< Markus 1 >

1 Wannan itace farkon bisharar Yesu Almasihu, Dan Allah.
Beginning of the gospel of Jesus Christ, the Son of God;
2 kamar yadda aka rubuta cikin littafin annabi Ishaya. Duba, ina aika manzona, a gabanka, wanda zai shirya maka hanya.
even as it is written in the prophet Isaiah, Behold, I am sending my messenger before your face to prepare your way.
3 Akwai murya mai kira a jeji, tana cewa ka shirya hanyar Ubangiji. ka daidaita ta.
The voice of one crying aloud. In the desert make ready a road for the Lord. Make his paths straight.
4 Yahaya ya zo, yana baptisma acikin jeji yana wa'azin tuba, domin gafarar zunubai.
In the desert came Johnwho baptized, and preached a baptism of repentance for the remission of sins;
5 Dukan kasar Yahudiya da mutanen Urshalima suka zo wurin sa, a ka kuma yi masu baptisma a kogin urdun. suna furta zunubansu.
and all the land of Judea, and all the people of Jerusalem, kept going out to him, and were baptized by him in the Jordan river, confessing their sins.
6 Yahaya yana saye da tufa ta gashin rakumi, yana kuma da damara ta fata a kugunsa, abincinsa fara ce da zuma.
And Johnwas clothed with camel’s hair, and he had a leather girdle round his loins, and he ate locusts, and "honey of the wood."
7 Yana wa'azi, ya ce “akwai mai zuwa a bayana wanda ya ke da iko fiye da ni. wanda ko maballin takalminsa ban isa in kwance ba.
He made proclamation. "There is One mightier than I coming after me, and I am not worthy to stoop down and unfasten his sandal strap;
8 Ni ina yi maku baptisma da ruwa, amma mai zuwa a bayana zai yi maku baptisma da Ruhu Mai Tsarki''.
I have baptized you in water, but he shall baptize you in the Holy Spirit."
9 Sai ya kasance a kwanakin nan Yesu ya zo daga Nazarat ta Galili, sai Yahaya ya yi masa baptisma a kogin urdun.
It was at that time that Jesus came from Nazareth of Galilee, and was baptized by Johnin the Jordan;
10 Sa'adda Yesu ya fito daga ruwan, sai sama ta bude, sai Ruhu ya sauko a bisansa da kamanin kurciya.
and as soon as he rose from the water he saw the sky cleft asunder, and the Spirit like a dove descending upon him,
11 Sai wata murya ta zo daga sama, tana cewa, “Kai kaunataccen Dana ne. zuciyata ta na murna da kai kwarai''.
and a voice from the sky. "Thou art my Son, my beloved; in thee is my delight."
12 Sai Ruhu ya iza shi zuwa jeji.
Then the Spirit drove him at once into the desert,
13 Yana a jeji kwana arba'in, Shaidan yana jarabtar sa. Yana cikin jeji da dabobi, sai malaiku su ka yi masa hidima.
and he remained in the desert for forty days, tempted by Satan; and he was among the wild beasts, but the angels were ministering to him.
14 Bayan da aka kama Yahaya, Yesu ya shiga kasar Galili yana wa'azin bisharar Allah.
After Johnhad been thrown into prison Jesus came into Galilee preaching the gospel of God.
15 Yana cewa, “Lokaci ya yi, gama mulkin Allah ya kusato. Ku tuba ku bada gaskiya ga bishara”.
"The time is now come," he said, "and the kingdom of God is near! Repent and believe the gospel."
16 Sa'adda ya ke wucewa a gefen takun Galili, sai ya ga Saminu da Andarawus, dan'uwansa suna jefa taru a teku, domin su masunta ne.
And as he was passing along by the sea of Galilee he saw Simon and Andrew, Simon’s brother, casting their net into the sea, for they were fishermen;
17 Yesu ya ce masu ku zo, ku biyo ni, ni kuwa sai in maisheku masuntan mutane”.
so Jesus said to them, "Come after me, and I will make you to become fishers of men."
18 Nan da nan suka bar tarun su, suka bi shi.
At once they left their nets and followed him.
19 Sa'adda Yesu ya yi tafiya kadan, sai ya ga Yakubu dan Zabadi da Yahaya dan'uwansa; suna gyaran tarunsu a jirgin ruwa.
As he went a little farther on he saw James, the son of Zebedee, and Johnhis brother, who also were in their boat mending the nets.
20 Sai ya kira su, su kuwa suka bar mahaifinsu Zabadi a jirgin ruwan da ma'aikatansu, sai su ka bi shi.
Straightway he called them, and they left their father Zebedee in the ship with the hired servants and went after him.
21 Da su ka shigo cikin kafanahum, a ranar asabar, Yesu ya shiga majami'a ya koya masu.
So they came to Capernaum, and as soon as the Sabbath Day came he went into the synagogue and began to teach.
22 Su ka yi mamakin koyarwarsa, domin ya na koya masu da iko ba kamar marubuta ba.
They were astonished at his teaching, for he was teaching them with authority, not like the Scribes.
