< Luka 4 >

1 Sai Yesu, cike da Ruhu Mai Tsarki, ya dawo daga kogin Urdun, sai Ruhu Mai Tsarki ya bishe shi zuwa cikin jeji
Men Jesus vendte tilbage fra Jorden fuld af den Helligånd og blev ført af Ånden i Ørkenen
2 kwana arba'in, shaidan kuma ya jarabce shi. A kwanakin nan, bai ci abinci ba, kuma yunwa ta kama shi bayan karshen lokacin.
i fyrretyve Dage, medens han blev fristet af Djævelen. Og han spiste intet i de Dage; og da de havde Ende, blev han hungrig.
3 Shaidan ya ce masa, “Idan kai Dan Allah ne, ka umarci wannan dutse ya zama gurasa.”
Og Djævelen sagde til ham: "Dersom du er Guds Søn, da sig til denne Sten, at den skal blive Brød."
4 Yesu ya amsa masa, “A rubuce yake, 'Ba da gurasa kadai Mutum zai rayu ba.'”
Og Jesus svarede ham: "Der er skrevet: Mennesket skal ikke leve af Brød alene."
5 Sai shaidan ya kai shi zuwa wani tudu mai tsawo, ya kuma nuna masa dukan mulkokin duniyan nan a dan lokaci.
Og han førte ham op og viste ham alle Verdens Riger i et øjeblik.
6 Shaidan ya ce masa, “Zan ba ka iko ka yi mulkin dukan wadannan, da dukan daukakarsu. Zan yi haka domin an ba ni su duka in yi mulkinsu, kuma ina da yanci in ba dukan wanda na ga dama.
Og Djævelen sagde til ham: "Dig vil jeg give hele denne Magt og deres Herlighed; thi den er mig overgiven, og jeg giver den, til hvem jeg vil.
7 Saboda da haka, idan ka rusuna ka yi mani sujada, dukansu za su zama naka.”
Dersom du altså vil tilbede mig, skal den helt tilhøre dig."
8 Amma Yesu ya amsa ya ce masa, “A rubuce yake, 'Dole ne Ubangiji Allahnka za ka yi wa sujada, shi kadai kuma za ka bauta wa.”
Og Jesus svarede ham og sagde: "Der er skrevet: Du skal tilbede Herren din Gud og tjene ham alene."
9 Sai shaidan ya kai Yesu Urushalima, ya tsayadda shi a bisan kololuwar haikali, kuma ya ce masa, “Idan kai Dan Allah ne, ka jefas da kanka kasa daga nan.
Og han førte ham til Jerusalem og stillede ham på Helligdommens Tinde og sagde til ham: "Dersom du er Guds Søn, da kast dig ned herfra;
10 Domin a rubuce yake, 'Zai ba mala'ikunsa umarni su kiyaye ka, su kuma tsare ka,'
thi der er skrevet: Han skal give sine Engle Befaling om dig, at de skulle bevare dig,
11 kuma, 'Za su daga ka sama a hannunsu, don kada ka yi tuntube a kan dutse.”
og at de skulle bære dig på Hænderne, for at du ikke skal støde din Fod på nogen Sten."
12 Yesu ya amsa masa cewa, “An fadi, 'Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.'”
Og Jesus svarede og sagde til ham: "Der er sagt: Du må ikke friste Herren din Gud."
13 Da shaidan ya gama yi wa Yesu gwaji, sai ya kyale shi sai wani lokaci.
Og da Djævelen havde endt al Fristelse, veg han fra ham til en Tid.
14 Sai Yesu ya koma Galili cike da ikon Ruhu, kuma labarinsa ya bazu cikin dukan wuraren dake wannan yankin.
Og Jesus vendte i Åndens Kraft tilbage til Galilæa, og Rygtet om ham kom ud i hele det omliggende Land.
15 Ya yi ta koyarwa a cikin majami'unsu, sai kowa na ta yabon sa.
Og selv lærte han i deres Synagoger og blev prist af alle.
16 Wata rana ya zo Nazarat, birnin da aka rene shi. Kamar yadda ya saba yi, ya shiga cikin majami'a a nan ranar Asabaci, ya kuma tashi tsaye domin ya karanta Nassi.
Og han kom til Nazareth, hvor han var opfødt, og gik efter sin Sædvane på Sabbatsdagen ind i Synagogen og stod op for at forelæse.
