< Exodus 5 >

1 After these things, Moses and Aaron entered, and they said to Pharaoh: “Thus says the Lord God of Israel: Release my people, so that they may sacrifice to me in the desert.”
Daga bisani sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir’auna suka ce, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Bari mutanena su tafi domin su yi mini biki a hamada.’”
2 But he responded: “Who is the Lord, that I should listen to his voice and release Israel? I do not know the Lord, and I will not release Israel.”
Fir’auna ya ce, “Wane ne Ubangiji da zan yi biyayya da shi, har in bar Isra’ila su tafi? Ban san Ubangiji ba, kuma ba zan bar Isra’ila su tafi ba.”
3 And they said: “The God of the Hebrews has called us, so that we may go three days’ journey into the wilderness and sacrifice to the Lord our God. Otherwise, a pestilence or the sword may befall us.”
Sai suka ce, “Allah na Ibraniyawa ya sadu da mu. Yanzu bari mu ɗauki tafiyar kwana uku cikin hamada domin mu miƙa hadaya ga Ubangiji Allahnmu, don kada yă buga mu da annoba ko takobi.”
4 The king of Egypt said to them: “Why do you, Moses and Aaron, distract the people from their works? Go back to your burdens.”
Amma sarkin Masar ya ce wa, “Musa da Haruna, don me kuke hana mutane yin aikinsu? Ku koma wurin aikinku!”
5 And Pharaoh said: “The people of the land are many. You see that the turmoil has increased: how much more if you give them rest from the works?”
Sa’an nan Fir’auna ya ce, “Ga shi mutane sun yi yawa a ƙasar Masar, ku kuma yanzu kuna so ku hana su yin aiki.”
6 Therefore, on the same day, he instructed the overseers of the works, and the taskmasters of the people, saying:
A wannan rana Fir’auna ya ba da wannan umarni wa shugabannin masu gandu,
7 “You shall no longer give chaff to the people to form bricks, as before. But they may go and gather straw.
“Kada ku ƙara ba wa mutanen ciyawar tattaka domin su yi tubula, bari su tafi su tattara tattaka da kansu.
8 And you shall impose upon them the same quota of bricks that they made before. Neither will you lessen anything, for they are idle, and therefore they cry out, saying: ‘We shall go and sacrifice to our God.’
Ku kuma bukace su su yi tubula daidai yawan tubalin da suka saba yi, kada ku rage. Ragwaye ne, shi ya sa suke kuka cewa, ‘Bari mu tafi mu yi hadaya ga Allahnmu.’
9 They shall be oppressed with works, and these shall occupy them, so that they may not agree to lying words.”
Ku sa waɗannan mutane su yi aiki mai tsanani sosai, don kada su sami zarafin kasa kunne ga maganganun ƙarya.”
10 And so the overseers of the works and the taskmasters went out and said to the people: “Thus says Pharaoh: I give you no chaff.
Sai shugabannin masu aikin gandu suka fita suka gaya wa mutanen Isra’ila, “Ga abin da Fir’auna ya ce, ‘Ba zan ƙara ba ku tattaka ba.
11 Go, and collect it wherever you are able to find it. Neither will anything of your work be diminished.”
Ku tafi ku nemo wa kanku tattaka duk inda za ku samu, amma ba za a rage aikinku ba ko kaɗan.’”
12 And the people were dispersed through all the land of Egypt, in order to gather straw.
Saboda haka mutane suka warwatsu ko’ina a Masar domin tattara bunnun da za su yi amfani da su, maimakon tattaka.
13 Likewise, the overseers of the works pressured them, saying: “Complete your work each day, just as you were accustomed to do before, when straw was given to you.”
Shugabannin gandu suka dinga matsa musu suna cewa, “Ku cika aikin da aka bukace ku na kowace rana kamar yadda kuke yi sa’ad da kuke da tattaka.”
14 And those who were first in the works of the sons of Israel were scourged by Pharaoh’s taskmasters, saying: “Why have you not filled the quota of bricks, neither yesterday, nor today, just as before?”
Manyan Isra’ilawa waɗanda shugabannin gandun Fir’auna suka naɗa, suka sha dūka, aka kuma yi musu tambayoyi ana cewa, “Don me ba ku cika yawan tubula na jiya da na yau kamar yadda kuka saba ba?”
15 And the first among the sons of Israel came, and they cried out to Pharaoh, saying: “Why do act against your servants in this way?
Sai manyan Isra’ila masu bi da aikin gandu suka tafi wurin Fir’auna suka yi roƙo suna cewa, “Don me kake yi wa bayinka haka?
16 Straw is not given to us, and yet the same amount of bricks is commanded. So we, your servants, are cut up by scourging, and injustice is done against your people.”
Ba a ba wa bayinka tattaka, duk da haka ana ce mana, ‘Ku yi tubula!’ Ana wa bayinka dūka, amma fa laifin na mutanenka ne.”
17 And he said: “You are idle. And for this reason you say, ‘We shall go and sacrifice to the Lord.’
Fir’auna ya ce, “Ku ragwaye ne! Shi ya sa kuke cewa, ‘Bari mu tafi mu yi hadaya wa Ubangiji.’
18 Therefore, go and work. Straw will not be given to you, and you will return the customary number of bricks.”
Ku ɓace yanzu daga nan, ku koma wurin aikinku. Ba za a ba ku tattaka ba, kuma dole ku fid da tubula kamar yadda kuka saba.”
19 And the first among the sons of Israel saw themselves in a crisis, because it was said to them, “Nothing at all will be lessened from the bricks throughout each day.”
Manyan Isra’ilawa da suke bi da aikin gandu suka gane cewa sun shiga uku, sa’ad da aka gaya musu, “Ba za ku rage yawan tubulan da aka bukace ku ku yi na kowace rana ba.”
20 And they met with Moses and Aaron, who stood opposite them as they departed from Pharaoh.
Da suka bar Fir’auna, sai suka sadu da Musa da Haruna suna jira su sadu da su,
21 And they said to them: “May the Lord see and judge, because you have caused our odor to become foul before Pharaoh and his servants, and you have provided him with a sword, in order to kill us.”
sai suka ce, “Bari Ubangiji yă duba, yă kuma hukunta ku! Kun maishe mu abin ƙyama ga Fir’auna da bayinsa, kuka kuma sa musu takobi a hannunsu don su kashe mu.”
22 And Moses returned to the Lord, and he said: “Lord, why have you afflicted this people? Why have you sent me?
Musa ya koma wurin Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji, don me ka kawo wahala a kan mutanen nan? Abin da ya sa ka aiko ni ke nan?
23 For from the time that I entered to Pharaoh, so as to speak in your name, he has afflicted your people. And you have not freed them.”
Gama tun da na tafi wurin Fir’auna, na yi masa magana da sunanka, sai ya fara gasa wa mutanen nan azaba, ba ka kuma ceci mutanenka.”

< Exodus 5 >