihuwa.
12 And she laughed secretly, saying, “After I have grown old, and my lord is elderly, shall I give myself to the work of delight?”
Saboda haka Saratu ta yi dariya da ta yi tunani a zuci tana cewa, “Bayan ƙarfina ya ƙare, maigidana kuma ya tsufa, yanzu zan sami wannan jin daɗi?”
13 Then the Lord said to Abraham: “Why did Sarah laugh, saying: ‘How can I, an old woman, actually give birth?’
Sai Ubangiji ya ce wa Ibrahim, “Me ya ba Saratu dariya har da ta ce, ‘Har zan iya haifi ɗa duk ta tsufata yanzu?’
14 Is anything difficult for God? According to the announcement, he will return to you at this same time, with life as a companion, and Sarah will have a son.”
Akwai abin zai gagari Ubangiji? Zan komo wurinka a ƙayyadadden lokacin nan shekara mai zuwa kuma Saratu za tă haifi ɗa.”
15 Sarah denied it, saying, “I did not laugh.” For she was terribly afraid. But the Lord said, “It is not so; for you did laugh.”
Saratu ta ji tsoro, don haka sai ta yi ƙarya ta ce, “Ban yi dariya ba.” Ya ce, “A’a, kin yi dariya.”
16 Therefore, when the men had risen up from there, they directed their eyes against Sodom. And Abraham traveled with them, leading them.
Sai mutanen suka tashi suka nufi Sodom, Ibrahim kuwa ya yi musu rakiya, ya yi bankwana da su.
17 And the Lord said: “How could I hide what I am about to do from Abraham,
Sai Ubangiji ya ce, “Zan ɓoye wa Ibrahim abin da nake shirin yi?
18 since he will become a great and very robust nation, and in him all the nations of the earth will be blessed?
Lalle Ibrahim zai zama al’umma mai girma da kuma mai iko, kuma ta wurinsa dukan al’umman duniya za su sami albarka.
19 For I know that he will instruct his sons, and his household after him, to keep to the way of the Lord, and to act with judgment and justice, so that, for the sake of Abraham, the Lord may bring about all the things that he has spoken to him.”
Saboda na zaɓe shi don yă umarci’ya’yansa da iyalinsa a bayansa su kiyaye hanyoyin Ubangiji, ta wurin yin abin da yake daidai da kuma yin adalci, domin Ubangiji ya aikata abin da ya yi wa Ibrahim alkawari.”
20 And so the Lord said, “The outcry from Sodom and Gomorrah has been multiplied, and their sin has become exceedingly grievous.
Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Kuka a kan Sodom da Gomorra ta yi yawa, zunubinsu kuma ya yi muni sosai,
21 I will descend and see whether they have fulfilled the work of the outcry that has reached me, or whether it is not so, in order that I may know.”
zan gangara in ga ko abin da suka yi ya yi muni kamar yadda kukan ya zo gare ni, zan bincike.”
22 And they turned themselves from there, and they went toward Sodom. Yet in truth, Abraham still stood in the sight of the Lord.
Sai mutanen suka juya suka nufi wajen Sodom amma Ibrahim ya ci gaba da kasance a gaban Ubangiji.
23 And as they drew near, he said: “Will you destroy the just with the impious?
Sai Ibrahim ya matso wurinsa ya ce, “Za ka hallaka masu adalci tare da masu mugunta?
24 If there were fifty of the just in the city, will they perish with the rest? And will you not spare that place for the sake of fifty of the just, if they were in it?
Me zai faru in akwai mutum hamshin masu adalci a cikin birnin? Ashe, za ka hallaka shi, ba za ka cece wurin saboda mutane hamsin nan masu adalcin da suke a cikinsa ba?
25 Far be it from you to do this thing, and to kill the just with the impious, and for the just to be treated like the impious. No, this is not like you. You judge all the earth; you would never make such a judgment.”
Tabbatacce ba za ka taɓa aikata irin wannan abu ba, ka kashe masu adalci tare da masu mugunta, ka ɗauka masu adalci da masu mugunta daidai? Tabbatacce ba za ka taɓa aikata irin wannan abu ba! Mai hukuncin dukan duniya ba zai aikata gaskiya ba?”
26 And the Lord said to him, “If I find in Sodom fifty of the just in the midst of the city, I will release the entire place because of them.”
Ubangiji ce, “In na sami mutum hamshin masu adalci a cikin birnin Sodom, zan bar dukan birnin saboda su.”
27 And Abraham responded by saying: “Since now I have begun, I will speak to my Lord, though I am dust and ashes.
Sai Ibrahim ya ƙara cewa, “Yanzu da na yi karambani har na yi magana da Ubangiji, ko da yake ni ba kome ba ne illa turɓaya da toka,
28 What if there were five less than fifty of the just? Would you, despite the forty-five, eliminate the entire city?” And he said, “I will not eliminate it, if I find forty-five there.”
in yawan masu adalci sun kāsa hamshin da mutum biyar fa? Za ka hallaka dukan birnin saboda rashin mutum biyar ɗin?” Ya ce, “In na sami mutum arba’in da biyar a wurin, ba zan hallaka shi ba.”
29 And again he said to him, “But if forty were found there, what would you do?” He said, “I will not strike, for the sake of the forty.”
Ya sāke cewa, “In mutum arba’in kaɗai aka samu a can fa?” Ya ce, “Saboda mutum arba’in ɗin, ba zan aikata ba.”
30 “I ask you,” he said, “not to be angry, Lord, if I speak. What if thirty were found there?” He responded, “I will not act, if I find thirty there.”
Sai ya ce, “Kada Ubangiji ya yi fushi, amma bari in ƙara magana. A ce mutum talatin kaɗai aka samu a can fa?” Ya ce, “Ba zan aikata ba, in na sami mutum talatin a can.”
31 “Since now I have begun,” he said, “I will speak to my Lord. What if twenty were found there?” He said, “I will not put to death, for the sake of the twenty.”
Ibrahim ya ce, “Yanzu fa da na yi karambani har na yi magana da Ubangiji, in ashirin kaɗai aka samu a can fa?” Ya ce, “Saboda ashirin ɗin, ba zan hallaka shi ba.”
32 “I beg you,” he said, “not to be angry, Lord, if I speak yet once more. What if ten were found there?” And he said, “I will not destroy it for the sake of the ten.”
Sa’an nan Ibrahim ya ce, “Kada Ubangiji yă yi fushi, amma bari in ƙara magana sau ɗaya tak. In aka sami mutum goma kaɗai a can fa?” Ubangiji ya ce, “Saboda goma nan, ba zan hallaka shi ba.”
33 And the Lord departed, after he had ceased speaking to Abraham, who then returned to his place.
Sa’ad da Ubangiji ya gama magana da Ibrahim, ya tafi, Ibrahim kuma ya koma gida.

< Genesis 18 >