< Luka 20 >

1 Wata rana da Yesu yana koyar da mutane, yana musu wa’azin bishara a filin haikalin, sai manyan firistoci da malaman dokoki, tare da dattawan suka zo wurinsa.
In pripetilo se je, da so na enega izmed tistih dni, ko je v templju učil ljudi in oznanjal evangelij, prišli nad njega visoki duhovniki in pisarji s starešinami
2 Suka ce masa, “Gaya mana, da wane iko kake yin waɗannan abubuwa. Wa ya ba ka wannan ikon?”
in mu spregovorili, rekoč: »Povej nam, s kakšno oblastjo delaš te stvari? Ali kdo je tisti, ki ti je dal to oblast?«
3 Ya amsa ya ce, “Ni ma zan yi muku wata tambaya. Ku faɗa mini,
In odgovoril je ter jim rekel: »Tudi jaz vas bom vprašal eno besedo in odgovorite mi:
4 baftismar Yohanna, daga sama ne ta fito, ko kuwa daga wurin mutane ne?”
›Ali je bil Janezov krst iz nebes ali od ljudi?‹«
5 Sai suka yi shawara da junansu, suka ce, “In muka ce, ‘Daga sama ne,’ zai tambaya, ‘To, don me ba ku gaskata shi ba?’
Oni pa so razpravljali med seboj, rekoč: »Če bomo rekli: ›Iz nebes, ‹ bo rekel: ›Zakaj mu potem niste verjeli?‹
6 Amma in kuma muka ce, ‘Daga mutane ne,’ dukan mutanen za su jajjefe mu da duwatsu, domin sun tabbata cewa, Yohanna annabi ne.”
Toda če rečemo: ›Od ljudi, ‹ nas bodo vsi ljudje kamnali, kajti pregovorjeni so, da je bil Janez prerok.«
7 Don haka, sai suka amsa cewa, “Ba mu san inda ta fito ba.”
In odgovorili so, da ne morejo povedati, od kod je bil.
8 Yesu ya ce, “To, ni ma ba zan gaya muku, ko da wane iko ne, nake yin waɗannan abubuwa ba.”
In Jezus jim je rekel: »Niti vam jaz ne povem, s kakšno oblastjo delam te stvari.«
9 Sai ya ci gaba da gaya wa mutanen wannan misali ya ce, “Wani mutum ya yi gonar inabi, sai ya ba da hayarta ga waɗansu manoma, sa’an nan ya yi wata doguwar tafiya.
Potem je začel ljudem govoriti to prispodobo: »Neki človek je zasadil vinograd in ga prepustil poljedelcem ter za dolgo časa odšel v daljno deželo.
10 A lokacin girbi, sai ya aiki bawa zuwa wurin masu hayan, don su ba shi daga cikin’ya’yan inabin. Amma’yan hayan suka yi wa bawan nan dūka, suka kore shi hannu wofi.
Ob primernem obdobju pa je poslal k poljedelcem služabnika, da bi mu lahko dali od sadu vinograda, toda poljedelci so ga pretepli in ga odposlali praznega.
11 Ya sāke aikan wani bawa, shi ma suka yi masa dūka, suka kunyata shi, suka kuma kore shi hannu wofi.
On pa je ponovno poslal drugega služabnika in tudi njega so pretepli in sramotno ravnali z njim ter ga odposlali praznega.
12 Har yanzu, ya sāke aikan na uku, amma suka ji masa rauni, suka jefar da shi waje.
Pa je ponovno poslal tretjega in tudi njega so ranili ter ga vrgli ven.
13 “Sai mai gonar inabin ya ce, ‘Me zan yi? Zan aiki ɗana da nake ƙauna, wataƙila za su girmama shi.’
Potem je gospodar vinograda rekel: ›Kaj naj storim? Poslal bom svojega ljubljenega sina. Ko ga bodo videli, ga bodo mogoče spoštovali.‹
14 “Amma da’yan hayan suka gan shi, sai suka tattauna zancen, suka ce, ‘Wannan shi ne magājin, mu kashe shi sa’an nan gādon zai zama namu!’
Toda ko so ga poljedelci zagledali, so med seboj razpravljali, rekoč: ›Ta je dedič. Pridite, ubijmo ga, da bo dediščina lahko naša.‹
15 Sai suka fitar da shi waje, suka kashe shi. “To, me mai gonar inabin zai yi da su?
Tako so ga vrgli iz vinograda in ga ubili. Kaj jim bo torej storil gospodar vinograda?