17 An mika masa littafin anabi Ishaya, ya bude littafin ya kuma ga inda an rubuta,
Og man gav ham Profeten Esajas's Bog, og da han slog Bogen op; fandt han det Sted, hvor der stod skrevet:
18 “Ruhun Ubangiji yana kai na, domin ya shafe ni in yi wa'azin Bishara ga matalauta. Ya aike ni in yi shelar yanci ga daurarru, da kuma budewar idanu ga makafi, in 'yantar da wadanda su ke cikin kunci,
"Herrens Ånd er over mig, fordi han salvede mig til at forkynde Evangelium for fattige; han har sendt mig for at forkynde fangne, at de skulle lades løs, og blinde, at de skulle få deres Syn, for at sætte plagede i Frihed,
19 in kuma yi shelar shekarar tagomashi na Ubangiji.”
for at forkynde et Herrens Nådeår."
20 Sai ya rufe littafin, ya mai da shi ga ma'aikacin majami'ar, sai ya zauna. Dukan wadanda suke cikin majami'ar suka zura Idanuwansu a kansa.
Og han lukkede Bogen sammen og gav Tjeneren den igen og satte sig; og alles Øjne i Synagogen stirrede på ham.
21 Sai ya fara masu magana, “Yau wannan Nassi ya cika a kunuwanku.”
Men han begyndte at sige til dem: "I Dag er dette Skriftord gået i Opfyldelse for eders Øren."
22 Dukan wadanda ke wurin sun shaida abin da ya fadi kuma dukansu sun yi ta mamakin kalmomin alheri da suke fitowa daga bakinsa. Suna cewa, “Wannan ai dan Yusufu ne kawai, ko ba haka ba?”
Og de berømmede ham alle og undrede sig over de livsalige Ord, som udgik af hans Mund, og de sagde: "Er dette ikke Josefs Søn?"
23 Yesu ya ce masu, “Lallai za ku fada mani wannan karin magana, 'Likita, ka warkar da kanka. Duk abin da mun ji wai ka yi a Kafarnahum, ka yi shi a nan garinka ma.'”
Og han sagde til dem: "I ville sikkerlig sige mig dette Ordsprog: Læge! læg dig selv; gør også her i din Fædreneby så. store Ting, som vi have hørt ere skete i Kapernaum."
24 Ya sake cewa, “Hakika na fada maku, annabi baya samun karbuwa a garinsa.
Men han sagde: "Sandelig, siger jeg eder, at ingen Profet er anerkendt i sit Fædreland.
25 Amma na gaya maku gaskiya akwai gwauraye da yawa cikin Isra'ila a zamanin Iliya, lokacin da an rufe sammai shekaru uku da rabi babu ruwa, lokacin da anyi gagarumar yunwa a duk fadin kasar.
Men jeg siger eder i Sandhed: Der var mange Enker i Israel i Elias's Dage, da Himmelen var lukket i tre År og seks Måneder, den Gang der var en stor Hunger i hele Landet;
26 Amma ba a aiki Iliya zuwa wurin waninsu ba, sai wurin gwauruwa da ke a Zarifat can kusa da Sidon.
og til ingen af dem blev Elias sendt uden til Sarepta ved Sidon til en Enke.
27 Akwai kutare da yawa kuma a Isa'ila a zamanin anabi Elisha, amma babu wanda aka warkar sai dai Na'aman mutumin Suriya kadai.
Og der var mange spedalske i Israel på Profeten Elisas Tid, og ingen af dem blev renset, uden Syreren Naman."
28 Dukan mutanen da ke cikin majami'a suka fusata kwarai sa'adda suka ji wadannan zantattuka.
Og alle, som vare i Synagogen, bleve fulde af Harme, da de hørte dette.
29 Suka tashi suka tura shi zuwa wajen birnin, suka kai shi bakin dutsen da aka gina garinsu a kai dominsu jefar da shi kasa.
Og de stode op og stødte ham ud af Byen og førte ham hen til Skrænten af det Bjerg, på hvilket deres By var bygget, for at styrte ham ned.
30 Amma ya ratsa tsakaninsu ya yi gabansa.
Men han gik igennem, midt imellem dem, og drog bort.
