< Maimaitawar Shari’a 1 >

1 Waɗannan su ne kalmomin da Musa ya yi wa dukan Isra’ila, a hamada gabas da Urdun, wato, Araba, ɗaura da Suf, tsakanin Faran da Tofel, Laban, Hazerot da Dizahab.
These are the words that Moses spoke to all Israel beyond the Jordan in the wilderness, in the plain of the Jordan River valley over against Suph, between Paran, Tophel, Laban, Hazeroth, and Dizahab.
2 (Yakan ɗauki kwana goma sha ɗaya daga Horeb zuwa Kadesh Barneya ta hanyar Dutsen Seyir.)
It is eleven days' journey from Horeb by the way of Mount Seir to Kadesh Barnea.
3 A shekara ta arba’in, a rana ta fari ga wata na goma sha ɗaya, Musa ya yi shela ga Isra’ilawa game da dukan abin da Ubangiji ya umarta shi game da su.
It happened in the fortieth year, in the eleventh month, on the first day of the month, that Moses spoke to the people of Israel, telling them all that Yahweh commanded him concerning them.
4 Wannan ya faru bayan ya ci Sihon sarkin Amoriyawa wanda ya yi mulki a Heshbon da yaƙi. A Edireyi kuma ya ci Og sarkin Bashan wanda ya yi mulki a Ashtarot da yaƙi.
This was after Yahweh had attacked Sihon the king of the Amorites, who lived in Heshbon, and Og the king of Bashan, who lived in Ashtaroth at Edrei.
5 Gabas da iyakar Mowab, Musa ya fara bayyana wannan doka, yana cewa,
Beyond the Jordan, in the land of Moab, Moses began to announce these instructions, saying,
6 Ubangiji Allahnmu ya faɗa mana a Horeb cewa, “Daɗewarku a wannan dutse ya isa haka.
“Yahweh our God spoke to us at Horeb, saying, 'You have lived long enough in this hill country.
7 Ku tashi, ku ci gaba zuwa ƙasar tudun Amoriyawa; ku tafi wurin dukan maƙwabta a cikin Araba, a cikin duwatsu, a gindin yammancin tuddai, a Negeb da kuma a ta kwaruruka, da ƙasar Kan’aniyawa da kuma zuwa Lebanon, har zuwa babban kogi, wato, Yuferites.
Turn and take your journey, and go to the hill country of the Amorites and to all the places near there in the plain of the Jordan River valley, in the hill country, in the lowland, in the Negev, and by the seashore—the land of the Canaanites, and in Lebanon as far as the great river, the Euphrates.
8 Duba na riga na ba ku wannan ƙasa. Ku shiga ku mallaki ƙasar da Ubangiji ya rantse zai ba wa kakanninku, ga Ibrahim, Ishaku da kuma Yaƙub, da kuma ga zuriyarsu bayansu.”
Look, I have set the land before you; go in and possess the land that Yahweh swore to your fathers—to Abraham, to Isaac, and to Jacob—to give to them and to their descendants after them.'
9 A wancan lokaci na faɗa muku cewa, “Ku kaya ne masu nauyi da ni kaɗai ba zan iya ɗauka ba.
I spoke to you at that time, saying, 'I am not able to carry you myself alone.
10 Ubangiji Allahnku ya ƙara yawanku har yau kuka zama da yawa kamar taurari a sarari.
Yahweh your God has multiplied you, and, look, you are today as the multitude of the stars of heaven.
11 Bari Ubangiji, Allahn kakanninku yă ƙara yawanku sau dubu, yă kuma albarkace ku yadda ya yi alkawari!
May Yahweh, the God of your fathers, make you a thousand times as many as you are, and bless you, as he has promised you!
12 Amma yaya zan ɗauka dukan damuwoyinku da nawayarku da kuma faɗace-faɗacenku duka ni kaɗai?
But how can I myself alone carry your loads, your burdens, and your disputes?
13 Ku zaɓi waɗansu masu hikima, masu ganewa, da kuma mutanen da ake girmama daga kowace kabilarku, zan kuma sa su a kanku.”
Take wise men, understanding men, and men of good repute from each tribe, and I will make them heads over you.'
14 Kuka amsa mini, kuka ce, “Abin da ka ce za ka yi, yana da kyau.”
You answered me and said, 'The thing that you have spoken is good for us to do.'
15 Saboda haka na ɗauko shugabannin kabilanku masu hikima, waɗanda suka saba da ma’amala da jama’a, na sa su shugabanni a gabanku, waɗansu suka zama shugabanni a kan dubu-dubu, waɗansu a kan ɗari-ɗari, waɗansu a kan hamsin-hamsin, waɗansu kuma a kan goma-goma. Na sa su zama shugabanni a kabilanku.
So I took the heads of your tribes, wise men, and men of good repute, and made them heads over you, captains of thousands, captains of hundreds, captains of fifties, captains of tens, and officers, tribe by tribe.
