< Yohanna 1 >

1 Tun farar farawa akwai Kalma, Kalman kuwa yana nan tare da Allah, Kalman kuwa Allah ne.
V začetku je bila Beseda in Beseda je bila z Bogom in Beseda je bila Bog.
2 Yana nan tare da Allah tun farar farawa.
Ista je bila v začetku z Bogom.
3 Ta wurin Kalman ne aka halicci dukan abubuwa. In ba tare da shi ba, babu abin da aka yi wanda aka yi.
Vse stvari so bile narejene po njem in brez njega ni bilo narejeno nič, kar je bilo narejeno.
4 A cikinsa rai ya kasance, wannan rai kuwa shi ne hasken mutane.
V njem je bilo življenje in življenje je bilo svetloba ljudem.
5 Hasken yana haskakawa cikin duhu, amma duhun bai rinjaye shi ba.
In svetloba sveti v temi, tema pa je ni doumela.
6 Akwai wani mutumin da aka aiko daga Allah; mai suna Yohanna.
Bil je človek, poslan od Boga, katerega ime je bilo Janez.
7 Ya zo a matsayin mai shaida domin yă ba da shaida game da wannan haske, don ta wurinsa dukan mutane su ba da gaskiya.
Ta isti je prišel za pričo, da pričuje o Svetlobi, da bodo vsi ljudje po njem lahko verovali.
8 Shi kansa ba shi ne hasken ba; sai dai ya zo a matsayin shaida ne kaɗai ga hasken.
Ni bil on ta Svetloba, ampak je bil poslan, da pričuje o tej Svetlobi.
9 Haske na gaskiya da yake ba da haske ga kowane mutum mai shigowa duniya.
To je bila resnična Svetloba, ki razsvetljuje vsakega človeka, ki prihaja na svet.
10 Yana a duniya, kuma ko da yake an yi duniya ta wurinsa ne, duniya ba tă gane shi ba.
Bil je na svetu in svet je bil narejen po njem, svet pa ga ni spoznal.
11 Ya zo wurin abin da yake nasa, amma nasa ɗin ba su karɓe shi ba.
Prišel je k svojim lastnim, njegovi lastni pa ga niso sprejeli.
12 Duk da haka dukan waɗanda suka karɓe shi, ga waɗanda suka gaskata a sunansa, ya ba su iko su zama’ya’yan Allah
Toda tolikim, kot so ga sprejeli, njim je on dal moč, da postanejo Božji sinovi, torej njim, ki verujejo v njegovo ime,
13 ’ya’yan da aka haifa ba bisa hanyar’yan adam, ko shawarar mutum ko nufin namiji ba, sai dai haifaffu bisa ga nufin Allah.
ki so bili rojeni, ne iz krvi niti ne iz volje mesa niti ne iz volje moža, temveč iz Boga.
14 Kalman ya zama mutum, ya kuwa zauna a cikinmu. Muka ga ɗaukakarsa, ɗaukaka ta wanda yake Ɗaya kuma Makaɗaici, wanda ya zo daga wurin Uba, cike da alheri da gaskiya.
In Beseda je bila narejena meso in prebivala med nami (in zagledali smo njegovo slavo, slavo kot od edinorojenega od Očeta) polno milosti in resnice.
15 (Yohanna ya ba da shaida game da shi. Ya ɗaga murya yana cewa, “Wannan shi ne wanda na ce, ‘Mai zuwa bayana ya fi ni girma domin yana nan kafin ni.’”)
Janez je pričeval o njem in klical, rekoč: »Ta je bil tisti, o katerem sem govoril: ›Kdor prihaja za menoj, je obstajal pred menoj, kajti bil je prej kakor jaz.‹«
16 Daga yalwar alherinsa dukanmu muka sami albarka bisa albarka.
In iz njegove polnosti smo vsi prejeli in to milost za milostjo.
17 Gama an ba da doka ta wurin Musa; alheri da gaskiya kuwa sun zo ne ta wurin Yesu Kiristi.
Kajti postava je bila dana po Mojzesu, toda milost in resnica sta prišli po Jezusu Kristusu.
18 Ba wanda ya taɓa ganin Allah, sai dai Allah da yake Ɗaya da kuma Makaɗaici wanda yake a gefen Uba, shi ne ya bayyana shi.
Noben človek nikoli ni videl Boga. Edinorojeni Sin, ki je v Očetovem naročju, on ga je razodel.
19 To, ga shaidar Yohanna sa’ad da Yahudawan Urushalima suka aiki firistoci da Lawiyawa su tambaye shi ko shi wane ne.
In to je Janezovo pričevanje, ko so Judje poslali iz Jeruzalema duhovnike in Lévijevce, da ga vprašajo: »Kdo si ti?«
20 Bai yi mūsu ba, amma ya shaida a fili cewa, “Ba ni ne Kiristi ba.”
In priznal je in ni zanikal, temveč priznal: »Jaz nisem Kristus.«
21 Sai suka tambaye shi suka ce, “To, wane ne kai? Kai ne Iliya?” Ya ce, “A’a, ni ba shi ba ne.” “Kai ne Annabin nan?” Ya amsa ya ce, “A’a.”
