< Luka 2 >

1 Ananan cikin kwanakin, sai Kaisar Augustas ya yi shela ya umarta a kidaya dukan mutane da ke zaune a cikin duniya.
Men det skete i de dage, at en Befaling udgik fra Kejser Augustus, at al Verden skulde skrives i Mandtal.
2 Wannan itace kidaya ta farko da aka yi lokacin da Kiriniyus yake mulkin Suriya.
(Denne første Indskrivning skete, da Kvirinius var Landshøvding i Syrien, )
3 Sabili da haka, kowa ya koma garinsa domin a yi masa rijista domin kidayan.
Og alle gik for at lade sig indskrive, hver til sin By.
4 Yusufu kuma ya tashi ya bar birnin Nazarat zuwa garin Baitalami da ke Yahudiya, wanda ake kuma kira birnin Dauda, domin shi daga zuriyar iyalin Dauda ne.
Og også Josef gik op fra Galilæa, fra Byen Nazareth til Judæa til Davids By, som kaldes Bethlehem, fordi han var af Davids Hus og Slægt,
5 Ya je can ya yi rijista tare da Maryamu, wadda yake tashi tana kuma da juna biyu.
for at lade sig indskrive tillige med Maria, sin trolovede, som var frugtsommelig.
6 Ya zama sa'adda suke can, lokaci ya yi da za ta haifi danta.
Men det skete, medens de vare der, blev Tiden fuldkommet til, at hun skulde føde.
7 Ta haifi da, dan farinta kuwa, ta nade shi da kyau da 'yan tsummoki. Ta sa shi cikin wani kwami na dabbobi, gama babu daki dominsu a masaukin.
Og hun fødte sin Søn, den førstefødte, og svøbte ham og lagde ham i en Krybbe; thi der var ikke Rum for dem i Herberget.
8 A cikin wannan yankin, akwai makiyaya wadanda suke zama a sarari suna tsaron garken tumakinsu da dare.
Og der var Hyrder i den samme Egn, som lå ude på Marken og holdt Nattevagt over deres Hjord.
9 Nan da nan, sai mala'ikan Ubangiji ya bayyana gare su, daukakar Ubangiji kuma ta haskaka kewaye da su, sai suka figita kwarai.
Og se, en Herrens Engel stod for dem, og Herrens Herlighed skinnede om dem, og de frygtede såre
10 Sai mala'ikan ya ce masu, “Kada ku ji tsoro, domin na kawo maku labari mai dadi da zai kawo murna da yawa ga dukan mutane.
Og Engelen sagde til dem: "Frygter ikke; thi se, jeg forkynder eder en stor Glæde, som skal være for hele Folket.
11 Yau an haifi maku mai ceto a cikin birnin Dauda! Shine Almasihu Ubangiji!
Thi eder er i dag en Frelser født, som er den Herre Kristus i Davids By.
12 Wannan itace alama da za a ba ku. Za ku ga dan jariri nade cikin 'yan tsummoki kwance cikin kwamin dabbobi.”
Og dette skulle I have til Tegn: I skulle finde et Barn svøbt, liggende i en Krybbe."
13 Nan take, sai ga babban taro daga sama tare da mala'ikan suna yabon Allah, suna cewa,
Og straks var der med Engelen en himmelsk Hærskares Mangfoldighed, som lovede Gud og sagde:
14 “Daukaka ga Allah daga bisa, bari salama ta kasance a duniya tsakanin mutanen da ya ke jin dadinsu.”
"Ære være Gud i det højeste! og Fred på Jorden! i Mennesker Velbehag!
15 Ya zama sa'adda mala'iku suka bar su zuwa cikin sama, sai makiyayan su ka ce wa junansu, “Bari mu je Baitalami mu ga wannan abin da ya faru, wanda Ubangiji ya nuna mana.”
Og det skete, da Englene vare farne fra dem til Himmelen, sagde Hyrderne til hverandre: "Lader os dog gå til Bethlehem og se dette, som er sket, hvilket Herren har kundgjort os."
16 Su ka yi hamzari suka tafi can sun iske Maryamu da Yusufu, suka ga jaririn kuwa kwance a cikin kwamin dabbobin.
Og de skyndte sig og kom og fandt både Maria og Josef, og Barnet liggende i Krybben.
17 Bayan da sun ga wannan, suka gaya wa mutane abinda aka gaya masu game da wannan yaro.
Men da de så det, kundgjorde de, hvad der var talt til dem om dette Barn.
18 Dukan wadanda su ka ji, su ka yi mamaki kwarai game da abin da makiyayan su ka gaya masu.
Og alle de, som hørte det, undrede sig over det, der blev talt til dem af Hyrderne.