31 Sannan ya gangara zuwa Kafarnahum, wani birni a Galili. Wata Asabaci yana koya wa mutane a cikin majami'a.
Og han kom ned til Kapernaum, en By i Galilæa, og lærte dem på Sabbaterne.
32 Sun yi mamaki kwarai da koyarwan sa, domin maganarsa na da iko.
Og de bleve slagne af Forundring over hans Lære, thi hans Tale var med Myndighed.
33 A wannan lokacin akwai wani mutum a cikin majami'a mai kazamin ruhu, sai ya yi kara da babbar murya,
Og i Synagogen var der et Menneske, som havde en uren ond Ånd, og han råbte med høj Røst:
34 “Ina ruwan mu da kai, Yesu Banazarat? Ka zo domin ka hallaka mu ne? Na san ko kai wanene! Kai ne Mai Tsarki na Allah!”
"Ak! hvad have vi med dig at gøre, Jesus af Nazareth? Er du kommen for at ødelægge os? Jeg kender dig, hvem du er, du Guds hellige."
35 Yesu ya tsauta wa aljanin yana cewa, “Yi shiru ka fita daga cikinsa!” Da aljanin ya jefar da mutumin kasa a tsakiyarsu, ya fita daga cikinsa ba tare da yi masa rauni ba.
Og Jesus truede ham og sagde: "Ti, og far ud af ham!" Og den onde Ånd kastede ham ind imellem dem og for ud af ham uden at have gjort ham nogen Skade.
36 Dukan mutanen suka yi mamaki, kuma suna ta zancen wannan abu a tsakaninsu. Sun ce, “Wanda irin maganganu kenan? Ya umarce kazaman ruhohin da karfi da iko kuma sun fita.”
Og der kom en Rædsel over alle; og de talte med hverandre og sagde "Hvad er dog dette for et Ord; thi han byder over de urene Ånder med Myndighed og Kraft, og de fare ud?"
37 Saboda da haka, an fara yada labarinsa zuwa dukan kewayen yankin.
Og Rygtet om ham udbredtes alle Vegne i det omliggende Land.
38 Sai Yesu ya bar majami'ar ya shiga gidan Siman. A wannan lokacin, surukar Siman tana fama da zazzabi mai zafi, sai suka roke shi dominta.
Men han stod op og gik fra Synagogen ind i Simons Hus; og Simons Svigermoder plagedes at en stærk Feber; og de bade ham for hende.
39 Sai ya tsaya a kanta, ya tsautawa zazzabin, kuma ya rabu da ita. Nan take, ta tashi ta fara yi masu hidima.
Og han stillede sig hen over hende og truede Feberen, og den forlod hende. Men hun stod straks op og vartede dem op.
40 Da faduwar rana, mutane suka kawo wa Yesu dukan wadanda suke ciwo da cuttuttuka dabam dabam. Ya dora masu hannuwansa ya warkar da su.
Men da Solen gik ned, førte alle de, som havde syge med alle Hånde Svagheder, dem til ham; og han lagde Hænderne på hver enkelt af dem og helbredte dem
41 Aljanu kuma sun fita daga wadasunsu da dama, suna kuka cewa, “Kai ne Dan Allah!” Yesu ya tsauta wa aljannun ya kuma hana su magana, domin sun sani cewa shine Almasihu.
Også onde Ånder fore ud al mange, råbte og sagde: "Du er Guds Søn;" og han truede dem og tillod dem ikke at tale, fordi de vidste, at han var Kristus.
42 Da safiya ta yi, ya kebe kansa zuwa wani wurin da babu kowa. Jama'a da dama suna neman sa suka zo inda yake. Sun yi kokari su hana shi barin su.
Men da det var blevet Dag, gik han ud og drog til et øde Sted; og Skarerne ledte efter ham; og de kom hen til ham, og de holdt på ham, for at han ikke skulde gå fra dem.
43 Amma ya ce masu, “Dole in yi bisharar Allah a wasu birane da dama, domin dalilin da aka aiko ni nan kenan.”
Men han sagde til dem: "Også for de andre Byer bør jeg forkynde Evangeliet om Guds Rige; thi dertil blev jeg udsendt."
44 Sai ya ci gaba da wa'azi cikin majami'u dukan fadin Yahudiya.
Og han prædikede i Galilæas Synagoger.

< Luka 4 >