In vprašali so ga: »Kaj torej? Ali si Elija?« In reče: »Nisem.« »Ali si ti ta prerok?« In odgovoril je: »Ne.«
22 A ƙarshe suka ce, “Wane ne kai? Ka ba mu amsa don mu mayar wa waɗanda suka aike mu. Me kake ce da kanka?”
Potem so mu rekli: »Kdo si? Da bomo lahko dali odgovor tem, ki so nas poslali. Kaj praviš sam o sebi?«
23 Yohanna ya amsa da kalmomin annabi Ishaya, “Ni murya ne mai kira a hamada, ‘Ku miƙe hanya domin Ubangiji.’”
Rekel je: »Jaz sem glas nekoga, ki kliče v divjini: ›Naredite Gospodovo pot ravno, ‹ kakor je rekel prerok Izaija.«
24 To, waɗansu Farisiyawan da aka aika
Ti pa, ki so bili poslani, so bili izmed farizejev.
25 suka tambaye shi suka ce, “Don me kake yin baftisma in kai ba Kiristi ba ne, ba kuwa Iliya ba, ba kuma annabin nan ba?”
In vprašali so ga ter mu rekli: »Zakaj potem krščuješ, če ti nisi ta Kristus niti Elija niti ta prerok?«
26 Yohanna ya amsa ya ce, “Ni dai ina baftisma da ruwa ne, amma a cikinku akwai wani tsaye da ba ku sani ba.
Janez jim je odgovoril, rekoč: »Jaz krščujem z vodo, toda tam, med vami, stoji nekdo, ki ga vi ne poznate.
27 Shi ne mai zuwa bayana, wanda ko igiyar takalmansa ma ban isa in kunce ba.”
On je ta, ki prihaja za menoj, in je pred menoj, čigar čevljev jermena nisem vreden odvezati.«
28 Wannan duk ya faru ne a Betani a ƙetaren Urdun, inda Yohanna yake yin baftisma.
Te stvari so se zgodile v Betaniji, onstran Jordana, kjer je Janez krščeval.
29 Kashegari Yohanna ya ga Yesu yana zuwa wajensa sai ya ce, “Ku ga, ga Ɗan Rago na Allah mai ɗauke zunubin duniya!
Naslednji dan zagleda Janez k njemu prihajati Jezusa in reče: »Glejte, Jagnje Božje, ki odvzema greh sveta.
30 Wannan shi ne wanda nake nufi sa’ad da na ce, ‘Mutum mai zuwa bayana ya fi ni girma, domin yana nan kafin ni.’
To je on, o katerem sem rekel: ›Za menoj prihaja mož, ki je obstajal pred menoj, kajti bil je pred menoj.‹
31 Ko ni ma dā ban san shi ba, sai dai abin da ya sa na zo ina baftisma da ruwa shi ne domin a bayyana shi ga Isra’ila.”
In nisem ga poznal, vendar sem zato prišel krščevat z vodo, da bi se on razodel Izraelu.«
32 Sai Yohanna ya ba da wannan shaida, “Na ga Ruhu ya sauko kamar kurciya daga sama ya zauna a kansa.
In Janez je izjavil, rekoč: »Videl sem Duha spuščati se z neba, kakor golobico in je ostal na njem.
33 Dā ban san shi ba, sai dai wanda ya aiko ni in yi baftisma da ruwa ya gaya mini cewa, ‘Mutumin da ka ga Ruhu ya sauko ya kuma zauna a kansa shi ne wanda zai yi baftisma da Ruhu Mai Tsarki.’
In nisem ga poznal, toda kdor me je poslal, da krščujem z vodo, isti mi je rekel: ›Na kogar boš videl spuščati se Duha in ostajati na njem, isti je ta, ki krščuje s Svetim Duhom.‹
34 Na gani na kuma shaida cewa wannan Ɗan Allah ne.”
In videl sem in izjavil, da je ta Božji Sin.«
35 Kashegari kuma Yohanna yana can tare da biyu daga cikin almajiransa.
Naslednji dan je Janez ponovno stal in dva izmed njegovih učencev
36 Da ya ga Yesu yana wucewa, sai ya ce, “Ku ga, ga Ɗan Rago na Allah!”
in ko je gledal na Jezusa, medtem ko je hodil, reče: »Glej, Jagnje Božje!«
37 Da almajiran nan biyu suka ji ya faɗi haka, sai suka bi Yesu.
Dva učenca pa sta ga slišala govoriti in šla za Jezusom.
