< Luka 7 >

1 Bayan da Yesu ya gama fadar dukan abubuwan da zai fadi a jin kunnen dukan mutanen, sai ya shiga Kafarnahum.
After he had ended all his sayings in the hearing of the people, he went to Capernaum.
2 Bawan wani jarumi, wanda yake kauna, ba shi da lafiya har ma ya kusa mutuwa.
Here the slave of a certain Roman captain, a man dear to his master, was ill, and at the point of death.
3 Amma da ya ji labarin Yesu, jarumin ya aiki wadansu dattawan Yahudawa, ya ce a roki Yesu ya zo ya ceci bawansa daga mutuwa.
So when the captain heard about Jesus, he sent elders of the Jews to ask him to come and save his slave.
4 Sa'adda su ka zo kusa da Yesu, su ka roke shi da gaske, cewa, “Wannan ya isa ka yi masa haka,
And they, when they reached Jesus, asked him earnestly to do this. "He deserves that you should do this," they said,
5 saboda shi mai kaunar kasar mu ne, kuma shi ne ya gina mana majami'a.
"for he loves our nation, and himself has built a synagogue for us."
6 Sai Yesu ya tafi tare da su. Amma sa'adda ya zo kusa da gidan mutumin, jarumin ya aiki abokansa su ka ce da shi, “Ubangiji kada ka damu domin ni ban isa ka zo gida na ba.
So Jesus started to go with them, but while he was not far from the house, the captain sent friends to him with a message. "Lord do not trouble yourself, for I am not fit that you should come under my roof,
7 Shi ya sa na ga ban isa in zo wurinka ba, ka yi magana kadai bawa na kuwa zai warke.
"and so I did not think myself worthy to come to you; but speak the word, and let my man be cured.
8 Gama ni ma mutum ne mai iko, ina da sojoji karkashina. Ina iya cewa da wannan, 'Ka je' sai ya tafi, in kuma ce da wani 'ka zo' sai ya zo, in kuma ce da bawa na, 'Yi kaza,' sai ya yi.”
"For I also am a man obedient to authority, and have soldiers under me. And I say to one ‘come,’ and he comes, and to my slave ‘do this or that,’ and he does it."
9 Sa'adda Yesu ya ji haka, ya yi mamakin mutumin, ya juya wajen taron da su ke biye da shi, ya ce, “Na gaya maku, ko a cikin Isra'ila ban sami wani mai bangaskiya irin wannan ba”
But when Jesus heard this he was astonished and he turned and said to the crowd that was following him, "I tell you that not even in Israel have I found faith like that."
10 Daga nan wadanda a ka aika, suka dawo gida suka tarar da bawan cikin koshin lafiya.
And those who had been sent, on returning to the house, found the slave well.
11 Wani lokaci bayan wannan, ya zama Yesu yana tafiya wani gari da ake kira Na'im. Almajiransa su na tare da shi, da kuma taron mutane masu yawa.
Soon afterward he went to a city called Nain, accompanied by his disciples, and a great crowd of people.
12 Sa'adda ya kusa da kofar garin, sai ga wani matacce ana dauke da shi. Kuma shi kadai ne da a wurin mahaifiyarsa. Ita kuwa gwauruwa ce, mutane da dama daga cikin gari suna tare da ita.
Now when he drew near the gate of the city, behold, they were there carrying out one who was dead, the only son of his mother, and she was a widow.
13 Da ganin ta, sai Ubangiji ya cika da tausayi a game da ita ya ce da ita, “Kada ki yi kuka.”
A great crowd accompanied her. And when the Lord saw her, he had compassion on her and said to her, "Do not weep."
14 Sai ya zo ya taba makarar, sai masu dauke da shi su ka tsaya. Ya ce 'Saurayi na ce ma ka ka tashi.”
And he came near and touched the bier; the bearer stopped and he said, "Young man, I bid you to rise."
15 Sai mataccen ya tashi ya fara yin magana. Sai Yesu ya ba mahaifiyar danta.
And he who was dead sat up and began to speak; and he gave him to his mother.
16 Sai tsoro ya kama su duka. Su ka kama yabon Allah, su na cewa, “An ta da wani annabi mai girma a cikinmu” kuma “Allah ya dubi mutanensa.”
And awe took hold on them all, and they began to glorify God saying. "A great prophet has risen among us;" and, "God has visited his people."
17 Wannan labari na Yesu, ya ba zu a cikin dukan Yahudiya da yankuna da su ke kewaye.
And the report of what Jesus had done went forth throughout Judea and the surrounding regions.
