< Ƙidaya 22 >

1 Sai Isra’ilawa suka kama hanya, suka tafi filayen Mowab, a wajen Urdun, a ƙetare Yeriko, suka yi sansani a can.
The people of Israel traveled on until they camped in the plains of Moab near Jericho, on the other side of the Jordan River from the city.
2 To, fa, Balak ɗan Ziffor ya ga duk abin da Isra’ila suka yi da Amoriyawa.
Balak son of Zippor saw all that Israel had done to the Amorites.
3 Sai Mowab ya firgita ƙwarai saboda yawan mutanen. Tsoron Isra’ilawa ya kama su.
Moab was very afraid of the people because they were many, and Moab was in terror of the people of Israel.
4 Sai Mowabawa suka ce wa dattawan Midiyawa, “Wannan taron zai lashe duk abin da ya kewaye mu kamar yadda saniya takan lashe ciyawa a fili.” Saboda haka Balak ɗan Ziffor, wanda yake sarkin Mowab a lokacin,
The king of Moab said to the elders of Midian, “This multitude will eat up all that is around us as an ox eats up the grass in a field.” Now Balak son of Zippor was king of Moab at that time.
5 ya aika manzanni su zo da Bala’am ɗan Beyor, wanda yake a Fetor, kusa da Kogi, a ƙasar haihuwarsa. Balak ya ce, “Ga mutane sun fito daga Masar; sun mamaye ƙasar, suka kuma yi sansani kusa da ni.
He sent messengers to Balaam son of Beor, at Pethor which is by the Euphrates River, in the land of his nation and his people. He called him and said, “Look, a nation has come here from Egypt. They cover the face of the earth and they are right now next to me.
6 Ka zo yanzu ka la’anta waɗannan mutane, domin sun fi ƙarfina. Wataƙila zan iya cin nasara a kansu, in kuma kore su daga ƙasar. Gama na sani duk waɗanda ka sa musu albarka, sun zama masu albarka ke nan, waɗanda kuma ka la’anta, sun la’antu ke nan.”
So please come now and curse this nation for me, because they are too strong for me. Perhaps then I can manage to attack them and drive them out of the land. I know that whomever you bless will be blessed, and whomever you curse will be cursed.”
7 Sai dattawan Mowab da na Midiyawa suka tashi, suka ɗauki kuɗi don duba. Da suka zo wurin Bala’am sai suka faɗa masa abin da Balak ya ce.
So the elders of Moab and the elders of Midian left, taking payment for divination. They came to Balaam and spoke to him Balak's words.
8 Bala’am ya ce musu, “Ku kwana a nan, ni kuwa zan faɗa muku abin da Ubangiji ya faɗa mini.” Saboda haka dattawan sarkin Mowab suka zauna da shi.
Balaam said to them, “Stay here tonight. I will bring you what Yahweh says to me.” So the leaders of Moab stayed with Balaam that night.
9 Sai Allah ya zo wurin Bala’am ya ce, “Su wane ne waɗannan tare da kai?”
God came to Balaam and said, “Who are these men who came to you?”
10 Bala’am ya ce wa Allah, “Balak ɗan Ziffor, sarkin Mowab ne, ya aiko mini wannan saƙo cewa,
Balaam answered God, “Balak son of Zippor, king of Moab, has sent them to me. He said,
11 ‘Ga mutane sun fito daga Masar sun mamaye ƙasar. Ka zo yanzu ka la’anta mini su. Wataƙila ta haka zan yi nasara a kansu, in kuma kore su.’”
'Look, the people who have come from Egypt cover the surface of my land. Now come and curse them for me. Perhaps I will manage to fight them and drive them out.'”
12 Amma Allah ya ce wa Bala’am, “Kada ka tafi tare da su. Kada ka la’anta mutanen nan, gama su masu albarka ne.”
God replied to Balaam, “You must not go with those men. You must not curse the people of Israel because they have been blessed.”
13 Kashegari Bala’am ya tashi ya ce wa dattawan Balak, “Ku koma ƙasarku, domin Ubangiji ya hana ni in tafi tare da ku.”
Balaam rose up in the morning and said to Balak's leaders, “Go back to your land because Yahweh refuses to allow me to go with you.”