23 A nan cikin majami'a akwai wani mutum mai kazamin ruhu, sai ya yi ihu da karfi.
And at that very moment, there in their synagogue, a man in the grip of an unclean spirit shrieked out.
24 Yana cewa Ina ruwan mu da kai, Yesu Banazarat? Ka zo ne domin ka halakar da mu? Na san wanene kai. Kai ne Mai Tsarki na Allah”.
"What business have you with us, you Jesus of Nazareth? Are you come to destroy us? I know you who you are, the Holy One of God."
25 Sai Yesu ya tsauta wa kazamin ruhun ya ce, “Ka yi shiru ka fita daga cikinsa”.
But Jesus rebuked him, saying. "Be quit! Come out of him."
26 Bayan da kazamin ruhun ya buga shi kasa, sai kazamin ruhun ya yi ihu sa'annan ya fita daga jikinsa.
So the unclean spirit, after tearing him, came out of him with a loud cry;
27 Sai dukan mutanen su ka yi mamaki kwarai, suna tambayar junansu menene wannan? wace sabuwar koyarwa ce da iko haka? har yana umartar kazaman ruhohi suna kuwa yi masa biyayya!”
and every one was amazed so that they began questioning among themselves. "What does this mean? A new teaching with authority? He lays commands even upon unclean spirits and they obey him."
28 Nan da nan labarinsa ya bazu ko'ina a dukkan kewayen kasar Galili.
And at once his fame spread everywhere through that part of Galilee.
29 Bayan da suka bar majami'a, sai su ka shiga gidan Saminu da Andarawus, suna kuma tare da Yakubu da Yahaya.
On leaving the synagogue they went at once with Jamesand Johnto the house of Simon and Andrew.
30 Surikar Saminu tana kwance ba lafiya tana fama da zazzabi. Sai suka gaya wa Yesu game da ita.
Now Simon’s mother-in-law lay sick of fever, and without delay they told him about her.
31 Sai ya zo, ya kama hannunta, ya daga ta, sai zazzabin ya sake ta, ta fara yi masu hidima.
So he came and took her hand and raised her up. The fever left her at once, and she began to wait upon them.
32 Da yamman nan, bayan da rana ta fadi, sai su ka kawo masa dukan marasa lafiya da masu fama da aljanu.
At evening when the sun had set, people came and brought to him all the sick and demon-possessed,
33 Dukan mutanen garin su ka taru a bakin kofa.
and the whole town was gathered at the door.
34 ya warkar da masu ciwo da yawa da masu chututtuka iri-iri, ya kuma fitar da bakaken aljanu, amma bai yarda aljanun su yi magana ba domin sun san shi.
He cured many who were ill with various diseases, and drove out many demons. But he did not allow the demons to speak, because they knew who he was.
35 Ya tashi da sassafe, tun da sauran dare, ya tafi wurin da ba kowa, a can ya yi add'ua.
In the morning he rose a great while before day and went out to a desert place, and there prayed.
36 Saminu da wandanda suke tare da shi suka neme shi.
And Simon and his companions hunted him up,
37 Suka sa me shi, sai su ka ce masa, “kowa yana nemanka”.
and told him, "Every one is looking for you."
38 Ya ce, bari mu tafi wani wuri, zuwa wadansu garuruwan da ke kewaye, Saboda in yi wa'azi a can kuma. Wannan shi yasa na zo nan''.
"Let us go away," he answered, "to the neighboring country towns, that I may preach there, too; because for that purpose I came forth."
39 Ya tafi dukan kasar Galili, yana wa'azi a majimi'un su yana kuma fitar da aljanu.
So he went throughout Galilee, preaching in the synagogues and driving out demons.
40 Wani kuturu ya zo wurinsa. Yana rokonsa, ya durkusa. Ya ce masa, “in ka yarda kana iya warkar da ni.
One day a leper cane to him and besought him as he knelt down to him, saying, "If you choose, you are able to cleanse me."
41 Sai ya yi juyayi, Yesu ya mi ka hannun sa ya ta ba shi ya na ce masa “Na yarda. Ka sarkaka”.
Jesus, moved with compassion, put out his hand and touched him, saying, "I do choose, be clean!"
42 Nan da nan kuturtar ta barshi, ya kuma sa mu tsarkakewa.
The leprosy at once left him, and he was made clean.
43 Yesu ya yi masa gargadi sosai, ya salame shi.
Jesus immediately sent him away, charging him sternly and saying.
44 Ya ce masa “ka tabbata fa kada ka gayawa kowa, amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, sai ka je ka yi hadaya domin tsarkakewa kamar yadda Musa ya umurta, domin shaida.
"See you say nothing to any one; but go your way, show yourself to the priest, and offer for your purification what Moses commanded for a testimony to them."
45 Amma da ya fita sai ya fara gaya wa kowa, ya baza maganar a ko'ina, har Yesu bai iya tafiya a sake a garin ba. Ya tafi ya tsaya a wuraren da ba kowa, mutane kuwa su ka zo wurinsa daga ko'ina.
But he went out and began to tell every one and to publish it broadcast, so that Jesus could no longer enter any town openly; but he had to remain outside in lonely places, and people kept coming to him from every quarter.

< Markus 1 >