18 Almajiran Yahaya suka gaya masa dukan wadannan abubuwa.
John’s disciples brought him word of all these things
19 Sai Yahaya ya kira biyu daga cikin almajiransa, ya aike su wurin Ubangiji, suka ce da shi, “Kai ne mai zuwan nan, ko akwai wani wanda za mu saurari zuwansa?”
and, calling a certain two disciples to him, he sent them to Jesus, to say, "Are you ‘the coming one,’ or if we are to expect another?"
20 Sa'adda suka zo kusa da Yesu, sai mutanen suka ce, “Yahaya Mai Baftisma, ya aiko mu, mu tambaya, “Kai ne mai zuwan nan, ko akwai wani wanda za mu saurari zuwansa?”
So the men came to Jesus and said, "Johnthe Baptist has sent us to ask you if you are the coming one, or if we are to expect another."
21 A cikin wannan lokaci, ya warkar da mutane da yawa daga cututtuka da matsaloli da miyagun ruhohi. Makafi da yawa sun sami ganin gari.
At that moment Jesus was healing many people of diseases and plagues and evil spirits, and to many that were blind he was freely giving their sight.
22 Yesu, ya amsa ya ce masu, “Bayan kun tafi, ku ba Yohanna rahoton abin da ku ka ji da abin da ku ka gani. Makafi suna ganin gari, guragu suna tafiya, ana kuma tsarkake kutare. Kurame suna ji, ana tayar da matattu, ana gaya wa matalauta labari mai dadi.
So he answered them. "Go your way, tell Johnwhat you have seen and heard. How the blind are seeing, the lame are walking, the lepers are being cleansed, the deaf are hearing, the dead are being raised, and the poor are hearing the proclamations of glad tidings.
23 Mai albarka ne mutumin da ya tsaya a kan ba da gaskiya gare ni saboda ayukan da na ke yi.”
"And blessed is he who finds no cause of stumbling in me."
24 Bayan da mutanen da Yahaya ya aiko suka tafi, Yesu ya fara yi wa taron magana game da Yahaya. “Me ku ka tafi ku gani a cikin hamada, ciyawa wadda iska ta ke girgizawa?
When John’s messengers were gone he began to speak to the crowds about John, saying, "What went out you out to the desert to behold? A reed shaken by the wind?
25 Amma me ku ka tafi domin ku gani, mutum mai saye da tufafi masu taushi? Duba mutanen da su ke saye da tufafi masu daraja, kuma suna rayuwa cikin jin dadi suna fadar sarakuna.
"But what you went out to behold? A man clothed in soft robes? Behold, men who are gorgeously dressed and live in luxury are in kings’ palaces.
26 Amma me ku ka tafi domin ku gani, annabi ne? I, ina gaya ma ku, ya ma fi annabi.
"But what went you to see? A prophet?
27 Wannan shine wanda aka rubuta a kansa, “Duba, ina aika manzo na a gabanka, wanda za ya shirya maka hanya a gabanka.
"Yes, I tell you and more than a prophet. This is he who it is written. "Behold I send a messenger before thy face, Who shall prepare thy way before thee.
28 Ina gaya maku, a cikin wadanda mata suka haifa, ba wanda ya fi Yahaya girma. Duk da haka, wanda ya fi kankanta a mulkin Allah, ya fi shi girma.
"I tell you that among all that are born of women not one is greater than John; yet he that is little in the kingdom of God is greater than he."
29 Sa'anda dukan mutane suka ji haka, har da ma su karbar haraji, suka shaida Allah mai adalci ne. Su na cikin wadanda Yahaya ya yi wa baftisma.
On hearing this all the people and the tax-gatherers acknowledged the justice of God by being baptized with the baptism of John;
30 Amma Farisawa da wadanda su ke kwararru a cikin shari'ar Yahudawa, wadanda ba shi ne ya yi masu baftisma ba, suka yi watsi da hikimar Allah don kansu.
but the Pharisees and lawyers who had refused his baptism, frustrated God’s purpose for themselves.
31 Sa'annan Yesu ya ce, “Da me zan kamanta mutanen wannan zamani? Da me suka yi kama?
"To what then shall I compare the men of this generation?
32 Suna kama da yaran da suke wasa a kasuwa, wadanda suke magana da junansu suna cewa, “Mun yi maku busa, ba ku yi rawa ba. Mun yi makoki, ba ku yi kuka ba.”
"To What are they like, they are like children sitting in the market- place and calling to one another. "‘We have piped to you,’ they say, ‘and you have not danced; we have wailed, and you did not cry.’
33 Haka, Yahaya ya zo, bai ci gurasa ba, bai sha ruwan inabi ba, amma ku ka ce, 'Aljani ne yake mulkinsa.
"For Johnthe Baptist has come eating no bread and drinking no wine, and you say, ‘He has a demon!’