14 Saboda haka dattawan Mowab suka koma wurin Balak suka ce, “Bala’am ya ƙi yă zo tare da mu.”
So the leaders of Moab left and went back to Balak. They said, “Balaam refused to come with us.”
15 Sai Balak ya aika waɗansu dattawa masu yawa, masu daraja kuma fiye da na dā.
Balak sent again more leaders who were even more honored than the first group.
16 Suka zo wurin Bala’am suka ce, “Ga abin da Balak ɗan Ziffor ya ce, Kada ka bar wani abu yă hana ka zuwa wurina,
They came to Balaam and said to him, “Balak son of Zippor says this, 'Please let nothing stop you from coming to me,
17 gama zan ba ka lada mai yawa in kuma yi duk abin da ka ce. Ka zo ka la’anta mini waɗannan mutane.”
because I will pay you extremely well and give you great honor, and I will do whatever you tell me to do. So please come and curse this people for me.'”
18 Amma Bala’am ya amsa musu ya ce, “Ko da a ce Balak zai ba ni gidansa cike da azurfa da zinariya, ba zan yi wani abu ko kaɗan saɓanin umarnin Ubangiji Allahna ba.
Balaam answered and said to Balak's men, “Even if Balak would give me his palace full of silver and gold, I cannot go beyond the word of Yahweh, my God, and do less or more than what he tells me.
19 To, fa, sai ku kwana a nan kamar yadda waɗancan suka yi, ni kuma in roƙi Ubangiji, in ji, wace magana zai ce mini.”
Now then, please wait here tonight too, so that I may learn anything further that Yahweh says to me.”
20 A wannan dare, Allah ya zo wurin Bala’am ya ce, “Da yake waɗannan mutane sun zo su tafi da kai, to, ka tafi tare da su, sai dai ka yi abin da na ce ka yi ne kaɗai.”
God came to Balaam at night and said to him, “Since these men have come to summon you, get up and go with them. But only do what I tell you to do.”
21 Bala’am ya tashi da safe, ya ɗaura wa jakarsa sirdi, ya tafi tare da dattawan Mowab.
Balaam got up in the morning, saddled his donkey, and went with the leaders of Moab.
22 Amma Allah ya husata sa’ad da ya tafi, mala’ikan Ubangiji kuwa ya tsaya a hanya don yă hana shi. Bala’am kuwa yana kan jakarsa tare da bayinsa biyu.
But because he went, God's anger was kindled. The angel of Yahweh placed himself in the road as someone hostile to Balaam, who was riding on his donkey. Balaam's two servants were also with him.
23 Da jakar ta hangi mala’ikan Ubangiji tsaye a hanya da takobi a hannunsa, sai ta kauce daga hanya, ta shiga jeji. Bala’am kuwa ya buge ta don tă koma hanya.
The donkey saw the angel of Yahweh standing in the road with his drawn sword in his hand. The donkey turned off the road and went into a field. Balaam struck the donkey to turn her back to the road.
24 Sai mala’ikan Ubangiji ya tsaya a wata matsattsiyar hanya tsakanin gonaki inabi biyu, da bango a kowane gefe.
Then the angel of Yahweh stood in a narrow part of the road between some vineyards, with a wall on his right side and another wall on his left side.
25 Sa’ad da jakar ta ga mala’ikan Ubangiji, sai ta matse a jikin bango, ta goge ƙafar Bala’am da bangon. Saboda haka sai Bala’am ya sāke bugunta.
The donkey saw the angel of Yahweh again. She went against the wall and pinned Balaam's foot against it. Balaam struck her again.
26 Sai mala’ikan Ubangiji ya sha gabansa, ya tsaya a ƙunƙuntaccen wuri inda ba wurin juyawa dama ko hagu.
The angel of Yahweh went further and stood in another narrow place where there was no way to turn to either side.
27 Da jakar ta ga mala’ikan Ubangiji, sai ta kwanta a ƙasa, Bala’am kuwa ya husata, sai ya buge ta da sandansa.
The donkey saw the angel of Yahweh, and she lay down under Balaam. Balaam's anger was kindled, and he struck the donkey with his staff.
28 Ubangiji ya buɗe bakin jakar, sai jakar ta ce wa Bala’am, “Me na yi maka da ka buge ni har sau uku?”
Then Yahweh opened the donkey's mouth so she could talk. She said to Balaam, “What have I done to you that induced you to strike me these three times?”
