< Karin Magana 1 >

1 Karin maganar Solomon ɗan Dawuda, sarkin Isra’ila.
The proverbs of Solomon, the son of David, king of Israel:
2 Ga karin magana da za su taimake ka don samun hikima da horo; don ganewa kalmomi masu zurfi;
To know wisdom and instruction, to discern the words of understanding.
3 don neman rayuwa ta horo da kuma ta hankali, kana yin abin da yake daidai, mai adalci da kuma wanda ya dace;
To receive instruction in wise dealing, in righteousness, justice, and equity.
4 don sa marar azanci yă yi hankali, yă sa matasa su sani, su kuma iya rarrabewa,
To give shrewdness to the inexperienced, knowledge and discretion to the young man.
5 bari masu hikima su saurara, su kuma ƙara ga saninsu, bari masu tunani kuma su sami jagora,
A wise man will hear and increase in learning, and a man of understanding will attain to sound counsel.
6 don su fahimci karin magana da kuma misalai, kalmomi da kuma kacici-kacici masu hikima.
To understand a proverb, and parables, the words and riddles of the wise.
7 Tsoron Ubangiji shi ne masomin ilimi, amma wawaye sun rena hikima da horo.
The fear of Jehovah is the beginning of knowledge; but the foolish despise wisdom and instruction.
8 Ɗana, ka saurari umarnin mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
My son, listen to your father's instruction, and do not forsake your mother's teaching:
9 Za su zama kayan ado don su inganta ka da kuma sarƙar wuya don su yi wa wuyanka ado.
for they will be a garland to grace your head, and a necklace around your neck.
10 Ɗana, in masu zunubi sun jarabce ka, kada ka yarda.
My son, if sinners entice you, do not consent.
11 In suka ce, “Zo mu tafi; mu yi kwanton ɓauna, mu nemi wani mu kashe, mu fāɗa wa marasa laifi;
If they say, "Come with us, Let's lie in wait for blood; let's lurk secretly for the innocent without cause;
12 mu haɗiye su da rai gaba ɗaya kamar kabari, kamar waɗanda suke gangarawa zuwa rami; (Sheol h7585)
let's swallow them up alive like Sheol, and whole, like those who go down into the pit. (Sheol h7585)
13 za mu sami dukiya masu daraja iri-iri, mu kuma cika gidajenmu da ganima;
We'll find all valuable wealth. We'll fill our houses with spoil.
14 ka haɗa kai da mu, za mu kuwa raba abin da muka sato”
Throw in your lot with us. We'll all have one purse."
15 ɗana, kada ka tafi tare da su, kada ka taka ƙafarka a hanyarsu;
My son, do not walk in the way with them. Keep your foot from their path,
16 gama ƙafafunsu kan yi sauri ga yin zunubi, suna saurin yin kisankai.
for their feet run to evil. They hurry to shed blood.
17 Ba shi da amfani a kafa tarko a idanun dukan tsuntsaye!
For in vain is the net spread in the sight of any bird:
18 Waɗannan irin mutane kansu suke kafa wa tarko; ba sa kama kome, sai rayukansu!
but these lie in wait for their own blood. They lurk secretly for their own lives.
19 Dukan waɗanda suke neman ribar da ba a samu a hanya mai kyau; ƙarshen wannan yakan ɗauke rayukansu.
So are the ways of everyone who is greedy for gain. It takes away the life of its owners.
20 Hikima tana kira da ƙarfi a kan titi, tana ɗaga muryarta a dandalin taron jama’a;
Wisdom calls aloud in the street. She utters her voice in the public squares.
21 tana kira da ƙarfi a kan tituna masu surutu, tana yin jawabinta a hanyoyin shiga gari.
She calls at the head of noisy places. At the entrance of the city gates, she utters her words:
22 “Har yaushe ku da kuke marasa azanci za ku ci gaba a hanyoyinku marasa azanci? Har yaushe ku masu ba’a za ku yi ta murna cikin ba’arku wawaye kuma ku ƙi ilimi?
"How long, you simple ones, will you love simplicity? How long will mockers delight themselves in mockery, and fools hate knowledge?
23 Da a ce kun saurari tsawatata, da na faɗa muku dukan abin da yake zuciyata in kuma sanar da ku tunanina.
Turn at my reproof. Look, I will pour out my spirit on you. I will make known my words to you.
24 Amma da yake kun ƙi ni sa’ad da na yi kira ba kuma wanda ya saurara sa’ad da na miƙa hannuna,
Because I have called, and you have refused; I have stretched out my hand, and no one has paid attention;
25 da yake kun ƙi dukan shawarata ba ku kuma yarda da tsawatata ba,
but you have ignored all my counsel, and wanted none of my reproof;
26 Zan yi muku dariya sa’ad da masifa ta same ku, zan yi muku ba’a sa’ad da bala’i ya same ku,
I also will laugh at your disaster. I will mock when calamity overtakes you;
27 sa’ad da bala’i ya sha kanku kamar hadiri, sa’ad da masifa ta share ku kamar guguwa, sa’ad damuwa da wahala suka mamaye ku.
when calamity overtakes you like a storm, when your disaster comes on like a whirlwind; when distress and anguish come on you.
28 “Sa’an nan za su kira gare ni amma ba zan amsa ba; za su neme ni amma ba za su same ni ba.
Then will they call on me, but I will not answer. They will seek me diligently, but they will not find me;
29 Da yake sun ƙi sani ba su kuwa zaɓi tsoron Ubangiji ba,
because they hated knowledge, and did not choose the fear of Jehovah.
30 da yake ba su karɓi shawarata ba suka kuwa yi kunnen ƙashi ga tsawatata,
They wanted none of my counsel. They despised all my reproof.
31 za su sami sakayyar abubuwan da suka yi su kuma ƙoshi da sakayyar makircinsu.
Therefore they will eat of the fruit of their own way, and be filled with their own schemes.
32 Gama rashin hankalin marasa azanci zai kashe su, rashin kulawar wawaye kuma zai hallaka su;
For the backsliding of the simple will kill them. The careless ease of fools will destroy them.
33 amma duk wanda ya saurare ni, zai zauna lafiya yă kuma kasance da rai kwance, ba tare da tsoron lahani ba.”
But whoever listens to me will dwell securely, and will be at ease, without fear of harm."

< Karin Magana 1 >