16 Na kuma umarci alƙalanku a wancan lokaci, na ce, “Ku yi adalci cikin shari’a tsakanin’yan’uwanku, ko damuwar tana tsakanin’yan’uwa Isra’ilawa ne, ko kuwa tsakanin Isra’ilawa da baƙin da suke zaune a cikinku.
I commanded your judges at that time, saying, 'Hear the disputes between your brothers, and judge righteously between a man and his brother, and the foreigner who is with him.
17 Kada ku nuna sonkai a cikin hukuncinku, ku saurari kowane ɓangare, babba da ƙarami, kada ku ji tsoron wani, gama hukunci na Allah ne. Ku kawo kowane batun da ya sha ƙarfinku, zan kuwa saurare shi.”
You will not show partiality to anyone in a dispute; you will hear the small and the great alike. You will not be afraid of the face of man, for the judgment is God's. The dispute that is too hard for you, you will bring to me, and I will hear it.'
18 A wancan lokacin kuwa na faɗa muku dukan abin da ya kamata ku yi.
I commanded you at that time all the things that you should do.
19 Sa’an nan, muka kama hanya daga Horeb muka ratsa wajen ƙasar tudun Amoriyawa ta dukan hamadarta mai fāɗi, da kuma mai bantsoron da kuka gani, muka kuma kai Kadesh Barneya yadda Ubangiji, Allahnmu ya umarce mu.
We journeyed away from Horeb and went through all that great and terrible wilderness that you saw, on our way to the hill country of the Amorites, as Yahweh our God had commanded us; and we came to Kadesh Barnea.
20 Sai na ce muku, “Kun iso ƙasar tudun Amoriyawa, wadda Ubangiji, Allahnmu yake ba mu.
I said to you, 'You have come to the hill country of the Amorites, which Yahweh our God is giving to us.
21 Duba, Ubangiji Allahnku ya ba ku ƙasar. Ku haura ku mallake ta yadda Ubangiji Allahn kakanninku ya faɗa muku. Kada ku ji tsoro, kada ku fid da zuciya.”
Look, Yahweh your God has set the land before you; go up, take possession, as Yahweh, the God of your fathers, has spoken to you; do not be afraid, neither be discouraged.'
22 Sai dukanku kuka zo wurina kuka ce, “Bari mu aiki mutane su yi gaba su leƙi mana asirin ƙasar, su kuma kawo mana labari game da hanyar da za mu bi, da kuma biranen da za mu shiga.”
Every one of you came to me and said, 'Let us send men ahead of us, so that they may search out the land for us, and bring us word about the way by which we should attack, and about the cities to which we will come.'
23 Ra’ayin nan naku ya yi mini kyau, saboda haka na zaɓe ku goma sha biyu, mutum guda daga kowace kabila.
The advice pleased me well; I took twelve men of you, one man for every tribe.
24 Suka tafi, suka haura zuwa ƙasar tudu, suka kai Kwarin Eshkol, suka leƙo asirin ƙasar.
They turned and went up into the hill country, came to the Valley of Eshkol, and scouted it.
25 Suka ɗebi’ya’yan itatuwan ƙasar, suka sauko mana da su, suka kuma ba da labari cewa, “Ƙasar da Ubangiji Allahnmu yake ba mu, kyakkyawa ce.”
They took some of the produce of the land in their hands and brought it down to us. They also brought us word and said, 'It is a good land that Yahweh our God is giving to us.'
26 Amma ba ku yi niyya ku haura ba, kuka yi tawaye gāba da umarnin Ubangiji Allahnku.
Yet you refused to attack, but rebelled against the commandment of Yahweh your God.
27 Kuka yi gunaguni a cikin tentunanku, kuna cewa, “Ubangiji ya ƙi mu; shi ya sa ya fitar da mu daga Masar don yă ba da mu ga hannuwan Amoriyawa su hallaka mu.
You complained in your tents and said, “It is because Yahweh hated us that he has brought us out of the land of Egypt, to give us into the hand of the Amorites to destroy us.
28 Ina za mu?’Yan’uwanmu suka sa muka fid da zuciya. Suka ce, ‘Mutanen sun fi mu ƙarfi, sun kuma fi mu tsayi; biranen manya ne, da katanga har sama. Mun ma ga Anakawa a can.’”
Where can we go now? Our brothers have made our heart to melt, saying, 'Those people are bigger and taller than we are; their cities are large and are fortified up to the heavens; moreover, we have seen the sons of the Anakim there.'”
29 Sai na ce muku, “Kada ku firgita; kada ku ji tsoronsu.
Then I said to you, 'Do not be terrified, neither be afraid of them.
