< Luka 18 >

1 Ya kuma ba su wani misali cewa ya kamata kullum su yi addu'a kada kuma su karaya,
He also taught them by a parable how they ought always to pray and never to lose heart.
2 yace, “A wani gari an yi wani alkali mara tsoron Allah, kuma baya ganin darajan mutane.
"There was a certain town," he said, "a judge who had neither reverence for God, nor respect for man.
3 Akwai wata mace gwauruwa a wannan garin, wadda ta rika zuwa wurinsa, tana ce masa, 'Ka taimake ni yanda zan sami adalci a kan abokin gaba na.'
"In that same town there was a widow who came again and again before him, saying, "‘Do for me the justice of my adversary.’
4 An dade bai so ya taimaka mata, amma daga baya sai ya ce a ransa, 'ko da yake ba na tsoron Allah, ba na kuma darajanta mutane,
"For a while he would not, but afterwards he said to himself, ‘Though I have neither reverence for God nor regard for man,
5 duk da haka saboda gwauruwar nan ta dame ni, zan taimake ta domin ta sami adalci, yadda ba za ta gajiyar da ni da zuwanta wurina ba.'”
"‘yet because this woman annoys me I will give her justice, lest by her continual coming she wear me out.’
6 Sai Ubangiji ya ce, “Ku ji fa abin da alkalin nan marar gaskiya ya fada.
"Listen" said the Lord, "to what this unjust judge says.
7 A yanzu Allah ba zai biya wa zababbunsa da suke yi masa kuka dare da rana hakkinsu ba? Zai yi jinkiri a wajen taimakonsu ne?
"And will not God see justice done to his elect who are crying unto him day and night, even if he seems to delay helping them?
8 Ina gaya maku, zai biya masu hakkin su da wuri. Amma sa'adda Dan Mutum ya zo, zai tarar da bangaskiya a duniya?”
"I tell you that he will quickly see justice done to his elect! Nevertheless, when the Son of man comes, will he find faith upon the earth?"
9 Ya sake ba da misalin nan ga wadansu masu amincewa da kansu, wai su masu adalci ne, har suna raina sauran mutane,
Moreover he spoke this parable to some who trusted in themselves because they were righteous, and looked down upon the rest.
10 “Wadansu mutane biyu suka shiga haikali domin yin addu'a - daya Bafarise, dayan kuma mai karbar haraji ne.
"Two men are going up to the temple to pray; the one a Pharisee, the other a tax-gatherer.
11 Sai Bafarisen ya mike, ya yi addu'a a kan wadannan abubuwa game da kansa, 'Allah, na gode maka, da cewa ni ba kamar sauran mutane dake mazambata ba, ko marasa adalci, ko mazinata, ko kamar wannan mai karbar harajin.
"The Pharisee stood apart and thus began to pray by himself. "‘O God, I thank thee that I am not like the rest of men, extortioners, rogues, adulterers, or even like this tax gatherer;
12 Duk mako ina azumi sau biyu. Nakan bayar da zakkar dukan abin da na samu.'
"‘I fast twice a week, I pay tithes of all my possessions.’
13 Amma mai karbar harajin kuwa yana tsaye daga can nesa, bai yarda ya daga kai sama ba, sai dai yana bugun kirjin sa, yana cewa, 'Allah, ka yi mini jinkai, ni mai zunubi.'
"But the tax-gatherer, standing far back, would not lift up so much as his eyes to heaven, but kept beating his breast and saying, "‘O God be merciful to me, the sinner!’
14 Ina gaya maku, wannan mutum ya koma gidansa baratacce, ba kamar dayan ba, domin dukan wanda ya daukaka kansa, za a kaskantar da shi, amma duk wanda kaskantar da kansa kuwa daukaka shi za a yi.”
"I tell you that this man went down to his house justified rather than the other; for every one who exalts himself shall be humbled; but he who humbles himself shall be exalted."
15 Sai mutanen suka kawo masa jariransu, domin ya taba su, da almajiransa suka ga haka, sai suka kwabe su.
And they kept bringing their babies for him to touch them; but when his disciples saw it they began to rebuke them.
16 Amma Yesu ya kira su wurinsa, ya ce, “Ku bar yara kanana su zo wurina, kada ku hana su. Ai mulkin Allah na irin su ne.
But Jesus called for the babies. "Let the little children come to me," he said, "do not hinder them; for of such is the kingdom of heaven.
17 Gaskiya ina gaya maku, duk wanda bai karbi mulkin Allah kamar karamin yaro ba, lallai ba zai shige shi ba.”
"I tell you in solemn truth that whoever will not receive the kingdom of God like a little child, he will never get into it."
18 Wani shugaban jama'a ya tambaye shi ya ce “Malam managarci, me zan yi in gaji rai Madawwami?” (aiōnios g166)
A ruler put this question to him. "Good teacher, what shall I do to inherit eternal life?" (aiōnios g166)
19 Yesu ya ce masa, “Don me ka kira ni managarci? Babu wani managarci sai Allah kadai.
"Why are you calling me ‘good’?"said Jesus to him; "no one is good but God.
20 Ka dai san dokokin - kada ka yi zina, kada ka yi kisankai, kada ka yi sata, kada ka yi shaidar karya, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.”
"You know the commandments. "Do not commit adultery, Do not murder, Do not steal, Do not bear false witness, Honor your father and mother."
