< Ƙidaya 21 >

1 Sa’ad da sarkin Arad, mutumin Kan’ana, wanda yake zaune a Negeb, da ya ji cewa Isra’ila yana zuwa ta hanyar Atarim, sai ya fito, yă yaƙi Isra’ilawa, yă kuma kama waɗansunsu.
When the Canaanite king of Arad, who lived in the Negev, heard that Israel was traveling by the road to Atharim, he fought against Israel and took some of them captive.
2 Sai Isra’ila suka yi alkawari wa Ubangiji suka ce, “In ka ba da waɗannan mutane a hannunmu, za mu hallaka dukan garuruwansu ƙaf.”
Israel vowed to Yahweh and said, “If you give us victory over these people, then we will completely destroy their cities.”
3 Ubangiji kuwa ya saurari kukan Isra’ila, ya kuma ba da Kan’aniyawa a gare su. Suka hallaka su da biranensu ƙaf; saboda haka aka sa wa wurin suna Horma.
Yahweh listened to Israel's voice and he gave them victory over the Canaanites. They completely destroyed them and their cities. That place was called Hormah.
4 Suka kama hanya daga Dutsen Hor ta hanya zuwa Jan Teku, don su kauce wa Edom. Amma mutane suka rasa haƙuri a hanya;
They traveled from Mount Hor by the road to the Sea of Reeds to go around the land of Edom. The people became very discouraged on the way.
5 suka yi wa Allah da Musa gunaguni, suka ce, “Me ya sa kuka fitar da mu daga Masar, kuka kawo mu mu mutu a wannan hamada? Babu abinci! Babu ruwa! Mu dai mun gaji da wannan abinci marar amfani!”
The people spoke against God and Moses: “Why have you brought us up out of Egypt to die in the wilderness? There is no bread, no water, and we hate this miserable food.”
6 Sai Ubangiji ya aiko da macizai masu dafin a cikinsu, suka sassari mutane, Isra’ilawa masu yawa kuwa suka mutu.
Then Yahweh sent poisonous snakes among the people. The snakes bit the people; many people died.
7 Mutanen suka zo wurin Musa, suka ce, “Mun yi zunubi, da muka yi wa Ubangiji da kai gunaguni. Ka yi addu’a don Ubangiji yă ɗauke mana macizan nan.” Saboda haka Musa ya yi addu’a domin mutane.
The people came to Moses and said, “We have sinned because we have spoken against Yahweh and you. Pray to Yahweh for him to take the snakes away from us.” So Moses prayed for the people.
8 Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ƙera siffar maciji ka rataye shi a bisa doguwar sanda; kowa da maciji ya sare shi, idan ya dubi macijin nan da ka rataye, zai rayu.”
Yahweh said to Moses, “Make a snake and attach it to a pole. It will happen that everyone who is bitten will survive, if he looks at it.”
9 Saboda haka Musa ya ƙera macijin tagulla, ya kuma rataye shi bisa doguwar sanda. Sa’an nan duk wanda maciji ya sare shi, ya kuma dubi macijin tagullar, zai warke.
So Moses made a bronze snake and attached it to a pole. When a snake bit any person, if he looked at the bronze snake, he survived.
10 Isra’ilawa suka kama hanya, suka yi sansani a Obot.
Then the people of Israel traveled on and camped at Oboth.
11 Sai suka tashi daga Obot, suka yi sansani a Iye Abarim a hamadar da take fuskantar Mowab, wajen fitowar rana.
They traveled from Oboth and camped at Iye Abarim in the wilderness that faces Moab toward the east.
12 Daga nan kuma suka ci gaba, suka yi sansani a Kwarin Zered.
From there they traveled on and camped in the Valley of Zered.
13 Suka tashi daga nan, suka sauka kusa da Arnon wanda yake a hamadar da ta miƙe zuwa iyakar Amoriyawa. Arnon shi ne iyakar Mowab, wanda yake tsakanin Mowab da Amoriyawa.
From there they traveled on and camped on the other side of the Arnon River, which is in the wilderness that extends from the border of the Amorites. The Arnon River forms the border of Moab, between Moab and the Amorites.
14 Shi ya sa Littafin Yaƙoƙin Ubangiji ya ce, “Waheb ta cikin yankin Sufa, da kwaruruka na tuddan Arnon,
That is why it says in the scroll of the Wars of Yahweh, “... Waheb in Suphah, and the valleys of the Arnon,
15 da gangaren kwaruruka, wanda ya nausa zuwa garin Ar, ya kuma dangana da kan iyakar Mowab.”
the slope of the valleys that lead toward the town of Ar and lie along the border of Moab.”
16 Daga can, suka gangara zuwa Beyer, wato, rijiyar da Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka tattara mutane duka, zan kuwa ba su ruwa.”
From there they traveled to Beer, the well where Yahweh said to Moses, “Gather the people together for me to give them water.”
17 Sai Isra’ilawa suka rera wannan waƙa, “Ki ɓuɓɓugo da ruwa, Ke rijiya! Rera waƙa game da ita,
Then Israel sang this song: “Spring up, well! Sing about it,
18 game da rijiyar da’ya’yan sarki suka haƙa, rijiyar da manyan mutane masu sandunan sarauta suka nuna da sandunansu.” Sa’an nan suka tashi daga hamadar, suka tafi Mattana,
about the well that our leaders dug, the well the nobles of the people dug, with the scepter and their staffs.” Then from the wilderness they traveled to Mattanah.