38 Da juyewa, sai Yesu ya ga suna bin sa, sai ya tambaye, su ya ce, “Me kuke nema?” Suka ce, “Rabbi” (wato, “Malam”), “ina kake da zama?”
Potem se je Jezus obrnil in ju videl slediti ter jima reče: »Kaj iščeta?« Rekla sta mu: »Rabi (kar prevedeno pomeni Učitelj), kje prebivaš?«
39 Ya amsa musu ya ce, “Ku zo, za ku kuma gani.” Saboda haka suka je suka ga inda yake da zama, suka kuma zauna a can tare da shi. Wajen sa’a ta goma ce kuwa.
Reče jima: »Pridita in poglejta.« Prišla sta in videla, kje prebiva ter ta dan ostala z njim, kajti bilo je okrog desete ure.
40 Andarawus ɗan’uwan Siman Bitrus, yana ɗaya daga cikin biyun nan da suka bi Yesu bayan da suka ji maganar Yohanna a kan Yesu.
Eden izmed dveh, ki sta slišala Janeza govoriti in sta mu sledila, je bil Andrej, brat Simona Petra.
41 Abu na fari da Andarawus ya yi shi ne ya sami ɗan’uwansa Siman ya gaya masa cewa, “Mun sami Almasihu” (wato, Kiristi).
Ta je najprej našel svojega lastnega brata Simona in mu rekel: »Našli smo Mesija, « kar je prevedeno, Kristusa.
42 Ya kuma kawo shi wurin Yesu. Yesu ya dube shi ya ce, “Kai ne Siman ɗan Yohanna. Za a ce da kai Kefas” (in an fassara, Bitrus ke nan).
In privedel ga je k Jezusu. In ko ga je Jezus pogledal, je rekel: »Ti si Simon, Jonov sin. Imenoval se boš Kefa, « kar je po razlagi: ›Kamen.‹
43 Kashegari Yesu ya yanke shawara yă tafi Galili. Da ya sami Filibus sai ya ce masa, “Bi ni.”
Naslednji dan je Jezus nameraval oditi naprej v Galilejo in najde Filipa ter mu reče: »Sledi mi.«
44 Filibus, kamar Andarawus da Bitrus shi ma daga garin Betsaida ne.
Torej Filip pa je bil iz Betsajde, Andrejevega in Petrovega mesta.
45 Filibus ya sami Natanayel ya kuma gaya masa, “Mun sami wanda Musa ya rubuta game da shi a cikin Doka, kuma wanda annabawa suka rubuta a kansa, Yesu Banazare, ɗan Yusuf.”
Filip najde Natánaela in mu reče: »Našli smo tistega, o katerem so Mojzes in preroki pisali v postavi, Jezusa iz Nazareta, Jožefovega sina.«
46 Natanayel ya ce, “A Nazaret! Wani abin kirki zai iya fito daga can?” Filibus ya ce, “Zo ka gani.”
Natánael pa mu je rekel: »Ali lahko iz Nazareta pride kakršnakoli dobra stvar?« Filip mu reče: »Pridi in poglej.«
47 Da Yesu ya ga Natanayel yana zuwa, sai ya yi magana game da shi cewa, “Ga mutumin Isra’ila na gaske wanda ba shi da ha’inci.”
Jezus je videl k njemu prihajati Natánaela in reče o njem: »Glejte, pravi Izraelec, v katerem ni zvijače!«
48 Natanayel ya yi tambaya ya ce, “A ina ka san ni?” Yesu ya amsa ya ce, “Na gan ka yayinda kake a gindin itacen ɓaure, kafin Filibus yă kira ka.”
Natánael mu reče: »Od kod me poznaš?« Jezus je odgovoril in mu rekel: »Preden te je Filip poklical, sem te videl, ko si bil pod figovim drevesom.«
49 Sai Natanayel ya ce, “Rabbi, kai Ɗan Allah ne. Kai ne Sarkin Isra’ila.”
Natánael je odgovoril in mu reče: »Rabi, ti si Božji Sin. Ti si Izraelov Kralj.«
50 Yesu ya ce, “Ka gaskata domin na ce maka na gan ka a gindin itacen ɓaure. Za ka ga abubuwan da suka fi haka.”
Jezus je odgovoril in mu rekel: »Ker sem ti rekel: ›Videl sem te pod figovim drevesom, ‹ veruješ? Videl boš večje stvari kakor te.«
51 Sai ya ƙara da cewa, “Gaskiya nake gaya muku, za ku ga sama a buɗe, mala’ikun Allah kuma suna hawa suna kuma sauka a kan Ɗan Mutum.”
In reče mu: »Resnično, resnično, povem vam: ›Odslej boste videli odprta nebesa in Božje angele, ki se vzpenjajo in spuščajo nad Sinom človekovim.‹«

< Yohanna 1 >