29 Bala’am ya ce wa jakar “Domin kin wulaƙanta ni! Da a ce ina da takobi a hannuna da zan kashe ki nan take.”
Balaam replied to the donkey, “It was because you acted so stupidly with me. I wish there were a sword in my hand. If there were, by now I would have killed you.”
30 Jakar ta ce wa Bala’am, “Ni ba jakarka ba ce wadda kake hawa kullum, har yă zuwa yau? Na taɓa yin maka haka?” Bala’am ya ce, “A’a.”
The donkey said to Balaam, “Am not I your donkey on which you have ridden all your life long to this present day? Have I ever been in the habit of doing such things to you before?” Balaam said, “No.”
31 Sa’an nan Ubangiji ya buɗe idanun Bala’am, ya kuwa ga mala’ikan Ubangiji tsaye a hanya da takobi a zāre. Sai ya sunkuyar da kansa, ya fāɗi rubda ciki.
Then Yahweh opened Balaam's eyes, and he saw the angel of Yahweh standing in the road with his drawn sword in his hand. Balaam lowered his head and lay facedown.
32 Sa’an nan mala’ikan Ubangiji ya tambaye shi, “Don me ka buge jakarka har sau uku? Na fito ne don in hana ka, gama hanyarka ba daidai ba ce a gabana.
The angel of Yahweh said to him, “Why have you struck your donkey these three times? Look, I have come as someone hostile to you because your actions before me have been wicked.
33 Jakar ta gan ni, ta kauce mini har sau uku. Da a ce ba tă kauce ba, lalle da na kashe ka, in kuwa bar ta da rai.”
The donkey saw me and turned away from me these three times. If she had not turned away from me, I would certainly have killed you and spared her life.”
34 Bala’am ya ce wa mala’ikan Ubangiji, “Na yi zunubi. Ban san ka tsaya a hanya don ka hana ni ba. Yanzu in ba ka ji daɗin tafiyata, sai in koma.”
Balaam said to the angel of Yahweh, “I have sinned. I did not know that you stood against me in the road. So now, if it is displeasing to you, I will turn back.”
35 Mala’ikan Ubangiji ya ce wa Bala’am, “Ka tafi tare da mutanen, amma abin da na faɗa maka ne kaɗai za ka faɗa.” Saboda haka Bala’am ya tafi tare da dattawan Balak.
But the angel of Yahweh said to Balaam, “Go on ahead with the men. But you must only speak the words that I tell you.” So Balaam went with the leaders of Balak.
36 Da Balak ya ji cewa Bala’am yana zuwa, sai ya fito, ya tarye shi a garin Mowabawa da suke a iyakar Arnon, a ƙarshen yankinsa.
When Balak heard that Balaam had come, he went out to meet him at a city in Moab at the Arnon, which is on the border.
37 Balak ya ce wa Bala’am, “Ban aika maka saƙo cikin gagawa ba? Me ya sa ba ka zo ba? Ko ban isa in sāka maka ba ne?”
Balak said to Balaam, “Did I not send men to you to summon you? Why did you not come to me? Am I not able to honor you?”
38 Bala’am ya amsa ya ce, “To, ai, ga shi, na zo yanzu. Ina da wani ikon yin wata magana ne? Dole in faɗa abin da Allah ya ce in faɗa ne kawai.”
Then Balaam replied to Balak, “See, I have come to you. Do I now have any power to say anything? I can only say the words that God puts into my mouth.”
39 Sa’an nan Bala’am ya tafi tare da Balak zuwa Kiriyat-Huzot,
Balaam went with Balak, and they arrived at Kiriath Huzoth.
40 a can ya yi hadaya da shanu da tumaki, ya kuwa aika wa Bala’am da dattawan da suke tare da shi.
Then Balak sacrificed oxen and sheep and gave some meat to Balaam and the leaders who were with him.
41 Kashegari, Balak ya ɗauki Bala’am ya kai shi kan Bamot Ba’al, daga can ya iya ganin sassan sansanin Isra’ilawa.
In the morning, Balak took Balaam up to the high place of Baal. From there Balaam could see only a part of the Israelites in their camp.

< Ƙidaya 22 >