34 Dan Mutum, ya zo, yana ci, yana sha, amma, kuka ki shi, kuna cewa dubi mutum mai hadama, mai shan ruwan inabi da yawa, abokin masu karbar haraji da masu zunubi!
"The son of man has come eating and drinking, and you say, ‘Behold a gluttonous man and a winebibber, a friend of publicans and sinners!’
35 Amma hikimar Allah tana shaidar dukan 'yayanta.”
"Nevertheless, wisdom is justified by all her children."
36 Wata rana wani Bafarise, ya roki Yesu ya je ya ci abinci tare da shi. Bayan da Yesu ya shiga gidan Bafarisen, ya zauna a teburi domin ya ci abinci.
One of the Pharisees kept urging him to dine, so he entered the house and reclined at table.
37 Sai ga wata mace mai zunubi, ta fito daga cikin birni. Sa'anda ta ji labari Yesu yana gidan Bafarisen, domin ya ci abinci. Ta dauki tandun mai na alabastar mai kamshi.
Now there was a woman who was in the city, a sinner and when she knew that that Jesus was reclining at meat in the Pharisees house, she brought an alabaster vase of perfume,
38 Ta tsaya kusa da Yesu tana kuka. Ta fara jika kafafunsa da hawayenta, tana shafe kafafunsa da gashin kanta. Tana yi wa kafafunsa sumba, tana shafe su da turare.
and standing behind, at his feet, weeping, she began to wet his feet with her tears, and to wipe them with her hair, while she tenderly kissed his feet, and poured the perfume over them.
39 Sa'anda Bafarisen da ya gaiyaci Yesu, ya ga haka, sai ya yi tunani a cikin ransa, da cewa, “In da wannan mutum annabi ne, da ya gane ko wacce irin mace ce, wannan da take taba shi, ita mai zunubi ce.”
When he noticed this the Pharisee, who had invited him, said to himself, "If this man were really a prophet he would have perceived who and what sort of woman this is who is touching him, and would know that she is a sinner."
40 Yesu ya amsa ya ce masa, “Siman, ina so in gaya maka wani abu.” Ya ce, “malam sai ka fadi!”
Jesus then spoke to him. "Simon, I have a word to say to you." "Rabbi, say on," he replied.
41 Yesu ya ce, “wani mutum mai ba da bashi yana bin wadansu mutane su biyu kudi, yana bin dayan sule dari, dayan kuma yana bin sa sule hamsin.
"There were once to men," said Jesus, "in debt to one money- lender. One owed him fifty pounds; the other five.
42 Da yake ba su da kudin da za su iya biyan sa, sai ya yafe masu, su duka biyu. A cikin su biyu, wanne ne zai fi nuna kauna ga wannan mutum?”
"When they had nothing pay he forgave them with such charm. "Tell me, then, which of these will love him most?"
43 Siman ya amsa ya ce, “Ina tsammani wanda ya yafe wa kudi da yawa.” Yesu ya amsa ya ce masa, “Ka shari'anta dai dai.”
"I take it," said Simon, "the one he forgave the most."
44 Yesu ya juya wajen matar, ya ce da Siman, “Ka ga matan nan. Na shiga gidanka. Ba ka ba ni ruwa domin kafafuna ba, amma ita ta ba ni, da hawayenta ta wanke kafafuna, ta kuma shafe su da gashin kanta.
"You have rightly judged." answered Jesus, and turning to the woman, he said to Simon. "Do you see this woman? When I came into your house you gave me no water for my feet; but she has wet my feet with her tears and wiped them with her hair.
45 Kai ba ka yi ma ni sumba ba, amma ita ta yi, tun sa'adda na shigo nan ba ta dena sumbatar kafafuna ba.
"You gave me no kiss; but she, since she came in, has never ceased tenderly kissing my feet;
46 Kai ba ka shafe kai na da mai ba, amma ita ta shafe kafafuna da turare.
"you never anointed my head with oil; but she has anointed my feet with my feet with perfume.
47 Saboda haka, ita wadda ta ke da zunubi da yawa ta bayar da mai yawa, ta kuma nuna kauna mai yawa. Amma shi wanda aka gafarta wa kadan, ya kuma nuna kauna kadan.”
"This is why I tell you that her sins, many as they are, are forgiven, for her love is great; but he who is forgiven little, loves but little.
48 Daga nan sai ya ce mata, “An gafarta zunubanki.”
"Your sins are forgiven," he said to her.
49 Wadanda su ke a nan zaune tare da shi suka fara magana da junansu, “Wanene wannan wanda har yake gafarta zunubai?
Then the other guest began to say among themselves, "Who is this even to forgive sins?"
50 Sai Yesu ya ce da matar, “Bangaskiyarki ta cece ki. Ki tafi da salama.”
But he said to the woman. "Your faith has saved you. Go in peace."

< Luka 7 >