< Luka 3 >

1 A cikin shekara ta goma sha biyar da Tibariyus Kaisar ke mulki, Bilatus Babunti kuma ke jagorar Yahudiya, Hirudus yana sarautar Galili, dan'uwansa Filibus yana sarautar yankin Ituriya da Tirakonitis, Lisaniyas kuma na sarautar yankin Abiliya,
Men i Kejser Tiberius's femtende Regeringsår, da Pontius Pilatus var Landshøvding i Judæa, og Herodes var Fjerdingsfyrste i Galilæa, og hans Broder Filip var Fjerdingsfyrste i Ituræa og Trakonitis's Land og Lysanias Fjerdingsfyrste i Abilene,
2 kuma zamanin da Hanana da Kayafa suke manyan firistoci, maganar Allah ta zo wurin Yahaya dan Zakariya, a cikin jeji.
medens Annas og Kajfas vare Ypperstepræster, kom Guds Ord til Johannes, Sakarias's Søn, i Ørkenen.
3 Ya yi tafiya cikin dukan yankuna da ke kewaye da Kogin Urdun, yana wa'azin baftismar tuba domin gafarar zunubai.
Og han gik ud i hele Omegnen om Jordan og prædikede Omvendelses-Dåb til Syndernes Forladelse,
4 Kamar yadda aka rubuta a cikin littafin annabi Ishaya, “Ga muryan wani yana kira a cikin jeji, 'Shirya hanyar Ubangiji, ka daidaita tafarkunsa!
som der er skrevet i Profeten Esajas's Talers Bog: "Der er en Røst af en, som råber i Ørkenen: Bereder Herrens Vej, gører hans Stier jævne;
5 Za a cika kowani kwari, za a fasa kowani dutse a kuma baje kowani tudu, za a mike karkatattun hanyoyi, za a cike hanyoyi masu gargada,
hver Dal skal opfyldes, og hvert Bjerg og Høj skal nedtrykkes, og det krumme skal gøres lige, og de ujævne Veje skulle gøres jævne;
6 kuma dukan mutane za su ga ceton Allah.”
og alt Kød skal se Guds Frelse."
7 Sai Yahaya ya kara fada wa taron jama'ar da ke zuwa domin ya yi masu baftisma, “Ku 'ya'yan macizai masu dafi, wa ya gargadeku ku guje wa fushin nan mai zuwa?
Han sagde altså til de Skarer, som gik ud for at døbes af ham: "I Øgleunger! hvem har lært eder at fly fra den kommende Vrede?
8 Ku ba da 'ya'ya da sun cancanci tuba, kada ku kuma fara cewa a cikinku, 'Muna da Ibrahim a matsayin Ubanmu', domin ina gaya maku, Allah yana iya ta da wa Ibrahim 'ya'ya daga cikin wadannan duwatsu.
Bærer da Frugter, som ere Omvendelsen værdige, og begynder ikke at sige ved eder selv: Vi have Abraham til Fader; thi jeg siger eder, at Gud kan opvække Abraham Børn af disse Sten.
9 Yanzu kuwa, an rigaya an sa gatari a gindin itatuwa. Sabili da haka, duk itacen da bai ba da 'ya'ya masu kyau ba za a sare shi kasa a kuma jefa shi cikin wuta.”
Men Øksen ligger også allerede ved Roden af Træerne; så bliver da hvert Træ, som ikke bærer god Frugt, omhugget og kastet i Ilden."
10 Sai mutanen da ke cikin taron jama'ar suka tambaye shi cewa, “To me za mu yi?”
Og Skarerne spurgte ham og sagde: "Hvad skulle vi da gøre?"
11 Ya amsa ya ce masu, “Idan wani yana da taguwa biyu, sai ya ba wanda bashi da ita daya, kuma wanda yake da abinci ya yi haka nan.”
Men han svarede og sagde til dem: "Den, som har to Kjortler, dele med den, som ingen har; og den, som har Mad, gøre ligeså!"
12 Masu karban haraji ma suka zo domin a yi masu baftisma, suka ce masa, “Malam, me za mu yi?”
Men også Toldere kom for at døbes, og de sagde til ham: "Mester! hvad skulle vi gøre?"
13 Ya ce masu, “Kada ku karba kudi fiye da yadda aka umarce ku.”
Men han sagde til dem: "Kræver intet ud over, hvad eder er forordnet."
14 Wasu sojoji ma suka tambaye shi cewa, “To, mu fa? Yaya za mu yi?” Ya ce masu, “Kada ku kwace wa wani kudi, kada ku kuma yi wa wani zargin karya. Ku dogara ga albashinku.”
Men også Krigsfolk spurgte ham og sagde: "Hvad skulle vi da gøre?" Og han sagde til dem: "Øver ikke Vold imod nogen, bruger ikke Underfundighed imod nogen, og lader eder nøje med eders Sold!"
15 Ana nan da mutane ke sauraron zuwan Almasihu, kowa yana ta tunani a zuciyar sa game da Yahaya, ko shi ne Almasihu.
Men da Folket var i Forventning, og alle tænkte i deres Hjerter om Johannes, om ikke han skulde være Kristus,
16 Yahaya ya amsa ya ce masu duka, “Game da ni dai, na yi maku baftisma da ruwa, amma akwai wani tafiye wanda ya fi ni iko, ban ma isa in kwance maballin takalmansa ba. Shi zai yi maku baftisma da Ruhu Mai Tsarki da kuma wuta.
da svarede Johannes og sagde til alle: "Jeg døber eder med Vand; men den kommer, som er stærkere end jeg, og hvis Skotvinge jeg ikke er værdig at løse; han skal døbe eder med den Helligånd og Ild.