16 Zai zo ya karkashe masu hayan nan, ya ba wa waɗansu gonar inabin.” Da mutanen suka ji wannan, sai suka ce, “Allah ya sawwaƙa!”
Prišel bo in uničil te poljedelce, vinograd pa bo dal drugim.« Ko pa so to slišali, so rekli: »Bog ne daj.«
17 Yesu ya zura musu ido ya ce, “To, mene ne ma’anar abin da aka rubuta cewa, “‘Dutsen da magina suka ƙi, shi ne kuwa ya zama dutsen kan ginin’
On pa jih je pogledal in rekel: »Kaj je torej to, kar je pisano: ›Kamen, ki so ga graditelji zavrgli, ta isti je postal glava vogalu?‹
18 Duk wanda ya fāɗi a kan dutsen nan, zai kakkarye. Kuma in dutsen nan ya fāɗi a kan wani, zai murƙushe shi.”
Kdorkoli bo padel na ta kamen, bo razbit, toda na kogarkoli bo ta padel, ga bo zmlel v prah.‹«
19 Malaman dokoki da manyan firistoci, suka nemi hanyar kama shi nan da nan, domin sun san cewa, ya yi wannan misali a kansu ne, amma suna jin tsoron mutane.
In visoki duhovniki ter pisarji so skušali to isto uro položiti roke nanj; bali pa so se ljudi, kajti zaznali so, da je to prispodobo govoril proti njim.
20 Sai suka sa masa ido, suka aiki’yan leƙen asiri, waɗanda suka nuna kamar su masu gaskiya ne, suna nufin su kama shi game da abin da zai faɗa, domin su ba da shi ga gwamna mai mulki, da mai iko.
In opazovali so ga ter poslali oglednike, ki naj bi se hlinili [za] pravične može, da bi ga lahko prijeli za njegove besede, da bi ga tako lahko izročili voditeljevi moči in oblasti.
21 Sai’yan leƙen asirin suka tambaye shi, suka ce, “Malam, mun sani kana faɗin, kuma kana koyar da abin da yake daidai, ba ka kuma nuna bambanci, amma kana koyar da hanyar Allah bisa ga gaskiya.
In vprašali so ga, rekoč: »Učitelj, vemo, da prav govoriš in učiš niti ne sprejemaš zunanjega videza kogarkoli, temveč resnično učiš Božjo pot:
22 Daidai ne mu biya haraji ga Kaisar, ko babu?”
›Ali je za nas zakonito, da dajemo cesarju davek ali ne?‹«
23 Ya gane makircinsu, sai ya ce musu,
Vendar je zaznal njihovo prebrisanost in jim rekel: »Zakaj me skušate?
24 “Nuna mini dinari. Hoton wane ne, kuma rubutun wane ne a kai?” Suka amsa, “Na Kaisar.”
Pokažite mi kovanec. Čigavo podobo in napis ima?« Odgovorili so in rekli: »Cesarjevo.«
25 Sai ya ce musu, “Ku ba wa Kaisar abin da yake na Kaisar, ku kuma ba wa Allah abin da yake na Allah.”
In rekel jim je: »Povrnite torej cesarju stvari, ki so cesarjeve, Bogu pa stvari, ki so Božje.«
26 Ba su iya kama shi a kan abin da ya faɗa a fili ba. Amsarsa ya ba su mamaki, shi ya sa suka yi shiru.
In pred ljudmi ga niso mogli prijeti zaradi njegovih besed in čudili so se ob njegovem odgovoru in molčali.
27 Waɗansu Sadukiyawa da suke cewa, ba tashin matattu, suka zo wurin Yesu da tambaya cewa,
Potem so prišli k njemu nekateri izmed saducejev, ki zanikajo, da obstaja kakršnokoli vstajenje in vprašali so ga,
28 “Malam, Musa ya rubuta mana cewa, ‘In ɗan’uwan wani mutum ya mutu, ya bar mata amma ba’ya’ya, dole mutumin ya aure gwauruwar, ya samo wa ɗan’uwansa’ya’ya.’
rekoč: »Učitelj, Mojzes nam je napisal: ›Če komu umre brat, ki ima ženo in umre brez otrok, da naj njegov brat vzame njegovo ženo in svojemu bratu obudi seme.
29 To, an yi waɗansu’yan’uwa bakwai. Na fari ya auri wata mace, ya mutu ba’ya’ya.
Bilo je torej sedem bratov in prvi je vzel ženo ter umrl brez otrok.
