< Zabura 3 >

1 Zabura ta Dawuda. Sa’ad da ya gudu daga ɗansa Absalom. Ya Ubangiji, abokan gābana nawa ne! Su nawa suke gāba da ni!
[A Psalm by David, when he fled from Absalom his son.] Jehovah, how my adversaries have increased. Many rise up against me.
2 Da yawa suna magana a kaina suna cewa, “Allah ba zai cece shi ba.” (Sela)
Many there are who say of my soul, "There is no salvation for him in God." (Selah)
3 Amma kai ne garkuwa kewaye da ni, ya Ubangiji; ka ba ni ɗaukaka ka kuma ɗaga kaina.
But you, Jehovah, are a shield around me, my glory, and the one who lifts up my head.
4 Ga Ubangiji na yi kuka mai ƙarfi, ya kuwa amsa mini daga tudunsa mai tsarki. (Sela)
I cried out to Jehovah with my voice, and he answered me from his holy mountain. (Selah)
5 Na kwanta na yi barci; na kuma farka, gama Ubangiji yana kiyaye ni.
I lay down and slept. I awoke, for Jehovah sustains me.
6 Ba zan ji tsoro ko dubu goma suka ja dāgā gāba da ni a kowane gefe ba.
I am not afraid of ten thousands of people who have set themselves against me on every side.
7 Ka tashi Ya Ubangiji! Ka cece ni, ya Allahna! Ka bugi dukan abokan gābana a muƙamuƙi; ka kakkarya haƙoran mugaye.
Arise, Jehovah. Save me, my God. For you slap all my enemies in the face. You break the teeth of the wicked.
8 Daga wurin Ubangiji ne ceto kan zo. Bari albarkanka yă kasance a kan mutanenka. (Sela)
Salvation belongs to Jehovah. Your blessing is upon your people. (Selah)

< Zabura 3 >