< Luka 21 >

1 Da Yesu ya ɗaga ido, sai ya ga waɗansu masu arziki suna sa baikonsu a ma’ajin haikalin.
In pogledal je navzgor in videl bogataše metati svoje darove v zakladnico.
2 Ya kuma ga wata gwauruwa matalauciya, ta saka anini biyu.
Videl pa je tudi neko siromašno vdovo vreči vanjo dva kovanca.
3 Sai ya ce, “Gaskiya ina faɗa muku, wacce nan gwauruwa matalauciya ta sa fiye da dukan sauran.
In rekel je: »Resnično, jaz vam pravim, da je ta siromašna vdova vrgla vanjo več kot vsi,
4 Dukan mutanen nan sun ba da baikonsu daga cikin arzikinsu ne, amma ita daga cikin talaucinta, ta saka duk abin da take da shi na rayuwa.”
kajti vsi ti so iz svojega obilja vrgli vanjo daritve Bogu, toda ona je iz svojega uboštva vrgla vanjo vsa sredstva za preživljanje, ki jih je imela.«
5 Waɗansu daga cikin almajiransa, suka fara magana a kan yadda aka yi wa haikalin ado da duwatsu masu kyau, da kuma kyautai da aka keɓe wa Allah. Amma Yesu ya ce,
In ko so nekateri govorili o templju, kako je okrašen z lepimi kamni in darovi, je rekel:
6 “Wannan abin da kuke kallo a nan, lokaci yana zuwa da ba za a bar wani dutse a kan wani dutse ba. Kowannensu, za a rushe shi.”
» Glede teh stvari, ki jih gledate, pa bodo prišli dnevi, v katerih ne bo ostal en kamen na drugem, ki ne bi bil zrušen.«
7 Suka tambaye shi suka ce, “Malam, yaushe waɗannan za su faru? Kuma wace alama za tă nuna cewa suna dab da faruwa?”
In vprašali so ga, rekoč: »Učitelj, toda kdaj bodo te stvari? In kakšno znamenje se bo zgodilo, ko se bodo te stvari pripetile?«
8 Ya amsa ya ce, “Ku lura, kada ku kuma a ruɗe ku. Gama da yawa za su zo a cikin sunana, suna cewa, ‘Ai, ni ne shi,’ da kuma, ‘Lokaci ya yi kusa.’ Kada ku bi su.
In rekel je: »Pazite, da ne boste zavedeni, kajti mnogi bodo prišli v mojem imenu, rekoč: ›Jaz sem Kristus in čas se je približal; ‹ ne pojdite torej za njimi.
9 Sa’ad da kuka ji labarin yaƙe-yaƙe, da juye juyen mulki, kada ku tsorota. Dole ne waɗannan abubuwa su fara faruwa, amma ƙarshen ba zai zo nan da nan ba.”
Toda ko boste slišali o vojnah in vstajah, ne bodite prestrašeni, kajti te stvari se morajo najprej zgoditi, toda konec še ni v kratkem.«
10 Sai ya ce musu, “Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki zai tasar wa mulki.
Tedaj jim je rekel: »Narod bo vstal zoper narod in kraljestvo zoper kraljestvo
11 Za a yi manyan girgizar ƙasa, da yunwa, da annoba a wurare dabam-dabam, da kuma abubuwa masu bantsoro, da manyan alamu daga sama.
in veliki potresi bodo na raznih krajih in lakote ter kužne bolezni in strašni prizori ter velika znamenja se bodo zgodila z neba.
12 “Amma kafin duk abubuwa nan, za a kama ku a tsananta muku. Za a kai ku majami’u, da kurkuku. Za a kuma kai ku gaban sarakuna da gwamnoni, kuma dukan waɗannan saboda sunana.
Toda pred vsem tem bodo nad vas iztegovali svoje roke in vas preganjali ter vas izročali v shodnice in ječe [in] zaradi mojega imena boste privedeni pred kralje in vladarje.
13 Wannan zai sa ku zama shaidu a gare su.
To pa se bo obrnilo k vam za pričevanje.
14 Amma ku yi ƙuduri, wato, ku shirya zuciyarku, a kan ba za ku damu ba kafin lokacin, game da yadda za ku kāre kanku.
Pomirite se torej v svojih srcih, da ne boste prej premišljevali, kaj boste odgovorili,
15 Gama zan ba ku kalmomi, da hikima waɗanda ba ko ɗaya daga cikin maƙiyanku, za su iya tsayayya da ku, ko su ƙaryata.
kajti jaz vam bom dal usta in modrost, kateri vsi vaši nasprotniki ne bodo mogli ugovarjati niti se ji upirati.
16 Har iyayenku, da’yan’uwanku maza, da danginku, da abokanku ma, duk za su bashe ku, su kuma kashe waɗansunku.
Izdajali pa vas bodo tako starši kakor bratje, žlahta in prijatelji in nekaterim izmed vas bodo povzročili, da boste usmrčeni.
17 Duk mutane za su ƙi ku saboda ni.
In vsi ljudje vas bodo sovražili zaradi mojega imena.
18 Amma ko gashi ɗaya na kanku, ba zai hallaka ba.
Toda niti las z vaše glave ne bo propadel.
19 Ta wurin tsayawa da ƙarfi, za ku sami rai.
S svojim potrpljenjem si pridobivate svoje duše.
20 “In kuka ga mayaƙa sun kewaye Urushalima, za ku sani rushewarta ya yi kusa.