30 Na biyun,
In drugi jo je vzel za ženo ter umrl brez otrok.
31 da na ukun suka aure ta. Haka nan dukansu bakwai suka mutu babu’ya’ya.
In vzel jo je tretji in na podoben način tudi sedmi, pa niso zapustili otrok in so umrli.
32 A ƙarshe, ita macen ma ta mutu.
Zadnja izmed vseh je umrla tudi ženska.
33 Shin, a tashin matattu, matar wa za tă zama? Tun da su bakwan nan, sun aure ta.”
Čigava žena od teh bo torej ob vstajenju? Kajti sedem jo je imelo za ženo.‹«
34 Yesu ya amsa ya ce, “Mutanen zamanin nan suna aure, suna kuma ba da aure, (aiōn g165)
Jezus jim odgovori in reče: »Otroci tega sveta se poročajo in so dane v zakon, (aiōn g165)
35 amma su waɗanda aka ga sun cancantar kasancewa a zamanin can, da kuma na tashin matattu, ba za su yi aure, ko su ba da aure ba. (aiōn g165)
toda tisti, ki bodo šteti za vredne, da dosežejo oni svet in vstajenje od mrtvih, se ne bodo niti poročali, niti ne bodo dane v zakon, (aiōn g165)
36 Kuma ba za su sāke mutuwa ba, gama su kamar mala’iku ne. Su’ya’yan Allah ne, tun da su’ya’yan tashin matattu ne.
niti ne morejo več umreti, kajti enaki so angelom in so Božji otroci, saj so otroci vstajenja.
37 Amma bisa ga labari na bishiya nan, mai cin wuta da Musa ya gani a jeji, ko Musa ma, ya nuna cewa, matattu suna tashi. Gama ya kira Ubangiji, ‘Allah na Ibrahim, da Allah na Ishaku, da kuma Allah na Yaƙub.’
Torej, da so mrtvi obujeni, je pokazal celó Mojzes pri grmu, ko je imenoval Gospoda ›Bog Abrahamov in Bog Izakov in Bog Jakobov.‹
38 Shi ba Allah na matattu ba ne, amma na masu rai ne, gama a gare shi, duka na da rai.”
Kajti on ni Bog mrtvih, temveč živih, kajti njemu vsi živijo.«
39 Sai waɗansu malaman dokoki suka amsa suka ce, “Ka faɗi daidai, malam!”
Tedaj so nekateri izmed pisarjev odgovorili in rekli: »Učitelj, dobro si povedal.«
40 Kuma ba wanda ya sami ƙarfin halin yin masa waɗansu tambayoyi.
Nató pa se ga niso drznili vprašati nobenega vprašanja več.
41 Sai Yesu ya ce musu, “Yaya suke cewa, ‘Kiristi ɗan Dawuda ne?’
In rekel jim je: »Kako pravijo, da je Kristus Davidov sin?
42 Dawuda da kansa ya faɗa a cikin Zabura, “‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana,
In sam David pravi v knjigi Psalmov: › Gospod je rekel mojemu Gospodu: ›Sedi na mojo desnico,
43 sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka.”’
dokler ne naredim tvojih sovražnikov [za] tvojo pručko.‹‹
44 Dawuda ya kira shi ‘Ubangiji.’ Ta, yaya zai zama ɗansa?”
David mu torej reče Gospod, kako je potem on njegov sin?«
45 Yayinda dukan mutane suna cikin sauraronsa, sai Yesu ya ce wa almajiransa,
Potem je pred občinstvom vseh ljudi svojim učencem rekel:
46 “Ku yi hankali da malaman dokoki. Sukan so sa manyan riguna suna zaga, suna sha’awan karɓan gaisuwa a wuraren kasuwanci, da kuma wuraren zama mafi daraja a majami’u, da wuraren bangirma a bukukkuwa.
»Pazite se pisarjev, ki želijo hoditi v dolgih svečanih oblačilih in imajo radi pozdrave na trgih in najvišje sedeže v sinagogah ter vodilna mesta na praznovanjih,
47 Suna mamaye gidajen gwauraye, kuma don burga, suna dogayen addu’o’i. Ga irin waɗannan mutane, za a yi musu hukunci mai tsanani sosai.”
ki vdovam požirajo hiše in zaradi lepšega delajo dolge molitve; isti bodo prejeli večje prekletstvo.«

< Luka 20 >