19 daga Mattana, suka tafi Nahaliyel, daga Nahaliyel, suka tafi Bamot,
From Mattanah they traveled to Nahaliel, and from Nahaliel to Bamoth,
20 daga Bamot kuma suka tafi kwarin da yake cikin Mowab inda ƙwanƙolin Fisga yake fuskantar hamada.
and from Bamoth to a valley in the land of Moab. That is where the top of Mount Pisgah looks down on the wilderness.
21 Isra’ila suka aiki manzanni wurin Sihon sarkin Amoriyawa su ce,
Then Israel sent messengers to Sihon king of the Amorites saying,
22 “Ka bari mu ratsa ta ƙasarka. Ba za mu shiga wata gona ba, ba za mu kuma shiga gonar inabi, ko mu sha ruwa daga wata rijiya ba. Za mu bi ta babbar hanyar sarki, har mu fita ƙasarka.”
“Let us pass through your land. We will not turn into any field or vineyard. We will not drink the water from your wells. We will travel by the king's highway until we have crossed your border.”
23 Amma Sihon bai bar Isra’ila su ratsa ta yankinsa ba. Sai ya tara dukan sojojinsa, suka fita zuwa cikin hamada, su yaƙi Isra’ila. Da ya kai Yahaz, sai ya yaƙi Isra’ila.
But King Sihon would not allow Israel to pass through their border. Instead, Sihon gathered all his army together and attacked Israel in the wilderness. He came to Jahaz, where he fought against Israel.
24 Isra’ila fa suka kashe shi da takobi, suka ƙwace ƙasarsa, tun daga kogin Arnon har zuwa kogin Yabbok, zuwa kan iyakar Ammonawa kawai, gama sun yi wa iyakansu katanga.
Israel attacked the army of Sihon with the edge of the sword and took their land from the Arnon to the Jabbok river, as far as the land of the people of Ammon. Now the border of the people of Ammon was fortified.
25 Isra’ila suka ci dukan biranen Amoriyawa, suka kuma zauna a cikinsu, haɗe da babban birnin Heshbon da dukan ƙauyukanta.
Israel took all the Amorite cities and lived in all of them, including Heshbon and all of its villages.
26 Sihon sarkin Amoriyawa ya yi mulkin Heshbon, bayan ya ci sarkin Mowab na dā da yaƙi, ya kuma ƙwace dukan ƙasarsa har zuwa arewancin kogin Arnon.
Heshbon was the city of Sihon king of the Amorites, who had fought against the former king of Moab. Sihon had taken all his land from his territory to the Arnon River.
27 Shi ya sa Amoriyawa suka rubuta wannan waƙa game da Heshbon suka ce, “Ku zo mu sāke gina Heshbon, birnin Sihon.
That is why those who speak in proverbs say, “Come to Heshbon. Let the city of Sihon be rebuilt and established again.
28 “Mayaƙansa sun fito kamar harshen wuta suka ƙone birnin Ar na Mowab suna hallaka’yan ƙasar tuddan Arnon.
A fire blazed from Heshbon, a flame from the city of Sihon that devoured Ar of Moab, and the owners of the high places of Arnon.
29 Kaitonki, Mowab! Gunkinki Kemosh ya yashe mutanenki; aka kuma kama su, aka kai su bauta wajen Sihon sarkin Amoriyawa.
Woe to you, Moab! You have perished, people of Chemosh. He has made his sons to be fugitives and his daughters to be prisoners of Sihon king of the Amorites.
30 “Amma mun tumɓuke su, mun hallaka garuruwan Heshbon har zuwa Dibon. Mun ragargaza su har zuwa Nofa wanda ya miƙe zuwa Medeba.”
But we have conquered Sihon. Heshbon is devastated all the way to Dibon. We have defeated them all the way to Nophah, which reaches to Medeba.”
31 Ta haka Isra’ila suka zauna a ƙasar Amoriyawa.
So Israel began to live in the Amorites' land.
32 Sai Musa ya aika’yan leƙen asiri zuwa Yazer. Daga baya, sai Isra’ilawa suka ci ƙauyukan da suke kewaye, suka kuma kori Amoriyawa da suke zaune a can.
Then Moses sent men to look at Jazer. They took its villages and drove out the Amorites who were there.
33 Sai suka juya suka haura kan hanya ta zuwa Bashan, inda Og yake sarauta, ya kuwa fito tare da dukan sojojinsa suka yi yaƙi da Isra’ila a Edireyi.
Then they turned and went up by the road of Bashan. Og king of Bashan went out against them, he and all his army, to fight them at Edrei.
34 Ubangiji ya ce wa Musa, “Kada ka ji tsoronsa, gama na ba da shi a gare ka, da dukan sojojinsa da kuma ƙasarsa. Ka yi da shi yadda ka yi da Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulki a Heshbon.”
Then Yahweh said to Moses, “Do not fear him, because I have given you victory over him, all his army, and his land. Do to him as you did to Sihon king of the Amorites, who lived at Heshbon.”
35 Ta haka suka kashe shi, tare da’ya’yansa maza da kuma dukan sojojinsa, ba wanda ya ragu. Suka kuma mamaye ƙasarsa.
So they killed him, his sons, and all his army, until none of his people were left alive. Then they took over his land.

< Ƙidaya 21 >