30 Ubangiji Allahnku yana a gabanku, zai yi yaƙi saboda ku, kamar yadda ya yi a kan idanunku a Masar,
Yahweh your God, who goes before you, he will fight for you, like everything that he did for you in Egypt before your eyes,
31 da kuma a cikin hamada. A can ma kun ga yadda Ubangiji Allahnku ya riƙe ku ko’ina da kuka tafi, kamar yadda mahaifi yakan riƙe ɗansa, sai da kuka kai wannan wuri.”
and also in the wilderness, where you have seen how Yahweh your God carried you, as a man carries his son, everywhere you went until you came to this place.'
32 Duk da haka, ba ku amince da Ubangiji Allahnku ba,
Yet in spite of this word you did not believe Yahweh your God,
33 shi da ya sha gabanku a tafiyarku, cikin wuta da dad dare da kuma girgije da rana, don yă nemi wurare domin ku kafa sansani, don kuma yă nuna muku hanyar da za ku bi.
who went before you on the way to find a place for you to make camp, in fire by night and in a cloud by day.
34 Da Ubangiji ya ji abin da kuka faɗa, sai ya husata, ya kuma yi rantsuwa ya ce,
Yahweh heard the sound of your words and was angry; he swore and said,
35 “Babu wani a cikin wannan muguwar tsara da zai ga ƙasa mai kyau da na rantse zan ba wa kakanninku,
'Surely not one of these men of this evil generation will see the good land that I swore to give to your ancestors,
36 sai dai Kaleb ɗan Yefunne. Zai gan ta, zan ba shi duk ƙasar da tafin ƙafarsa ta taka, shi da zuriyarsa, gama ya bi Ubangiji da zuciya ɗaya.”
save Caleb son of Jephunneh; he will see it. To him I will give the land that he has stepped on, and to his children, because he has wholly followed Yahweh.'
37 Saboda ku Ubangiji ya husata da ni, ya kuma ce, “Kai ma, ba za ka shiga ƙasar ba.
Also Yahweh was angry with me because of you, saying, 'You also will not go in there;
38 Amma mataimakinka, Yoshuwa ɗan Nun, zai shiga. Ka ƙarfafa shi gama shi ne zai jagoranci Isra’ila su gāje ta.
Joshua son of Nun, who stands before you, he will go in there; encourage him, for he will lead Israel to inherit it.
39 Amma’ya’yanku ƙanana waɗanda ba su san mugunta ko nagarta ba, waɗanda kuke tsammani za a kwashe su ganima, su za su shiga ƙasar. Zan ba da ita gare su, za su kuwa mallake ta.
Moreover, your little children, the ones you said would be victims, who today have no knowledge of good or evil—they will go in there. To them I will give it, and they will possess it.
40 Amma ku kam, sai ku juya, ku koma cikin hamada ta hanyar Jan Teku.”
But as for you, turn and take your journey into the wilderness along the way to the Sea of Reeds.'
41 Sai kuka amsa, kuka ce, “Mun yi zunubi ga Ubangiji. Za mu haura mu yi yaƙi yadda Ubangiji Allahnmu ya umarce mu.” Saboda haka kowannenku ya yi ɗamara da kayan yaƙinsa, kuka yi tsammani zai zama muku da sauƙi ku ci ƙasar tuddai da yaƙi.
Then you answered and said to me, 'We have sinned against Yahweh; we will go up and fight, and we will follow all that Yahweh our God has commanded us to do.' Every man among you put on his weapons of war, and you were ready to attack the hill country.
42 Amma Ubangiji ya ce mini, “In faɗa muku, ‘Kada ku fāɗa musu da yaƙi, gama ba zai kasance tare da ku ba. Idan kuka kuskura, abokan gābanku za su murƙushe ku.’”
Yahweh said to me, 'Say to them, “Do not attack and do not fight, for I will not be with you, and you will be defeated by your enemies.'
43 Sai na faɗa muku, amma ba ku saurara ba. Kuka yi tawaye ga umarnin Ubangiji, a cikin jahilcinku kuwa kuka taka, kuka haura cikin ƙasar tudu.
I spoke to you in this way, but you did not listen. You rebelled against the commandment of Yahweh; you were arrogant and attacked the hill country.
44 Amoriyawan da suke zama a waɗannan tuddai, suka fito kamar tarin ƙudan zuma gāba da ku, suka kore ku, suka fatattake ku daga Seyir har zuwa Horma.
But the Amorites, who lived in that hill country, came out against you and chased you like bees, and struck you down in Seir, as far as Hormah.
45 Kuka dawo, kuka yi kuka a gaban Ubangiji, amma bai kula da ku ba, balle yă saurare ku.
You returned and wept before Yahweh; but Yahweh did not listen to your voice, nor did he pay attention to you.
46 Haka kuwa kuka zauna a Kadesh kwanaki masu yawa, kuka ci lokaci a can.
So you stayed in Kadesh many days, all the days that you stayed there.

< Maimaitawar Shari’a 1 >