21 Sai shugaban ya ce, “Dukan wadannan abubuwa na kiyaye su tun a kuruciya ta.”
"All of these," he replied, "I have kept from my youth up."
22 Da Yesu ya ji haka, ya ce masa, “Abu daya ne kadai ya rage maka. Dole ne ka sayar da dukan mallakarka, ka rarraba wa gajiyayyu, za ka kuma sami wadata a sama - sa'annan ka zo ka biyoni.”
And receiving this reply, Jesus said to him. "One thing you are still lacking. Sell all that you have and give it to the poor, and you shall have treasure in heaven. Then come and follow me."
23 Amma da mai arzikin ya ji wadannan abubuwa, sai yayi bakin ciki kwarai, don shi mai arziki ne sosai.
But when he heard these words he became deeply grieved, for he was exceedingly rich.
24 Yesu kuwa, da ya ga ransa ya baci, sai ya ce, “Yana da wuya masu dukiya su shiga mulkin Allah!
Jesus looked at him and said. "How hard it is for those who have money to enter into the kingdom of God!
25 Zai zama da sauki rakumi ya shiga kafar allura, da mai arziki ya shiga mulkin Allah.”
Why, it is easier for a camel to go through the eye of a needle than for a rich man to enter into the kingdom of God."
26 Wadanda suka ji wannan magana suka ce, “Idan hakane wa zai sami ceto kenan?”
"Who then can be saved?" exclaimed his hearers.
27 Yesu ya amsa, “Abin da ya fi karfin mutum, mai yiwuwa ne a gun Allah.”
"Things that are impossible with men," he answered them, "are possible with God."
28 Sai Bitrus ya ce, “To, ga shi mun bar mallakarmu, mun bi ka.”
Then Peter said, "Look! we have left our homes and followed you."
29 Yesu ya ce masu, “Hakika, ina gaya maku, ba wanda zai bar gida, ko matarsa, ko 'yan'uwansa, ko iyayensa, ko kuma 'ya'yansa, saboda mulkin Allah,
And he said to them, "In Solemn truth I tell you that there is no one who, for the sake of the kingdom of God, has left houses, or wife, or brother, or parents, or children,
30 sa'annan ya kasa samun ninkin ba ninkin a duniyan nan, da rai na har abada a duniya mai zuwa.” (aiōn g165, aiōnios g166)
"who shall not certainly receive many times as much in this time, and in the age to come eternal." (aiōn g165, aiōnios g166)
31 Bayan da ya tara su goma sha biyun nan, ya ce masu, “Ga shi, muna tafiya zuwa Urushalima, duk abubuwan da aka rubuta game da Dan Mutum ta hannun annabawa zasu tabbata.
Then he took the twelve aside and told them. "See, we are on our way to Jerusalem, and all prophets regarding the son of Man will be fulfilled.
32 Gama za a bashe shi ga al'ummai, a yi masa ba'a, a wulakanta shi, a kuma tofa masa miyau.
"He will be betrayed to the Gentiles, and be mocked, and shamefully treated, and spit upon;
33 Za su yi masa bulala, su kashe shi, a rana ta uku kuma zai tashi.”
"and they will scourge and kill him; and the third day he will rise again."
34 Amma ba su fahimci ko daya daga cikin wadannan abubuwa ba, domin zancen nan a boye yake daga garesu, ba su ma gane abin da aka fada ba.
But they understood none of these sayings. His words were a mystery to them, and they did not know what he meant.
35 Da ya kusato Yariko, ga wani makaho zaune a gefen hanya, yana bara,
As Jesus drew near to Jericho, there was a blind man who sat by the wayside begging.
36 da ya ji taro na wucewa, sai ya tambaya ko menene.
He heard the crowd passing and asked what the matter was.
37 Suka ce masa Yesu Banazarat ne yake wucewa.
They told him, "Jesus of Nazareth is passing by."
38 Sai makahon ya ta da murya mai karfi, ya ce, “Yesu, Dan Dauda, ka yi mani jinkai.”
Then he shouted out, saying, "Jesus, son of David, take pity on me!"
39 Sai wadanda suke gaba suka kwabe shi, suna gaya masa ya yi shiru. Amma ya kara daga murya kwarai da gaske, yana cewa, “Dan Dauda, ka yi mani jinkai.”
Those who went ahead began to reprove him and to tell him to be still; but he kept clamorously shouting all the more, "Son of David, take pity on me!"
40 Sai Yesu ya tsaya, ya umarta a kawo shi wurinsa. Da makahon ya zo kusa, sai Yesu ya tambaye shi,
So Jesus stopped and ordered him to be brought to him. When he was come near to him he asked him
41 “Me kake so in yi maka?” Ya ce, “Ubangiji, ina so in samu gani.”
"What do you want me to do for you?" "Lord," he answered, "that I might see again."
42 Yesu ya ce masa, “Karbi ganin gari, bangaskiyarka ta warkar da kai.”
"Receive your sight," said Jesus, "your faith has saved you."
43 Nan take ya samu gani, ya bi Yesu, yana daukaka Allah. Ganin haka, sai duk jama'a suka yabi Allah.
Instantly he regained his sight and followed Jesus, giving glory to God; and all the people who saw it gave praise to God.

< Luka 18 >