19 Amma ita Maryamu ta ci gaba da tunani akan wadanan abubuwa da ta ji, tana tunani mai zurfi a cikin zuciyarta.
Men Maria gemte alle disse Ord og overvejede dem i sit Hjerte.
20 Makiyayan suka koma suna ta daukaka da yabon Allah domin dukan abubuwan da suka ji, suka kuma gani, dadai da yadda aka gaya masu.
Og Hyrderne vendte tilbage, idet de priste og lovede Gud for alt, hvad de havde hørt og set, således som der var talt til dem.
21 Da ya kai kwana takwas, lokacin da za a yi wa jaririn kaciya, sai aka rada masa suna Yesu, sunan da mala'ikan ya bashi kamin a yi cikinsa.
Og da otte Dage vare fuldkommede, så han skulde omskæres, da blev hans Navn kaldt Jesus, som det var kaldt af Engelen, før han blev undfangen i Moders Liv.
22 Da kwanakin tsarkakewar su ya wuce bisa ga shari'ar Musa, Yusufu da Maryamu suka kawo shi cikin haikali a Urushalima dominsu mika shi ga Ubangiji.
Og da deres Renselsesdage efter Mose Lov vare fuldkommede, bragte de ham op til Jerusalem for at fremstille ham for Herren,
23 Kamar yadda aka rubuta a dokokin Ubangiji, “Za a kira duk da na fari kebabbe ga Ubangiji.”
som der er skrevet i Herrens Lov, at alt Mandkøn, som åbner Moders Liv, skal kaldes helligt for Herren,
24 Suka kuma zo su mika hadaya bisa ga yadda aka fada a shari'ar Ubangiji, “Kurciyoyi biyu ko 'yan tantabaru biyu.”
og for at bringe Offer efter det, som er sagt i Herrens Lov, et Par Turtelduer eller to unge Duer.
25 Ga shi akwai wani mutum a Ushalima mai suna Siman. Wannan mutum adali ne kuma mai ibada. Yana jiran mai ta'aziyar Isra'ila, kuma Ruhu Mai-sarki na bisansa.
Og se, der var en Mand i Jerusalem ved Navn Simeon, og denne Mand var retfærdig og gudfrygtig og forventede Israels Trøst, og den Helligånd var over ham.
26 An kuma bayyana masa ta wurin Ruhu Mai-tsarki cewa ba zai mutu ba sai ya ga Kristi na Ubangiji.
Og det var varslet ham af den Helligånd, at han ikke skulde se Døden, førend han havde set Herrens Salvede.
27 Wata rana Siman ya zo cikin haikali ta wurin jagorar Ruhu Mai-tsarki. Da iyayen suka kawo yaron ciki, wato Yesu, domin su cika sharudan da shari'ar ke bukata,
Og han kom af Åndens Drift til Helligdommen; og idet Forældrene bragte Barnet Jesus ind for at gøre med ham efter Lovens Skik,
28 sai Siman ya karbe shi cikin hanuwansa, ya yabi Allah ya ce,
da tog han det på sine Arme og priste Gud og sagde:
29 “Yanzu bari bawanka ya tafi da salama, Ubangiji, bisa ga kalmarka.
"Herre! nu lader du din Tjener fare i Fred, efter dit Ord.
30 Domin idanuna sun ga cetonka,
Thi mine Øjne have set din Frelse,
31 wanda ka shirya a gaban dukan mutane:
som du beredte for alle Folkeslagenes Åsyn,
32 Haske ne na wahayi ga al'ummai, kuma daukakar mutanenka Isra'ila.”
et Lys til at oplyse Hedningerne og en Herlighed for dit Folk Israel."
33 Mahaifin yaron da Mahaifiyarsa, sun yi mamaki kwarai domin abubuwan da aka fada akansa.
Og hans Fader og hans Moder undrede sig over de Ting, som bleve sagte om ham.
34 Sai Siman ya albarkace su ya ce wa uwatasa Maryamu, “Ki ji da kyau, wannan yaro zai zama sanadiyar faduwa da tashin mutane dayawa a Isra'ila, kuma alama wadda ake kushen ta.
Og Simeon velsignede dem og sagde til hans Moder Maria: "Se, denne er sat mange i Israel til Fald og Oprejsning og til et Tegn, som imodsiges,
35 Kuma takobi zai tsaga zuciyar ki yadda tunanin mutane za ya bayyana.”
ja, også din egen Sjæl skal et Sværd gennemtrænge! for at mange Hjerters Tanker skulle åbenbares."
