< Exodus 8 >

1 The Lord also said to Moses: “Enter to Pharaoh, and you will say to him: ‘Thus says the Lord: Release my people in order to sacrifice to me.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka je wurin Fir’auna, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka bar mutanena su tafi domin su yi mini sujada.
2 But if you are not willing to release them, behold, I will strike all your coasts with frogs.
In ka ƙi barinsu, zan hore ka da annoban kwaɗi a dukan ƙasarka.
3 And the river will seethe with frogs, which will go up and enter into your house, and your bedroom, and upon your bed, and into the houses of your servants and your people, and into your ovens, and into the remains of your foods.
Nilu zai cika da kwaɗi. Za su haura zuwa cikin fadanka da kan gadonka, cikin gidajen bayinka da kan mutanenka, cikin kwanonin toye-toyenka da na cin abincinka.
4 And to you, and to your people, and to all your servants, the frogs will enter.’”
Kwaɗin nan za su yi ta tsalle a kanka, da kan mutanenka, da kuma kan dukan bayinka.’”
5 And the Lord said to Moses: “Say to Aaron: ‘Extend your hand over the rivers, and also over the streams and the marshes, and bring forth frogs over the land of Egypt.’”
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ce wa Haruna, ‘Ka miƙa hannunka da sandanka bisa koguna da rafuffuka da kuma kududdufai, ka sa kwaɗi su fito su mamaye ƙasar Masar.’”
6 And Aaron extended his hand over the waters of Egypt, and the frogs came up and covered the land of Egypt.
Sai Haruna ya miƙa hannunsa bisa ruwan Masar, kwaɗi kuwa suka fito, suka mamaye ƙasar Masar.
7 Then the sorcerers also, by their incantations, did similarly, and they brought forth frogs upon the land of Egypt.
Amma bokaye ma suka yi abubuwan nan ta wurin sihirinsu; suka sa kwaɗi suka fito suka mamaye ƙasar Masar.
8 But Pharaoh called Moses and Aaron, and he said to them: “Pray to the Lord, so as to take away the frogs from me and from my people. And I will release the people, so as to sacrifice to the Lord.”
Fir’auna ya kira Musa da Haruna ya ce, “Yi addu’a ga Ubangiji yă ɗauke kwaɗi daga gare ni da mutanena, zan kuwa bar mutanenku su tafi su yi hadaya ga Ubangiji.”
9 And Moses said to Pharaoh: “Appoint for me a time, when I should petition on behalf of you, and your servants, and your people, so that the frogs may be driven away from you, and from your house, and from your servants, and from your people, and so that they may remain only in the river.”
Musa ya ce wa Fir’auna, “Na ba ka dama ka ba da lokacin da zan yi addu’a dominka da kuma bayinka da mutanenka, gidajenku kuwa za su rabu da kwaɗi, amma ban da waɗanda suke cikin Nilu.”
10 And he responded, “Tomorrow.” Then he said, “I will act according to your word, so that you may know that there is no one like the Lord our God.
Fir’auna ya ce, “Gobe.” Musa ya amsa, “Za a yi kamar yadda ka faɗa, domin ka sani babu wani kamar Ubangiji, Allahnmu.
11 And the frogs will withdraw from you, and from your house, and from your servants, and from your people. And they will remain only in the river.”
Kwaɗin za su bar ka da gidajenka, bayinka da mutanenka; za su kasance a Nilu ne kaɗai.”
12 And Moses and Aaron departed from Pharaoh. And Moses cried out to the Lord on behalf of the promise that he had made to Pharaoh concerning the frogs.
Bayan Musa da Haruna sun bar Fir’auna, Sai Musa ya yi kuka ga Ubangiji saboda kwaɗin da ya kawo a bisa Fir’auna.
13 And the Lord acted according to the word of Moses. And the frogs died out of the houses, and out of the villages, and out of the fields.
Sai Ubangiji ya yi abin da Musa ya nema. Kwaɗin suka mutu a gidaje, da filaye, da kuma gonaki.
14 And they gathered them together into immense piles, and the land was polluted.
Aka jibga su tsibi-tsibi, ƙasar ta yi ɗoyi saboda su.
15 Then Pharaoh, seeing that relief had been provided, hardened his own heart, and he did not listen to them, just as the Lord had instructed.
Amma da Fir’auna ya ga an sami sauƙi, sai ya taurare, ya ƙi yă saurari Musa da Haruna kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
16 And the Lord said to Moses: “Say to Aaron: ‘Extend your staff and strike the dust of the earth. And let there be stinging insects throughout the entire the land of Egypt.’”
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ce wa Haruna, ‘Miƙa hannunka ka bugi ƙurar ƙasa,’ dukan ƙurar ƙasar Masar kuwa za tă zama ƙwari masu cizo.”
17 And they did so. And Aaron extended his hand, holding the staff, and he struck the dust of the earth, and there came stinging insects upon men and upon beasts. All the dust of the earth was turned into stinging insects through all the land of Egypt.
Suka yi haka, da Haruna ya miƙa hannunsa da sandan, ya bugi ƙurar ƙasa, sai ƙwari masu cizo suka fito a kan mutane da dabbobi. Dukan ƙurar, ko’ina a ƙasar Masar ta zama cinnaku.
