< Genesis 15 >

1 And so, these things having been transacted, the word of the Lord came to Abram by a vision, saying: “Do not be afraid, Abram, I am your protector, and your reward is exceedingly great.”
Bayan wannan, maganar Ubangiji ta zo wa Abram cikin mafarki cewa, “Kada ka ji tsoro, Abram. Ni ne garkuwarka, kuma ladanka zai zama mai girma.”
2 And Abram said: “Lord God, what will you give to me? I may go without children. And the son of the steward of my house is this Eliezer of Damascus.”
Amma Abram ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, mene ne za ka ba ni, ganin cewa ba na haihuwa, wanda kuma zai gāji gādon gidana shi ne Eliyezer mutumin Damaskus?”
3 And Abram added: “Yet to me you have not given offspring. And behold, my servant born in my house will be my heir.”
Abram ya kuma ce, “Ga shi ba ka ba ni ɗa ba, don haka bawan da aka haifa a gidana ne zai zama magājina.”
4 And immediately the word of the Lord came to him, saying: “This one will not be your heir. But he who will come from your loins, the same will you have for your heir.”
Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo gare shi cewa, “Wannan mutum ba zai zama magājinka ba, ɗa da yake zuwa daga jikinka ne zai zama magājinka.”
5 And he brought him outside, and he said to him, “Take in the heavens, and number the stars, if you can.” And he said to him, “So also will your offspring be.”
Sai Ubangiji ya fito da kai shi waje ya ce, “Ka dubi sammai ka kuma ƙirga taurari, in har za ka iya ƙirga su.” Sa’an nan ya ce masa, “Haka zuriyarka za tă zama.”
6 Abram believed God, and it was reputed to him unto justice.
Abram ya gaskata, Ubangiji kuma ya lasafta shi adalci ga Abram.
7 And he said to him, “I am the Lord who led you away from Ur of the Chaldeans, so as to give you this land, and so that you would possess it.”
Ubangiji ya kuma ce wa Abram, “Ni ne Ubangiji wanda ya fitar da kai daga Ur na Kaldiyawa, domin in ba ka wannan ƙasa ka mallake ta.”
8 But he said, “Lord God, in what way may I be able to know that I will possess it?”
Amma Abram ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, yaya zan san cewa zan mallake ta?”
9 And the Lord responded by saying: “Take for me a cow of three years, and a she-goat of three years, and a ram of three years, also a turtle-dove and a pigeon.”
Saboda haka Allah ya ce masa, “Kawo mini karsana, akuya, da kuma rago kowanne yă kasance shi shekara uku ne, da kurciya da kuma ɗan tattabara.”
10 Taking all these, he divided them through the middle, and placed both parts opposite one another. But the birds he did not divide.
Abram ya kawo waɗannan duka a gaban Allah, ya raba kowannensu a tsakiya, ya ajiye su gab da juna, amma bai tsaga tsuntsayen a tsaka ba.
11 And birds descended upon the carcasses, but Abram drove them away.
Sai tsuntsaye masu cin nama suka sauko a kan gawawwakin, amma Abram ya kore su.
12 And when the sun was setting, a deep sleep fell upon Abram, and a dread, great and dark, invaded him.
Yayinda rana tana fāɗuwa, sai Abram ya yi barci mai zurfi, sai wani duhu mai kauri mai kuma bantsoro ya rufe shi.
13 And it was said to him: “Know beforehand that your future offspring will be sojourners in a land not their own, and they will subjugate them in servitude and afflict them for four hundred years.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Abram, “Ka sani tabbatacce cewa shekaru ɗari huɗu, zuriyarka za tă zama baƙi a ƙasar da ba tasu ba, za a mai da su bayi, a kuma wulaƙanta su.
14 Yet truly, I will judge the nation that they will serve, and after this they will depart with great substance.
Amma zan hukunta al’ummar da suka yi bauta kamar bayi, daga baya kuma za su fita da mallaka mai yawa.
15 But you will go to your fathers in peace and be buried at a good old age.
Amma kai za ka koma wurin kakanninka cikin salama a kuma binne ka da kyakkyawan tsufa.
16 But in the fourth generation, they will return here. For the iniquities of the Amorites are not yet completed, even to this present time.”
A tsara ta huɗu zuriyarka za tă komo nan, saboda zunubin Amoriyawa bai riga ya cika ba.”
17 Then, when the sun had set, there came a dark mist, and there appeared a smoking furnace and a lamp of fire passing between those divisions.
Sa’ad da rana ta fāɗi, aka kuwa yi duhu, sai wata tukunya mai hayaƙi, mai harshen wuta mai ci, ta bayyana, ta kuma wuce tsakanin abubuwan nan da aka tsaga.
18 On that day, God formed a covenant with Abram, saying: “To your offspring I will give this land, from the river of Egypt, even to the great river Euphrates:
A wannan rana, Ubangiji ya yi alkawari da Abram ya ce, “Ga zuriyarka na ba da wannan ƙasa, daga kogin Masar zuwa babban kogi, Yuferites ke nan,
19 the land of the Kenites and the Kenizzites, the Kadmonites
ƙasar Keniyawa, Kenizziyawa, Kadmoniyawa,
20 and the Hittites, and the Perizzites, likewise the Rephaim,
Hittiyawa, Ferizziyawa, Refahiyawa,
21 and the Amorites, and the Canaanites, and the Girgashites, and the Jebusites.”
Amoriyawa, Kan’aniyawa, Girgashiyawa da kuma Yebusiyawa.”

< Genesis 15 >