17 Kwaryar shikarsa na hanun sa domin ya share masussukarsa da kyau ya kuma tara alkama a cikin rumbunsa. Amma zai kona buntun da wuta marar mutuwa.
Hans Kasteskovl er i hans Hånd, for at han skal gennemrense sin Lo og sanke Hveden i sin Lade, men Avnerne skal han opbrænde med uslukkelig Ild."
18 Da gargadi masu yawa ya yi wa mutanen wa'azin bishara.
Ligeså formanede han også Folket om mange andre Ting og forkyndte dem Evangeliet.
19 Yahaya kuma ya tsauta wa sarki Hirudus domin ya auri matar dan'uwansa, Hiruduya, da kuma sauran abubuwan da Hirudus ya yi.
Men da Fjerdingsfyrsten Herodes blev revset af ham for hans Broders Hustru, Herodias's Skyld og for alt det onde, som Herodes gjorde,
20 Amma Hirudus ya kara yin wani mugun abu. Ya sa an kulle Yahaya a cikin kurkuku.
så føjede han til alt det øvrige også dette, at han kastede Johannes i Fængsel.
21 Ana nan, lokacin da ake yiwa dukan mutane baftisma, aka yiwa Yesu mai baftisma. Lokacin da yake yin addu'a, sai sama ta bude,
Men medens hele Folket blev døbt, skete det, da også Jesus var bleven døbt og bad, at Himmelen åbnedes,
22 kuma Ruhu Mai Tsarki ya sauko masa a kamanin kurciya, sai wata murya ta fito daga sama, “Kai ne kaunataccen Da na. Ina jin dadin ka.”
og at den Helligånd dalede ned over ham i legemlig Skikkelse som en Due, og at en Røst lød fra Himmelen: "Du er min Søn, den elskede, i dig har jeg Velbehag."
23 Ana nan Yesu da kansa, da ya fara, yana kimanin shekara talatin. Shi dan (kamar yadda ake tsammani) Yusufu ne, dan Heli,
Og Jesus selv var omtrent tredive År, da han begyndte, og han var, som man holdt for, en Søn af Josef Elis Søn,
24 dan Matat, dan Lawi, dan Malki, dan Yanna, dan Yusufu,
Matthats Søn, Levis Søn, Melkis Søn, Jannajs Søn, Josefs Søn,
25 dan Matatiya, dan Amos, dan Nahum, dan Hasli, dan Najjaya,
Mattathias's Søn, Amos's Søn, Naums Søn, Eslis Søn, Naggajs Søn,
26 dan Ma'ata, dan Matatiya, dan Shimeya, dan Yuseka, dan Yoda,
Måths Søn, Mattathias's Søn, Semeis Søn, Josefs Søn, Judas Søn,
27 dan Yowana, dan Resa, dan Zarubabila, dan Shiyaltiyel, dan Niri,
Joanans Søn, Resas Søn, Zorobabels Søn; Salathiels Søn, Neris Søn.
28 dan Malki, dan Addi, dan Kosama, dan Almadama, dan Er,
Melkis Søn, Addis Søn, Kosams Søn, Elmadams Søn, Ers Søn,
29 dan Yosi, dan Aliyeza, dan Yorima, dan Matat, dan Lawi,
Jesu Søn, Eliezers Søn, Jorims Søn, Matthats Søn, Levis Søn,
30 dan Saminu, dan Yahuda, dan Yusufu, dan Yonana, dan Aliyakima,
Simeons Søn, Judas Søn, Josets Søn, Jonams Søn, Eliakims Søn,
31 dan Malaya, dan Mainana, dan Matata, dan Natan, dan Dauda,
Meleas Søn, Mennas Søn, Mattathas Søn, Nathans Søn, Davids Søn,
32 dan Yesse, dan Obida, dan Bu'aza, dan Salmon, dan Nashon,
Isajs Søn, Obeds Søn, Boos's Søn, Salmons Søn, Nassons Søn,
33 dan Amminadab, dan Adimi, dan Arama, dan Hezruna, dan Feresa, dan Yahuda,
Aminadabs Søn, Arams Søn, Esroms Søn, Fares's Søn, Judas Søn,
34 dan Yakubu, dan Ishaku, dan Ibrahim, dan Tera, dan Nahor,
Jakobs Søn, Isaks Søn, Abrahams Søn, Tharas Søn, Nakors Sn,
35 dan Serug, dan Reyu, dan Feleg, dan Abiru, dan Shela,
Seruks Søn, Ragaus Søn, Faleks Søn, Ebers Søn, Salas Søn,
36 dan Kainana, dan Arfakshada, dan Shem, dan Nuhu, dan Lamek,
Kajnans Søn, Arfaksads Søn, Sems Søn, Noas Søn, Lameks Søn,
37 dan Metusela, dan Anuhu, dan Yaret, dan Mahalel, dan Kainana,
Methusalas Søn, Enoks Søn, Jareds Søn, Maleleels Søn, Kajnans Søn,
38 dan Enosh, dan Shitu, dan Adamu, dan Allah.
Enos's Søn, Seths Søn, Adams Søn, Guds Søn.

< Luka 3 >