18 And the sorcerers, with their incantations, did similarly, in order to bring forth stinging insects, but they were not able. And there were stinging insects, as much on men as on beasts.
Sa’ad da bokayen Fir’auna suka yi ƙoƙari yin sihiri iri na rufe ido domin su fito da kwari, sai suka kāsa. Ƙwari masu cizo kuwa suka rufe mutane da dabbobi.
19 And the sorcerers said to Pharaoh: “This is the finger of God.” And the heart of Pharaoh was hardened, and he did not listen to them, just as the Lord had instructed.
Sai bokaye suka ce wa Fir’auna, “Wannan fa da hannun Allah a ciki.” Amma zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa saurara ba, kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
20 The Lord also said to Moses: “Arise at first light, and stand in the sight of Pharaoh, for he will go out to the waters. And you will say to him: ‘Thus says the Lord: Release my people to sacrifice to me.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka tashi da sassafe ka sadu da Fir’auna a lokacin da za shi kogi, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, bari mutanena su tafi, don su yi mini sujada.
21 But if you will not release them, behold, I will send upon you, and upon your servants, and upon your people, and into your houses, diverse kinds of flies. And the houses of the Egyptians will be filled with diverse kinds of flies, as well as the whole land in which they will be.
In ba ka bar mutanena suka tafi ba, zan turo da tarin ƙuda a kanka da bayinka, a kan mutanenka da cikin gidajenka. Gidajen Masarawa za su cika da ƙudaje, har ma da ƙasa inda za su taka.
22 And in that day, I will cause a miracle in the land of Goshen, where my people are, so that flies will not be there. And you will know that I am the Lord in the midst of the earth.
“‘Amma zan keɓe yankin Goshen, inda mutanena suke don kada ƙudaje su taɓa wurin, domin ka sani cewa Ni, Ubangiji, ina cikin wannan ƙasa.
23 And I will set a division between my people and your people. Tomorrow this sign will be.’”
Zan sa iyaka tsakanin jama’ata da jama’arka. Gobe ne wannan mu’ujiza za tă auku.’”
24 And the Lord did so. And there came very grievous flies into the houses of Pharaoh and of his servants, and into all the land of Egypt. And the land was polluted, in this way, by the flies.
Ubangiji kuwa ya yi haka. Tarin ƙuda suka zubo a fadar Fir’auna da cikin gidajen bayinsa, da ko’ina a Masar, ƙasar kuwa ta lalace saboda ƙudaje.
25 And Pharaoh called Moses and Aaron, and he said to them, “Go and sacrifice to your God in this land.”
Sai Fir’auna ya kira Musa da Haruna ya ce, “Ku tafi, ku miƙa hadaya ga Allahnku, a nan a cikin ƙasar.”
26 And Moses said: “It cannot be so. For we will immolate the abominations of the Egyptians to the Lord our God. For if we slaughter those things which the Egyptians worship, in their presence, they will stone us.
Amma Musa ya ce, “Wannan ba zai yiwu ba. Hadayun da mukan miƙa wa Ubangiji, Allahnmu haram ne ga Masarawa. In kuwa muka miƙa hadayun da suke haram a idanunsu, ba za su jajjefe mu ba?
27 We will sojourn three days’ journey into the wilderness. And we will sacrifice to the Lord our God, just as he has instructed us.”
Dole mu yi tafiya kwana uku cikin hamada domin miƙa hadayu ga Ubangiji Allahnmu, yadda ya umarce mu.”
28 And Pharaoh said: “I will release you in order to sacrifice to the Lord your God in the desert. Yet you may only go so far. Petition for me.”
Fir’auna ya ce, “Zan bar ku ku tafi, don ku miƙa hadayu ga Ubangiji Allahnku, a cikin hamada, amma ba za ku tafi da nisa ba. Yanzu ku yi mini addu’a.”
29 And Moses said: “After departing from you, I will pray to the Lord. And the flies will withdraw from Pharaoh, and from his servants, and from his people, tomorrow. Yet do not be willing to deceive any longer, so that you would not release the people to sacrifice to the Lord.”
Musa ya amsa, “Da zarar na bar ka, zan yi addu’a ga Ubangiji, gobe kuwa ƙudaje za su bar Fir’auna da fadawansa da kuma mutanensa. Sai dai a tabbata Fir’auna bai sāke yin ruɗi ta wurin ƙin barin mutane su tafi su miƙa hadayu ga Ubangiji ba.”
30 And Moses, departing from Pharaoh, prayed to the Lord.
Sa’an nan Musa ya rabu da Fir’auna, ya kuma yi addu’a ga Ubangiji,
31 And he acted according to his word. And he took away the flies from Pharaoh, and from his servants, and from his people. There was not even one left behind.
Ubangiji kuwa ya yi abin da Musa ya roƙa. Ƙudaje suka rabu da Fir’auna da fadawansa da kuma mutanensa; ba ƙudan da ya rage.
32 And the heart of Pharaoh was hardened, so that, even at this turn, he would not release the people.
Amma a wannan lokaci ma, Fir’auna ya taurare zuciyarsa, bai kuma bar mutanen suka tafi ba.

< Exodus 8 >