36 Wata annabiya mai suna Annatu ta na nan wurin. Ita diyar Fanuyila ce daga kabilar Ashiru. Ta riga ta manyanta a shekaru sosai. Ta kasance da maigidanta shekaru bakwai bayan auren ta,
Og der var en Profetinde Anna, Fanuels Datter, af Asers Stamme; hun var meget fremrykket i Alder, havde levet syv År med sin Mand efter sin Jomfrustand
37 sannan ta yi zama gwambranci na shekaru tamanin da hudu. Ba ta taba barin haikali ba, tana ci gaba da yi wa Ubangiji sujada, dare da rana.
og var nu en Enke ved fire og firsindstyve År, og hun veg ikke fra Helligdommen, tjenende Gud med Faste og Bønner Nat og Dag.
38 A dadai lokacin nan, ta hau zuwa wurinsu ta fara yi wa Allah godiya. Ta gaya wa dukan wadanda ke jiran fansar Urushalima.
Og hun trådte til i den samme Stund og priste Gud og talte om ham til alle, som forventede Jerusalems Forløsning.
39 Da su ka gama komai da aka bukace su suyi bisa ga tafarkin shari'ar Ubangiji, sai suka koma Galili, zuwa birninsu, Nazarat.
Og da de havde fuldbyrdet alle Ting efter Herrens Lov, vendte de tilbage til Galilæa til deres egen By Nazareth.
40 Yaron kuma ya yi girma ya zama da karfi, yana karuwa da hikima, alherin Ubangiji kuma yana kansa.
Men Barnet voksede og blev stærkt og blev fuldt af Visdom: og Guds Nåde var over det.
41 Iyayensa sukan tafi Urushalima kowacce shekara domin idin ketarewa.
Og hans Forældre droge hvert År op til Jerusalem på Påskehøjtiden.
42 Da yana shekara goma sha biyu, suka sake haurawa daidai lokacin idin a al'adance.
Og da han var bleven tolv År gammel, og de gik op efter Højtidens Sædvane
43 Bayan da sun cika dukan kwanakin idin, sun fara dawowa gida. Amma dan yaron Yesu ya jinkirta ya zauna a Urushalima, kuma iyayensa basu sani ba.
og havde tilendebragt de Dage, blev Barnet Jesus i Jerusalem, medens de droge hjem, og hans Forældre mærkede det ikke.
44 Suna tsammani yana tare da sauran mutane da suke tafiya tare, sai suka yi tafiya na kwana daya. Suka fara neman sa a cikin danginsu da abokansu.
Men da de mente, at han var i Rejsefølget, kom de en Dags Rejse frem, og de ledte efter ham iblandt deres Slægtninge og Kyndinge.
45 Da ba su gan shi ba, sai suka koma Urushalima suna cigiyar sa a can.
Og da de ikke fandt ham, vendte de tilbage til Jerusalem og ledte efter ham.
46 Ya zama bayan kwanaki uku, su ka same shi a cikin haikali, yana zama a tsakiyar malamai, yana sauraron su yana kuma yi masu tambayoyi.
Og det skete efter tre Dage, da fandt de ham i Helligdommen, hvor han sad midt iblandt Lærerne og både hørte på dem og adspurgte dem.
47 Dukan wadanda suka ji shi suna ta mamakin fahimtar sa da amsoshin sa.
Men alle, som hørte ham, undrede sig såre over hans Forstand og Svar.
48 Da suka gan shi, suka yi mamaki kwarai. Mahaifiyarsa ta ce masa, “Da na, don me ka yi mana haka? Ka ji, mahaifinka da ni muna ta neman ka rai a bace.”
Og da de så ham, bleve de forfærdede; og hans Moder sagde til ham:"Barn! hvorfor gjorde du således imod os? Se, din Fader og jeg have ledt efter dig med Smerte."
49 Ya ce masu, “Don me kuke nema na? Ba ku sani cewa dole in kasance a gidan Ubana ba?”
Og han sagde til dem: "Hvorfor ledte I efter mig? Vidste I ikke, at jeg bør være i min Faders Gerning?"
50 Amma ba su gane abin da yake nufi da kalmomin nan ba.
Og de forstode ikke det Ord, som han talte til dem.
51 Sa'annan ya koma gida tare da su zuwa Nazarat yana kuma masu biyayya. Mahaifiayarsa kuma ta ajiye dukan wadannan abubuwa a zuciyarta tana yin tunani akansu.
Og han drog ned med dem og kom til Nazareth og var dem lydig og hans Moder gemte alle de Ord i sit Hjerte.
52 Amma Yesu ya ci gaba da hikima da girma, ya kuma karu da tagomashi wurin Allah da mutane.
Og Jesus forfremmedes i Visdom og Alder og yndest hos Gud og Mennesker.

< Luka 2 >