In ko boste videli Jeruzalem obdan z vojskami, tedaj vedite, da je blizu opustošenje le-tega.
21 A lokacin nan, bari waɗanda suke Yahudiya, su gudu zuwa cikin duwatsu. Bari waɗanda suke cikin birnin kuma su fita, bari kuma waɗanda suke ƙauye kada su shiga birnin.
Potem naj tisti, ki so v Judeji, pobegnejo v gore; in naj tisti, ki so v njegovi sredi, odidejo ven; in naj tisti, ki so na podeželju, ne vstopijo vanj.
22 Gama wannan shi ne lokacin hukunci, saboda a cika duk abin da aka rubuta.
Kajti to so dnevi maščevanja, da se bodo lahko izpolnile vse stvari, ki so napisane.
23 Zai zama abin kaito ga mata masu ciki, da mata masu renon’ya’ya, a waɗancan kwanakin! Za a yi baƙin ciki mai tsanani a ƙasar, da kuma fushi mai tsanani a kan mutanen nan.
Toda gorje v tistih dneh tem, ki so z otrokom in tem, ki dojijo! Kajti v deželi bo velika tegoba in bes nad temi ljudmi.
24 Za a kashe su da takobi, a kuma ɗauke su’yan kurkuku, zuwa dukan al’ummai. Al’ummai za su tattaka Urushalima, har sai lokacin Al’ummai ya cika.
In padali bodo pod ostrino meča in odvedeni bodo v ujetništvo med vse narode in Jeruzalem bodo mendrali pogani, dokler se ne dopolnijo časi poganov.
25 “Za a yi alamu a cikin rana, da cikin wata, da cikin taurari. A duniya, al’ummai za su yi baƙin ciki, su kuma rikice don tsoro, saboda ruri da kuma tafasar teku.
In znamenja bodo na soncu in na luni in na zvezdah; in nad zemljo tegoba narodov z zmedenostjo; morje in valovi bodo rjoveli;
26 Mutane za su suma don tsoro, za su kuma yi fargaba, a kan abin da yake zuwa a bisan duniya, gama za a girgiza duniyar taurarin sararin sama.
srca bodo ljudem odpovedovala zaradi strahu in zaradi opazovanja za temi stvarmi, ki prihajajo na zemljo, kajti moči neba se bodo majale.
27 A lokacin ne za su ga Ɗan Mutum yana zuwa cikin girgije, da iko, da ɗaukaka mai girma.
In tedaj bodo videli Sina človekovega prihajati v oblaku z močjo in veliko slavo.
28 Sa’ad da waɗannan abubuwa sun fara faruwa, ku tashi tsaye, ku ɗaga kawunanku, domin fansarku yana matsowa kusa.”
Ko pa se bodo te stvari začele dogajati, potem poglejte gor in dvignite svoje glave, kajti vaša odkupitev se približuje.«
29 Sai ya gaya musu wannan misali ya ce, “Ku dubi itacen ɓaure da dukan itatuwa.
In spregovoril jim je v prispodobi: »Poglejte figovo drevo in vsa drevesa;
30 A duk lokacin da sun fara fitar da ganye, za ku gani da kanku, ku san cewa, damina ta yi kusa.
ko sedaj poganjajo, vi vidite in sami veste, da je torej poletje blizu.
31 Haka ma, in kuka ga waɗannan abubuwa suna faruwa, ku sani mulkin Allah ya yi kusa.
Tako tudi vi, ko vidite, da se te stvari dogajajo, védite, da je Božje kraljestvo blizu.
32 “Gaskiya nake gaya muku, ba shakka, wannan zamani ba zai shuɗe ba, sai dukan waɗannan abubuwa sun cika.
Resnično, povem vam: ›Ta rod ne bo preminil, dokler ne bo vse izpolnjeno.
33 Sama da ƙasa za su shuɗe, amma kalmomina ba za su taɓa shuɗewa ba.
Nebo in zemlja bosta minila, toda moje besede ne bodo minile.
34 “Ku lura fa don kada son jin daɗi na banza, da shaye-shaye, da damuwa na rayuwa su rinjayi zuciyarku, har ranar ta auko muku ba tsammani kamar tarko.
Pazite pa se, da ne bi bila vaša srca kadarkoli preobremenjena s prenasičenostjo in pijanostjo in skrbmi tega življenja in tako, da ta dan nad vas ne pride nepričakovano.
35 Gama za tă zo a kan kowa da yake kan dukan duniya.
Kajti kakor zanka bo prišel na vse tiste, ki prebivajo na obličju celotne zemlje.
36 Ku yi tsaro kullum, ku yi addu’a don ku iya kuɓuta daga dukan waɗannan abubuwa da suke kusan faruwa, don ku iya tsayawa a gaban Ɗan Mutum.”
Čujte torej in nenehno molíte, da boste lahko šteti za vredne, da pobegnete vsem tem stvarem, ki se bodo pripetile in stopite pred Sina človekovega.‹«
37 Kowace rana, Yesu yakan je haikalin ya yi koyarwa, da kowace yamma kuma, ya je ya kwana a kan tudun da ake kira Dutsen Zaitun.
In podnevi je učil v templju, ponoči pa je odšel ven ter prebival na gori, ki se imenuje Oljska gora.
38 Da sassafe kuma, dukan mutanen suka zo haikalin, don su saurare shi.
In vsi ljudje so prihajali zgodaj zjutraj k njemu v tempelj, da bi ga poslušali.

< Luka 21 >